HAUSA NOVELWACECE NI Complete Hausa Novel

WACECE NI Complete Hausa Novel

 

Wasu hawaye ne masu zafi suka sake zubo mata tace “Allah na tuba niya Allah” daqyar ta tashi ta shiga bathroom ta hada ruwa tayi wanka tadan qara gasa jikinta ta debi gishiri ta zubava ruwan ta shiga ta zauna ruwan yana ratsata tanajin dadinsa tana kuka me ban tausayi da ace ita wata me gata ce da a yau bazata kwana a gdannan ba ficewa zatayi ya cutar da ita ta bangarori da yawa batada wani amfani sai wajen kashe sha’awar sa ya nemata ya nemi matan banza yaje ya kwaso cutar zamani ya liqa mata shikenan tata rayuwar ta lalace kuma daga qarshe yazo ya saketa tunda dama saboda rashin matarsa ne ya aureta ita kenan tayi tara babu yanzu da tana gdan marayu ko bata samu gatan komai ba zata samu naci gaba da karatunta.
Sake rushewa tayi da kuka tabbas itama ya kamata tayi wani abu domin ceton kanta madam Helin tace kada ta bari ta dauki ciki domin shine matakin farko na shigarta gararin rayuwa a gdansa hawaye ne ya sake zubo mata ta miqe a kasalance ta nufi bathroom din ta debo gishirin da yawa ta jiqa a wani dan qaramin kofin glass ta kafa kanta ta shanye tanajin maqaqinsa a zuciyarta kuka takeyi sosai tana addu’ar Allah yasa ta mutu ta huta tananan kwance girkin da bata qarasa ba kenan sai Baba Zulai ce ta qarasa har zuwa lkcn da tayi sallar isha taji Baba na qwanqwasa mata qofar bata budeba sai cewa tayi itafa bazataci abincin ba ta qoshi yana parlourn yanajin yanda Baba Zulai takeyi mata magiyar ta fito taci abinci amma taqi dun sai yaji jikinsa ya qara sanyi ya miqe ya hau saman ya dauko master key dinsa ya bude dakin ya shiga tana gudundune a saman gadon tanata aikin kuka.

 

 

Zama yayi a gefen gadon yasa hanu ya yaye bargon ya dagota jikinsa ta fizge ta dira daga gadon miqewa yayi da sauri ya dannawa qofar key ya mata ya sake riqota ta zame tayi qasa ta kuma rushewa da kuka tace “Kullum da koda yaushe bana kai qarar kowa gurin kowa sai gurin Allah saboda shine ya halicceni cikin msqasqantan bayin da duniya take wulaqantawa Ina roqonsa yabimin haqqina a gurin duk wanda yayimin dole saboda rashin gatana yasani nayi abinda banyi niyya ba Marwan da ace zaka cire kanka a cikin rayuwata kabarni nayita ni kadai kamar yanda na farota tun farko da nafi kowa farin ciki don Allah don Allah na roqeka ka ka kyaleni ka tashi ka fita ko kuma ni kabani damar na fita daga gdanka”

 

 

Zuba mata ido yayi cikin tsananin tausayinta so yake yabar dakin amma ya kasa kawai sai ya zauna a kusa da ita yakai hanu ya ruqo hanunta ya sanya dayan hanun a aljihunsa ya zaro wani key da kudi yan dari biyar raffers ya dora Mata a hanunta yace cikin sanyin muryarsa “wannan kudin sadakin kine da dukiyar aurenki kamar yanda waliccin gdan da kika taso suka yanka mani ban samu damar yi miki lefe ba kamar yanda al’ada tasa akeyi Marwah shiyasa na yanke shawarar mallaka miki wani filina dake yankaba a zagaye yake amma babu gini a cikinsa miqewa yayi ya juya zai fita tayi saurin riqoshi tace.

 

 

“Bana buqatar komai daga cikin dukiyarka ka riqe abinka na yafe banaso” miqa masa kudin tayi tace “ka zare dubu ashirin dinka ka mayar aljihunka sadaki shine dole shima na wakiltaka ka badashi sadaka fisabilillahi” tana fadin haka ta juya ta shige bathroom ta kulle yabi bayanta da kallo cike da tsoro da mamakin taurin zuciyar yarinyar tunda yake a rayuwarsa baitaba yin kyauta an dawo masa da ita ba sai akanta sadakinta ma tace bataso ya bayar sadaka to me hakan yake nufi?
Daqyar ya iya daga qafarsa ya fita daga dakin ya nufi samansa shima abincin da baici ba kenan kwana yayi yana juyi ga qoshi ga kwanan yunwa yana tsananin buqatar kasancewarsu tare da ita amma yakasa zuwa inda take kalamanta sun mugun yin tasiri a zuciyarsa ko kadan baison shiga haqqinta yana sani duk da yasan bashi da wanda zai tuhumeshi amma Allah yafi gaban wasa duk mutumin da yace ya barka da Allah to gara ka janye daga gareshi kada ka fadawa haqqinsa ka shiga dari da hamsin baka sani ba.

 

 

Washegari da wuri ya tashi ya fita yayi musu booking na jirgin da zasu hau zuwa Germany yini tayi bata fito daga dakinta ba sai wajen azahar taji shigowar Baba Zulai ita da wata miqewa tayi daga gadon ga mamakinta sai taga Helin gabanta yayi muguwar faduwa murmushi Helin tayi tace “nasake dawowa tashi maza sauri nakeyi Marwah fito da wani qullin baqar leda tayi a Jakarta tace “na rubuta komai a jikin takarda Allah yasa kin fara practicing din abinda na rubuta miki a waccan takardar?” Baba Zulai ce tace “wannan yar takin madam bayan wauta harda quruciya take damunta wlh tun ranar da kikazo dinnan basu qara hada daki da mijin ba kullum cikin rigima suke to har garama jiya yayi mata dole ya turmusheta a kitchen amma tun jiyan nake ganinsu cikin damuwa daga ita harshi haba ayi mutum bayajin shawara yarinya kece fah a ruwa har ka shi bashida kaico sai danasani wlh gara ki zage dantse ki rungumi mijinki Marwah ni nake tare daku a gdannan nasani kuma na yarda Soja yanasonki wlh tunda nake dasu a gdannan baitaba yin tafiya da Hajiya Ra’isah ba duk sanda zaiyi tafiya cewa yakeyi bashi kadai bane shida abokan aikinsa ne”

 

Murmushi Helin tayi tace “bakomai baba kishine ke damunta kinsan abinda ciwo dan bamu guri” fita Baba Zulai tayi nan fah Helin ta zauna ta rinqa tsara Marwah tare da fada mata sirrikan da zatake tafiyar da mijinta dasu tasake jaddada Mata ta koyi hadiye fushi Marwan bayason fushi yanzu zai iya samata na shago saida ta tabbatar da tayi amfani da abubuwan data bata sannan ta qara jaddada mata kada ta bari ta dauki ciki yanzu sannan tasata ta tashi tayi wanka ta Kira meyi mata lalle tazo suka koma bayan gdan akayi mata lalle na ubansun ita kuma Helin tayi ta kama dogon gashinta ta gyara matashi dayake yanada mugun santsi ta yarfa mata kalba qananu sosai bayan ta sallami mai lallen suka koma ciki ta bata sherving cream da kanta ta shafa mata a hammatarta qasanta kuma tace “kada ki shafa kiyi amfani da wannan qaramin almakashi ki rage tsayin gashin kada ki rinqa aske gabanki gaba daya mijinki yanason gashi a gaban mace kiyi qoqarin ganin kin koyar dashi sucking din gabanki saboda yana qara danqon soyayya shan ruwan gabanki asirine me zaman kansa do dai mijinki yanada qyanqyami amma ke tunda shine ya bareki nasan bazaiji qyanqyaminki ba”
Helin batabar gdan ba saida ta tabbatar Marwah ta zama cikakkiyar amarya ta dauki wani mahaukacin haske tayi kyau sosai kamar aljana faffadan hips dinta Helin ta dora hanunta tace “kece tsarin halittar macen da Colonel Marwan yake mafarkin samu duk inda yaga mace me irin halittarki rudewa yakeyi ya kashe ko nawane ya biya buqatarsa da ita saboda yace sunfi ruwa sunfi dadi to gaki a gidansa Allah ya bashi na waje saisu huta”

 

 

Biyar Helin tabar gdan shikuma biyar da rabi ya shigo gdan kai tsaye dakinsa ya shige ya shiga wanka ya fito ya zauna saman gadon yayi tagumi yanajin wayarsa tana ring ya dauka ya duba yaga number Ra’isah yayi tsaki kawai ya ajiye wayar saboda zuciyarsa da idanunsa Marwah kadai sukeson gani.
Baba Zulai ce taje ta fada mata ya dawo ta matsa Mata akan taje ta sameshi a saman batason yimata musu saboda haka ta tashi ta shiga kitchen din ta dauki lemon Apple din da Helin tasata ta hada masa a wani kyakkyawan jug ta nufi saman cikin takunta na isa gabanta yana faduwa……….

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button