UBAYD MALEEK 36

Saidata Gama ta janyo towel ta daura zata fito ta drwer jere da kalolin shavers da hair clippers a jere masu shegiyar tsada ta dauko ta kalli towel din jikinta sai alokacin tunanin dakinsa ne wannan din kenan yashigo Mata ta dafe kanta tana Jin wani iri kafin tafito.

Tana fitowa Yana zaune kan sofa yayi crossing legs Yana waya ahankali cikin nutsuwa da kamewa Amma tunda ta fito idanuwansa suke kanta duk wayar dayakeyi Kuma batareda yanayinsa ya sauya ba.

Jin idanuwansa akanta yasa takasa fita daga dakin ta nufi gaban madubinsa ta tsaya tana tunanin abinyi sai kawai taji mutum a bayanta tsaye Yana kallonta ta cikin mirror din da ido ya nuna Mata oil na Neutrogena ta Kai hannu ta dauka ta zauna gaban madubin tana shafawa ahankali 

Ganin yanda takeyi yasashi juyawa ya fice Yana gyaran murya sbd muryarsa data Dan shake da wainda yake wayar Dan Haka ya fice yaci gaba da wayarsa.

Tana gamawa saigashi yashigo ya ajiye Mata jakar kayan shopping dinta daya iso yakuma ficewa

Ta bude kayan ta dauki pant da bra tasaka ta shafa turare saita tsaya tunanin kayan sawa sbd gabaki daya ta manta da cewa kafin kayansu su iso saisun buqaci kayan sawa.

Kayan baccin ta daga taduba tana fitarda numfashi me zafi sbd wainnan kayan sanyima kamata zaiyi idan tace ta yini dasu ajikinta Dan babu ta arziki ita saiyanzuma tunanin waya kaita siyansu yafado Mata.

Tattara kayan tayi tasaka wardrobe ta dauki riga daya ta saka ta daure kanta tareda Dora jallabiyarta akai ta tada sallar la’asar da akai hadda azahar da batayiba.

Tana cikin yi yashigo dakin ya Dan kalleta ganin tana sallah saidai baice komaiba ya nemi guri ya zauna Yana waya da Mr Omar dake basa bayanin komai na tafiya akan tsari.

Tana idarwa ta miqe tareda warware nadin kanta takasa cire rigar jikinta batareda ya aje wayar dayakeyi ba yace taje ankawo abinci.

Tanajin yunwa Dan Haka Bata tsayaba ta wuce Ashe Yana bayanta ya zauna dining din me kujera biyu rak ta waiwaya ahankali tace”

Farhat zandubo tazo taci abinci…

Aje wayarsa yayi tareda kashewa gabaki daya yana cewa”

Batanan tana gurin Sarah zata kula da ita.

Da marairaice fuska ta kallesa bama tareda tasan tayi hakan ba 

Ya Dan bude idonsa akanta ganin yarintar datake Shirin zuba Masa Dan kamar zatayi kuka ta langwabe kai.

Saidata zuba Masa komai kafin ta hada ruwan zafi da kanta tazo ta zauna Tasha black tea me zafi tana lumshe ido sbd nutsuwar datakeji ruwan dumin nashiga cikinta.

Abincin kadan taci Tasha magani ta Dan daddaure ta gyara gurin Takoma daki ta kwanta take bacci ya dauketa sbd maganin yanasa bacci shikuma ya hau duba wasu tarin emails daya samu duk a yau din hadda na jiya dabai Samu damar dubawaba.

Bacci tayi sosai sai magriba ta tashi bawai Dan ya saketaba saima kashe Mata jiki da maganin yayi ta tashi da qyar tayo alwala tazo tayi sallah tana gamawa tadawo Palo tadan zauna tareda kunna tv Amma tsoron ganin ita kadaice yasa tana ganin lokacin ishai yayi ta koma daki tayi sallar ishai din tana gamawa ta tube tasake komawa toilet taduba har lokacin shiri period din Bai saukaba sai tayi wanka tafito ta shafa turare kawai tasaka kayan bacci kenan tana tunanin yanda zata koma dayan daki ta kwana ita kadai saigashi yashigo.

##MAMUH#

 **************Suna fitowa Kai tsaye wani qaramin underground gidansa dake cikin anguwar suka nufa Wanda keda 2 bedrooms rak da manyan Palo guda biyu sai kitchen me hade da dining acikinsa komai na gidan is milk Mr Omar ne kawai yasanda gidan Babu Wanda yasan gidan nasane Haka gidan komai a kip kip yake anan yake wasu private wayoyinsa da ayyukansa hakama wata maganar me buqatan tsananin sirri anan suke zuwa suyita da Mr Omar.

Parking Mr Omar yayi yafito ya budewa MALEEK yafito kafin yabudewa NURU ita saiya zagaya ya budewa farhat tareda kamo hannunta suka biyo bayan maleek dake gaba tareda NURU dake tafiya ahankali sbd ciwon Mara.

Suna shiga palon NURU ta dago ta kalli koina cikin palon cikeda mamakin tsaruwar gidan da cikin yafi wajenma kyau sosai saidai sbd yanayinta bazata iya qarewa koina kalloba a matse take data samu guri ta kwanta Tasha ruwan zafi masu zafi Sosai ko zata Dan fada Mata tasamu period din ya sauko wahalar ta rage Mata.

A palon farko ya dakata tareda kallonta Yana nuna Mata kofar palon qurya inda bedrooms suke cikin nutsuwa yace”

Ki Shiga ciki zanyi mgn da Mr Omar.

Dan dagowa tayi ta kallesa har lokacin ita yake kallo ta gyada Kai ahankali ta juya farhat na riqeda hannunta suka wuce cikin.

Palon cikin baiyi girman na farkon ba Amma yafisa tsaruwa ta juya gurin bedrooms din ta nufi Wanda yake damarta ta murda tareda budewa ahankali batasan lokacinda ta sauke ajiyar zuciyaba sbd ganin girma da tsaruwar dakin ga makeken gadon daya kusa cika dakin komai fes fes sai qamshi koina gidan keyi da Alama kullum Ana gyara koina agidan ayi mopping Dan ko yau kila anyi Dan qamshin dayake koina dagaji sabon gyarane.

Tana Isa bakin gadon ta sulale ta haye tareda kwantawa tana dungulewa guri daya tana dafe mararta rufe idanuwanta tana Jin Dan dama dama data kwanta din.

Sai daga baya ta bude idanuwanta ahankali ta kalli farhat da duk tayi wani iri sbd halinda aka shiga sai taji yarinyar tasake shiga ranta sbd tausayinta ta cire hannu daya takamota kusada ita ta bude Baki daqyar tace”

Sweetie kadakiji tsoro ko damuwan komai kinji daddy Yana Nan Nima Ina Nan Afia ma zatazo komai lafiya Inshallah,yanzu Kinga Banda lafiya I can’t treat and drss your wound kije kifadawa daddy Akira mum Sarah tazo ko Dr aduba kafanki kafin anjima nasamu naji Dan sauki kinji.

Gyada Kai tayi tareda juyawa ta fice zuwa gurin daddynta din.

Tana fita NURU tasake nadewa guri daya kaman jira Marar keyi ta kwanta tasamu nutsuwa sai ciwon yasake taso Mata wani irin zafi da zufa suka fara karyo Mata ta tashi zaune daqyar ta kunna AC Takoma ta kwanta tana shigewa cikin bargon dake kan gadon me tsananin laushi fari tas.

Kallon Mr Omar maleek yayi yace”

Kasan abinda zakayi next idan an daukosu din.

Gyada Kai Mr Omar yayi Yana cewa”

Za’a kaisu wancan gidan ne na 7579 zibrian kowa yasan aikinsa yakama suyi gyaran koina Kafin zuwa gobe ko jibi ku Isa can din.

Gyada Masa Kai maleek yayi Kai tsaye zai juya saiga farhat ta qaraso gurinsa ta shige jikinsa tana cewa”

Daddy aunt NURU batada lafiya bazata iya duba ciwona ba tace Akira min mum Sarah ko Dr” taqarasa fada tana nuna kafarta.

Kallon kafar sukayi dukkaninsu inda ruwan zafin suka zubar Mata a kafa sai alokacin sukasani ga ‘yar farar kafar tata har tayi ja 

Maleek ya dago ya kalli farhat din yace”

Aunt dinki bazata iya duba Miki qafanba ta gyara?

Eh daddy tun jiya da daddare aunt NURU tace cikinta na ciwo haryanxu be Dena ba gurin karbo Mata tea ne ruwan zafin ya zuba a kafana mum taketa fada.

Shiru maleek yayi kafin ya dago ya kalli Mr Omar dayayi saurin rage kansa Yana cewa”

Za’a kaita gurin Sarah acan zibrian ta kula da qafar kafin ku iso zankira Dr Damien ma yazo ya duba kafan Inshallah.

Kama hannun farhat Mr Omar din yayi Yayi gaba suka fice ya nufi mota ya bude ya sakata ya zagaya yashiga Yana waya da Edward akan idan sun Isa zibrian din da kowa yace Masa eh ankai kowa Babu Wanda aka baro a tsohon gidan sai tsohuwan madam da princess afia.

Previous page 1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button