MAKAUNIYAR KADDARA 42

 

*Page 42*

_________________________

*MG’S SKINCARE*

Hi my peole????‍♀️

Are you tired of using different skincare product that won’t work on ur skin no matter what❓then trust me @mg’s skincare is the right plug for you????

Are you guys battling with pimples,dark spot, sunburn, acne, stretch mark,knuckle,dark armpit,damaged/bleached skin 

Have you getting dark due to childbirth or sun exposure????worry no more@mg’s skincare gat you covered✅

Want ur skin to glow buh you don’t like using cream/lotion try *mg’s herbal whitening black soap* nd you’ll achieve that free/shiny skin????????‍♀️

For those that wanna achieve that milky flawless skin that turns head wherever you go????????‍♀️ try mg’s  *beauty kit* that’s the secret to beautiful skin????you’ll 

get an amazing magic result???? you can also buy the soap nd combine it with any of our product to get more result????

Glow gang

What are you  waiting for 

Shop urs now before we get sold out again????

Mg’s product is 1in town????if you know you know kawai????

Nd mg’s products are organic they dnt bleach they are made with natural ingredients  that will make ur skin lk brighter nd tone ur skin???? it just bring out 

that hidden beauty in you????we HV everything available now so is time to glow dearies

Pamper ur skin????‍♀️

Shine like a bride????

Make ur skin brighter????

Glow????

Soap price:3k

Beauty kit:11k 

Chat 08062991549

Call 08064532391

Instagram: glow_with_mgs

Facebook:mg’s skincare

DNT forget to follow us????like/comment????

Team glow????

_________________________

*Page 42*

………..Cikin farin ciki Baffah da ƙanwarsa Mommy (Bilkisu) suka tari juna, duk da kuwa basu daɗe da rabuwa a london ba duba mahaifiyarsu Hajiya iya. 

Sama-sama suka gaisa ya shiga ciki watsa ruwa. Koda ya fito massallaci suka fice da matasan ƴaƴansa. Sai da aka idar da sallar isha’i sannan suka sake 

shigowa gidan.

     Sai lokacin matan gidan suka sami damar zuwa masa sannu da zuwa da ALLAH ya sanya alkairin ɗaura aure da sukaji a bakin ƴaƴansu. 

    Hakama Mommy ta shigo har falonsa inda aka shirya musu abinci tare, cikin farin ciki sukaci abinci shi da ƴar uwarsa. Sai da suka kammala suka sami 

zaman yin hira sosai, inda a cikin hirar ne Baffah yay kiran Khalipha ya sakashi ya haɗasu da Hajiya iya. 

     Tsaf ya kwashe mata komai ya sanar mata game da ɗaurin aure. Duk da yasan zatai farin ciki dama dajin haka sai yaji murnar data nuna ma ta zarta wadda 

yay zato, dan albarka dai ya shata har babu adadin ƙididdiga. Suna tsaka da wayarne AK da Huzaifa suka shigo ɗakin. Kai tsaye wajen Mommy data ware masa 

hannu ya nufa. Ya zauna kusa da ita tare da ɗan hugging ɗinta ta gefe yana murmushi har haƙoransa na bayyana. Dan har ransa yana ƙaunar ƙanwar mahaifin nata 

saboda itama tana ƙaunarsa.

        “Ina cewa zanje na gaisheki tunda wancan zuwan ban samu shigaba sai kuma gaki?”.

    Murmushi Mommy tayi dakai hannu ta shafa kan AK mai maganar. Tace, “Ja’iri anya na yarda dakai kuwa? Yanda ka ƙwace mana Inna ka kai London bamma 

tsammaci zuwanka nan kusaba. Nazata sai bikin su Saffiya, ashe ma kai zaka fara angwancewa kafin su. To ALLAH ya sanya alkairi ya bada zaman lafiya na har 

abada”.

      Kansa ya duƙar yana murmushi, akan laɓɓansa ya amsa da amin.

    Cikin tsokana Huzaifa yace, “Aini Mommy soma nake naga wace mai sa’a ce ta shiga tsakkiyar lailah Majnoon ɗin nan haka? Dan naga alamar itama da 

ƙarfinta take dan tun ɗazun murmushi yaƙi barin fuskar ɗan naki”.

    Dariya Mommy da Baffah suka sanya, AK kuma ya zubama Huzaifa harara da masa daƙƙuwa.

      Cikin dariya Mommy tace, “To ai kaga ya nuna maka shi ba matsoraci bane, cikakken jarumine tunda gashi har yaje ta biyu, kai kota ɗayanma ka kasa”.

       “Faɗa masa dai Mommy. Dan wlhy ban taɓa ganin matsoracin irin wannan yaron ba, maybe sai ya tsufa mu taimaka masa da wata yafendo a dangi”.

      Filo Huzaifa ya ɗauka ya jefama AK mai maganar, saurin cafewa AK ɗin yay yana masa gwalo. Su Baffah dai nata musu dariya. Dan kowa yasan dama inhar 

Huzaifa da AK suka haɗu duk rashin son maganarsa sai ya takura masa yayi harma suyi faɗa. 

      Suna tsaka da wannan nishaɗin Moos’ab da Haneef suka shigo ɗauke da little daketa faman zuba musu surutun da ba fahinta sukeba sosai suna dariya. 

       Kusan a tare suka ɗago suna sauke idanunsu akan little. Yayinda Mommy ta sauke wata sassanyar ajiyar zuciya tana kallon yaron ko ƙyaftawa babu da 

tsarkake sunan ALLAH buwayi gagara misali daya sanya wannan kamar mai ƙarfi tsakaninsa da AK, Huzaifa kuwa hannu ya miƙa masa alamar yazo. Amma sai ya 

maƙalƙane Haneef yana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya. 

       Haneef ne dake ɗauke dashi ya ajiyesa a tsakkiyar falon yana faɗin, “Bara muga wajenwa zai je”.

        Tsit falon yay sunason suga yaya za’a kwashe? Dan yanda little ɗin ke musu kallon ɗaya bayan ɗaya dolene ya baka dariya. Kamar wanda aka raɗamawa 

sai ya nufi inda Baffah yake, duk zatonsu wajen Baffah ya nufa, dan haka Baffah dake murmushi ya sake gyara zamansa. Yana zuwa gab da shi sai ya zagayeshi 

ya miƙa hannu zai tsinki appale ɗin dake a jikin flower ɗin kusa da baffan kamarma baiga kowa a falonba.

       Hannu baffa ya kai ya dungure ƙeyar little ɗin yana faɗin, “Like father like son” fuskarsa ɗauke da murmushi.

     A take duk suka kwashe da dariya, banda AK da yay ƙasa dakai kawai yana murmushi, dan shima dai yanda Little ɗin ya wanu basar da kowa ya bashi mamaki, 

dan sak halayyarsa na basarwa da mutane ke yawan faɗa masa ya iya.

      Hannu Baffah yasa ya ɗaukesa ya ɗaura a cinya yana faɗin, “Ja’iri, saika mana yanga dan kaga muna son ɗaukarka?”.

    Kamar little yasan mi baffan ke nufi ya wani ƙyalƙyale da dariyar data basu mamaki, dan sanda suka shigo duk da surutu yakema su Haneef dan zuwa yanzu 

ya saba dasu fuskarsa a turɓune take.

    Suma dai duk dariyar sukayi kafin Baffah ya mikama Mommy shi. Zuciyarta cike da rauni ta amshesa tana murmushi, har cikin ranta jitayi so da ƙaunar 

yaron na shigarta. musamman yanda yake kamanni sosai da AK kamar yayi kaki ya aje.

       Fita su Moos’ab sukayi dan son zuwa su huta. hakanne ya bama su Baffah damar tattaunawa akan zancen little dake lafe jikin Mommy. AK dai baice 

komaiba. Sai su uku suke maganarsu da juya al’amarin. Ganin sunata jefama AK tambaya a ɗan fakaice Huzaifa yace, “Niko dai zuciyata nason min wani hasashe, 

amma dai kubari zan sake bincike kafin kuji minene”.

        Baffah dake kallonsa yace, “Son faɗa mana mana karka barmu a tunani”.

       “A’a Baffah, banson inyi gaggawa ne, amma dai kuyi haƙuri na ƙara nazari akai”.

       Haƙura sukai suka barshi akan yayi nazarin. AK da dai dama ba saka baki yake a zancenba sosai ya miƙe yana faɗin, “Bara naje na kwanta wlhy na gani 

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button