Noor Albi

NOOR ALBI 15

Koda suka iso Turaki na gida sbd Ganin Daya daga cikin motocinsa Rolls Royce phantom baqa pake a hanyar daf da Shiga sashensa hakama ganin A Abdoul a harabar gidan yasake tabbatarda hakan sbd idan Yana gidane kawai kake ganin A Abdoul.

A Abdoul da sauran masu aikin sashen Anne ne suka fito tarbanta tareda daukan kayan da akazo dasu duk da bawasu Kaya bane daga qaramar luggage din Anne sai handbag dinta su Sa’adah da laylah akwati dayace sukazo da ita na iya sabbin kayan da aka dinkawa Sa’adah sai kayan Laylah guda biyu aciki itama sababbin da Anne ta Bata dinne Kai tsaye aka karba komai akai ciki dashi kafin suka nufi babbans sashen Annen Dake baya kadan daga can gefen sosai danasu Turakin.

Daga Sa’adah data Saba zuwa gidanjen masu ‘yan kananun kudi dangin uwarta har Laylah da Bata zuwa koina daga gida sai gida sai kasuwa sai asibiti
Babu Wanda ya rudar da kansa da wani kalle kalle sbd daidai gwargwadon nutsuwarsu,
Dan sani Kam sunsan sunzo wata duniyarce ta daban Amma Kuma Basu rikita kansu da wani kalle kalle a saima kokarin sake nutsuwa dasukeyi Dan kuwa jikinsu duka sanyi yayi Dan Basu dauka Haka duniyar gidan Turakin take da banbanci fiyeda tunani da inda Suka fitoba.

Ita Laylah Bata tunanin komai bayan bin duk dinta Yar uwarta tayi sbd dama tasan dawainiyar Yar uwarta tazo yi duk da taga yanayin gurin Kam ba lallai ta iya wasu ayyukan batareda an koyar da ita saidai Kam har a zuci da sarari tayi anty Sa’adah fatar samun rayuwar farin ciki da kwanciyar hankali tareda mijinta Dan kuwa shima da Anne zasu Shiga adduarta tunda suka aminta da karban riqonta a gidan batareda sunqi amincewaba.

Palon Anne Kam zaunawa sukayi Sa’adah na kallon koina tana yaba tsarki na ubangiji Mai ni’imta bayin dayaso.

Sanin akwai gajiya da buqatar hutawa a tareda dasu tace akaisu dakinta daya dake sama Kai tsaye Dan qasan manyan palone guda biyu da kicin dasu dining room sai dakin baqi guda daya Dana masu aikinta su biyu dasukai shekaru masu tsayi tare.

Ana kaisu dakin da’akace na Sa’adah ne aka fito aka barsu Sa’adah na kallon koina cikin dakin dayaji English royal set na gado Ash Mai haske da curtains milk masu touch na Ash kadan kadan aciki,
Daga gefe ga wasu set na sofa gua uku golden da table a tsakiyarsu.

Ac da aka kunna ne yafara Kama dakin da Sanyi Mai Dadi ga qamshin turaren Rose night dake fita kadan kadan daga Air defyair Yana sakar da wata irin nutsuwa da kwanciyar hankali a dakin.

Kallon Laylah wadda ke kallonta cikin Dan yanayi na sake shaidar da farin cikin da Antynta take ciki Ahankali tace”

Laylah???

Ahankali ta amsa cikin Taushin lafazinta da cewa”

Na’am.

Jinjina Kai Sa’adah tayi tana sauke numfashi ajere tana cewa”

Zamu iya rayuwa Inshallah anan,
Zamuyi kokarin inganta rayuwarmu sbd tamkar marayu muke yanzu mu dukan,
Ta wani sashen Kuma tamkar nice marainiyar kinfini gata yanzu.

Dan sauke Kai Laylah tayi cikin qaramin sauti Mai sanyi tace”

Anty Sa’adah kece kadai gatana a yanzu da Allah ya bani,
Nagode sosai Allah yasaka Miki da alkhairi Kuma Zan Miki biyayya daganan har qarshen rayuwata Anty Sa’adah,
Anne ma da mutanen gidan Nan Zan musu biyayya kowa bazan Bari kiyi danasanin zuwa daniba har su Abba yadawo Inshallah.

Murmushi Mai sauti Sa’adah tayi tana cewa”

Naji wannan maza muje toilet Naga abinda Zan koya Miki kiyo alwala akwai salloli akanmu.

A toilet kam qarasa saddakar da komai sukayi na gidan da rayuwar gidan Dan kuwa yanzu sukam sai abinda kawai idanuwansu suka ganar musu Amma girman toilet din da tsaruwarsa har kayar da agaban Laylah yayi.

Alwala sukayo bayan sunfito Aka kawo musu kayan ciye ciye dansu suci su huta kafin su sauko cin abinci,
Mai aikin ce ta nuna masu inda zasu kalla suyi sallah kafin ta fice.
Suna idarwa anty Sa’adah ce tafara cin su snacks din da akayi su a tsare sunyi kyau da Dadi Sosai sai fresh milk masu sanyi.

Sai data cewa laylah taci tukuna tasaka hannu a natse tafara dauka tanaci tareda Shan fresh milk din datai sanyi sosai ga wani irin kauri da dadin zallar Madara da nono.

Sosai sukaci suka koshi kafin Sa’adah ta miqe ta Haye gado tareda miqewa sbd gajiyar datake ji.
Laylah kuwa tattare gurin tayi tareda daukan kayan ta fito dasu har qasa
Masu aikin sukai saurin tarbanta cikin tsananin girmamawa suka karba suna cewa ta ringa kiransu a kowane aiki.

Ba musu ta gyada Kai a girmame itama kafin ta juya tana Shirin komawa wani qamshi Mai qarfin sanyin qamshi ya fara gauraye palon batareda ta dakataba ta Dan waiwayo kadan daidai shigowarsa Sanye cikin wani tsaddaden farin yafin filtex daya fitarda haskensa da annurinsa sosai
Take tayi saurin sauke kanta tana sauke idanuwanta daya cika matasu har Saida gabanta ya fadi
Taqarawa kanta sauri zata qarasa wucewa Kamar daga sama muryar Anne ta sauka cikin Kulawa tace”

LAYLAH dawo ki gaidasa.

Cak ta tsaya tareda juyowa ahankali batareda takuma dagowaba muryarta a wani irin Sanyaye ta furta”

Ina wuni?

Gabaki daya Bai lurada kowaba agurin Saida Annen tayi magana Dan Haka Kai tsaye ya amsa gaisuwar da sautinsa Mai kamewa batareda ya kalli gurinba yaqarasa wucewa zuwa palon Anne Dake hade da bedroom dinta.
Kallon Laylah dake sanyeda kayan dasukazo dasu har lokacin ajikinta Riga da skirt na wani babban zallar farin lace Mai adon golden ajiki.
Fuskarta ta kalla tasaki Dan murmushi tana cewa”

Jeki kihuta za’a kawo kayan sawarki zuwa Anjima ko gobe da safe
Karkiyi aikin komai kinji.

Gyada Kai tayi Ahankali tareda furta” Nagode” cikin sauti qarami kafin ta wuce tabar Anne nabin Dan kwankwasonta da kallo duk da akwai mayafi Mai Dan girma ajikinta Amma Kam Laylahn batada kiba ko kadan saidai ahakanma duk da Bata ganta dakyauba ta lurada tanada cikar qirji da qasa saidai Suma Kam duk Basu wani fitoba sbd Ganin take harda yunwa ajikin Laylan.

Juyawa tayi itama tayi hanyar palonta da Turakin ya nufa.

Laylah nakomawa daki zaunawa tayi tunda basuda abin Yi ga Sa’adah ba damar samun Momy a waya bare takira suji duk da kila Basu isabama
Qarshe dai Kawu suka Kira suji koya Isa din shima tunda shima a ranar ya wuce da nasa tarin Sha Tara ta arzikin da Turaki yabasa Wanda sai lokacin daya tak ya sawa dangin Momy albarka dasuka kirasa yazo Dan son ransu gashi shi gaba takaisa Dan kuwa yasan Inshallah shi da rashi sunyi hannun Riga Dan babbar sanaar zaije yafara da abin daya samo din.

Kawun bai Isa nijar ba Amma suna Hanya Dan Haka sama sama yakuma musu Yar nasiha tareda gargadi Mai girma akan su maida hankali ga karatun da za’a sakasu Dan iyayensu suyi alfahari dasu idan suka dawo.

Sai bayan sallar magriba aka kawo musu kayan dogayen jallabiya marasa nauyin adon stones ko wani abun daban sukai wanka akai musu ison fitowa cin abinci suka sauko Sa’adah ce agaba Laylah na bayanta.

Dining room aka nufa dasu aka Basu gurin zama a kujerun dining din
LAYLAH ita aka bawa wadda ke facing ta Anne sbd sanin itace Matar gidan sai Sa’adah da aka bawa ta gefen Anne din alamar itakuma ‘ya kaidar zaman dining kenan.

Laylah data dauka hakan amatsayin kusancin alaqar Mata da sirikane yasa Sa’adah ke zaune gefe ahankali ta furtawa halima data ja mata kujerar data zauna “Nagode”

Abinci kusan kala biyu ne sai drinks da fresh milk da kayan plates dasu Tumblrs ke jere a fadadden dining din da Air-cooler ke facing dinsa suka fara cin abinci Banda Laylah data kasa sakewa sbd rashin sabo
Dan a gida tasaba tsaitsaye takecin abinci sbd tarin ayyukan gabanta Bata iya cin abinci Haka.

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button