TAKUN SAAKA COMPLETE HAUSA NOVEL

TAKUN SAAKA 6

 *_Typing????_*

__________________

*_ASSALAMU ALAIKUM BEAUTIFUL PEOPLE!! ZAFAFA BIYAR FAMILY????????????????❤️_*

_MUNGODE DA ZABIN LITTAFAN ZAFAFA BIYAR. ALLAH YA KARA BUDI YA KUMA BAR ZUMUNCI_

*_KAMAR KO DA YAUSHE, WANNAN KARON MA MUNZO DA KOKON BARAR YOUTUBE CHANNEL DIN YARON MU, SUDEIS MASOYI KUMA MAKARANCI, MAHADDACIN ALKUR’ANI MA GIRMA_*

_WANNAN KARON MA DAN ALLAH A TEMAKA ADANNA WA CHANNEL DINSA KARARRWA DOMIN KASANCEWA DA MU A DUK SANDA MUKA DORA FEFAN BIDIYON SA, A TALLAFA A KALLA A KUMA DANNA MASA SUBSCRIPTION. HAKAN NA KARAWA SUDEIS KWARIN GWIWAR SAKE DAGEWA YA KUMA KARA KAIMI WAJEN YIN KARATUN SOSAI. MUNGODE KWARAI????????????❤️_

*_GA CHANNEL DIN DAKE YOUTUBE NAN????????_*

https://youtube.com/c/sudaiskura

_Sudais is a young boy who has passion in recitation of the Holy Qur’an at a very young age._

_Please help him grow his YouTube channel by subscribing and liking his videos to encourage the little boy. Jazakumullahu khairan????????_

_________________________

*_Chapter Six_*

…………..Ƙoƙarin kauda fuskarta taketa faman yi saboda kar Yah Muhammad ya ga hawayen dake guje-gujen sakko mata akan fuska tun bayan barowarsu gida. Sai dai kuma abinda bata sani ba tuni ya fahimci kuka takeyi, yadai mata shiru ne domin bata damar rage nauyin zuciyarta.

       Sai da ya ɗauka titin da zai kaisu har makarantar tasu sannan yay gyaran murya batare da ya kalleta ba. Shiru Hibbah bata motsa ba saboda zurfi da tai a tunani….

      “Auta!” 

Ya kira sunanta cike da kulawa. Nanma shiru babu alamar ta jisa. Leɓensa yaɗan ciza na ƙasa yana gangarawa gefen titi. Harya kashe motar gaba ɗaya ya juya yana kallonta batasan mi yakeyi ba. Cikin damuwar data bayyana sosai akan fuskarsa ya ce, “Muhibbat!!”.

       A firgice ta juyo garesa tana sauke wata irin nannauyar ajiyar zuciya. Sai kuma tai saurin kai hannunta akan fuskarta ta shiga share hawayenta tana ƙaƙalo murmushi. “Lah Yaya banjikaba ALLAH. Ina can wajen kallon hanya har idanuna na hawaye dan ƙauyanci”.

      Murmushin da bai niyyar yi baneba ya suɓuce masa. A ransa yanajin ƙaunar ƴar ƙanwar tasu da yaba halinta na manya. Duk da rawan kanta da tsiwa ita ɗin yarinyace data san yakamata. Tana da wasu nagartattun halaye da sai ka nutsu gareta kake iya ganosu. Amma a kallo ɗaya zaka iya dangantata da yarinya mai rawar kai da shirme. Ya ɗanja numfashi yana furzarwa a hankali tare da kafeta da idanunsa irin nata.

      “Mi kike tunani Muhibbat!?”.

A yanda yay maganar babu wasa a cikinta ne ya sata ɗago idanunta dake ƙoƙarin tara ƙwalla ta dubesa. Sai kuma tai saurin girgiza kanta tana ƙoƙarin maida kukan dake son ƙwace mata. 

     “Ba bu komai Yayah”.

Ta faɗa muryarta na rawa.

        Sosai ya sake kafeta da idanunsa dake canja kala zuwa ɓacin rai. Sai dai kuma cikin tausasa murya ya ce, “Kin dai san banason ƙarya ko?”.

     Kanta ta jinjina masa hawayen da taketa ƙoƙarin makalewa suka gangaro a hankali bisa fuskarta…. “Yaya! Abba ne, miyasa baya sonmu? Musamman ma ni ya tsaneni bayason ganina”. 

         Takai ƙarshen maganar tata da fashewa da wani irin kuka mai cin rai ga ma’abocin saurare. Idanunsa ya lumshe a hankali tare da cije leɓensa na ƙasa da ƙarfi. Addu’a ya fara karantowa a zuciyarsa domin samun dai-daito daga fushi da fusatar damuwar ƴar uwar tasa. Ya kamo hannunta cikin nashi ya rumtse da ƙarfi.

         Kamar jira take ta sake fashewa da wani kukan, fuskarta ta kwantar akan hannayen nasu dake cikin na juna, hawayenta suka shiga gangarowa har akan fatar hannunsa data ɗora kanta a kai. Cikin kuka ta cigaba da faɗin “Yaya miyasa Ummi ta yarda ta auresa? Bayan kuma tasan shi ɗin mugu ne. Miyasa bata haƙura ta zauna damu mu kaɗai ba bayan rasuwar Abbanmu?. Wlhy Yaya banason Abba na tsanes…….”

       “Muhibbat!”. Yay saurin katseta da ƴar tsawa. 

Ɗago kanta tai tana kalonsa, ganin yanda ya ɗaure fuska ne ya sake sakata fashewa da kukan.

      Yaya miyasa bakwaso nace banason Abba bayan shima baya son mu. Kullum shike gusar da farin ciki a kan fuskokinku. Duk randa yazo sashenmu sai Ummi tayi kuka a ɓoye. Sannan fuskarta tana kumbura kamar wadda aka daka Yayanmu”.

       A matuƙar razane yake kallonta a yanzun. Dan tabbas tun basukai hakaba suke tambayar Ummi mike samunta a fuska a maban-banta lokaci, amma sai takan ce musu wani ciwo ne yake mata haka akan fuska lokaci-lokaci, amma tana shan magani. Sunsha damunta suje asibiti amma sai taƙi yarda. Sai dai kuma yau gashi ƙaramar ƙanwarsu tazo da wani batu mai girma. Shin kodai da gaske ne da ake cewa duk ƙanƙantar ɗiya mace tafi ɗa namiji lura da maida hankali akan abu…….

      “Yayanmu dan ALLAH kasa mubar musu gidansu mu koma can wani gari da zama mu daina ganinsu suma su daina ganinmu.”

      Hibbah ta katse masa tunani ta hanyar girgizasa tana kuka da roƙonsa.

        “Tanee! kinga nutsu muyi magana. Maza share hawayenki na tambayeki”.

     Da sauri ta shiga share hawayenta da handkerchief ɗinsa. Duk da wasu nabin wasu hakan bai hanata faɗin, “Yaya na goge”.

          “Auta kin taɓa ganin wani ya daki Ummi ne?”.

      Kanta ta girgiza masa.

“To miyasa kikace kamar ana dukanta?”.

          “Yaya nidai haka kawai nake ganin kamar shatin yatsu a fuskarta a duk randa fuskan yay kumburi. Sai kuma ranar da Abba ya kwana a sashenmu na taɓa jin kamar tana kuka na fito ɗaukar ruwa dana manta ban ɗauka ba da dare. Tana kuka sosai, ina kumajin muryan Abba yana mata kamar magana cikin faɗansan nan”.  

         Kallonta kawai yake ko ƙyaftawa babu, acan ƙasan ransa kuma yanama kalamanta fashin baƙi dalla-dalla. Ganin yaƙi cewa komai yasata kai hannunta akan masa ta girgiza shi.

     Ajiyar zuciya ya sauke da haɗiye damuwar dake neman kufcewa akan kamilalliyar fuskarsa. 

      “Yaya baka yarda ba ko?”.

“A’a Auta, taya zan ƙaryataki bayan nasan ke ɗin baki da ƙarya. Kawai dai ina nazari ne akan maganar taki. Amma inaga yanzu ba shine lokacin yinsa ba. Bara na kaiki makaranta karki makara. Idan mun koma gida zamuyi magana. Amma na roƙeki bayan ni karki faɗama kowa zancen nan har cikin su Usman kinji ko”.

       “Insha ALLAH Yaya bazan faɗa musu ba. Amma dan ALLAH ka tambayi Ummi kaji ko Abba yake dukanta ne?”.

      Ɗan murmushi yayi a ƙasan ransa yana jinjina wautarta. “Karki damu insha ALLAH bazan manta ba.

     Koba komai ta ɗanji sanyi a ranta. Dan haka ta ƙarasa share hawayenta nauyin da zuciyarta yay mata yana sauka a hankali.

       Tunda ya tada motar suka cigaba da tafiya sai shi ya koma cikin yanayin shiru ɗin. Dan gaba ɗaya tunaninsa da hankalinsa sun koma akan zantukan Hibbah. 

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button