RAYUWAR MACE 1

Hafsat Rano
Free Page (1)
Sanye take da hijabi ruwan toka dogo har kafarta, kanta a k’asa sanda zata wuce ta daidai majalisar mazan wadda kullum sai ta bi ta wajen idan zata je islamiyya tana kuma jin yadda suke maganar ta a kullum idan tazo wucewa, tun abin na damun ta har ta iiik ya dake makale a kafadarta ta jingine ta a wajen ta nufi dakin nasa kirjin ta n I’m aw dukan uku-uku.
Shi kadai ne a dakin daga gani ya gama shiryawa fita zai kasuwa, tun bayan da manyan yayanta maza suka taso sai ya zama ba kasafai Abban yake fita ba sai ya dau kwanaki yana gida yana hutawa.
“Sannu da hutawa Abba.”. Tace tana neman waje ta rabe dan ta riga ta san kwanan zancen, ya kwana biyu be mata maganar ba shiyasa ta dan samu nutsuwa a kwanakin
“Yawwa Asma’u, an dawo!?”
“Eh Abba.”
“Toh Madallah, sannu da dawowa.”
“Yawwa.” Ta amsa a ciki tana sake lankwasa kafarta
“Kina jina ko,akwai wani da yazo ko kuwa har yanzu dai?”
“Babu kowa Abba.” Tace a sanyaye dan tuni har yar karamar kwalla ta soma taruwa a idon ta.
Shiru Abban yayi be tanka ba, tamkar me tunanin abinda zai ce, bayan wasu yan dakiku ya kalle ta sannan yace
“Ko dai kina korar su ne Ma’u?”
Da sauri ta girgiza kai hawayen da take kokarin rikewa suka sakko. Kura mata ido yayi sosai sannan ya soma magana a nutse cikin son kwantar mata da hankali
Kanta a kasa tana jin Abban har ya kai karshe, cikin nutsuwa tayi masa godiya sannan ta mike ta baro dakin zuciyar ta na sake tsinkewa. Idan tace bata damuwa da rashin aure tayi karya. Tafi kowa son ganin tayi auren kamar yadda yake burin duk wasu iyaye da zarar yar su ta kai munzalin aure! Tabbas tasan duk wasu iyaye da yar su ke gaban su basu da kwanciyar hankali har sai sun ga sun aurar da ita gudun magana da abinda ka iya zuwa ya dawo. Amma kuma abu guda da mutane suka kasa ganewa shine, aure, haihuwa da mutuwa duk lokaci ne mutum be isa ya bawa kansa ba idan ba har lokacin ne yayi ba.
Da yan yatsun hannun ta, take kokarin kirga adadin kannenta da akayi wa aure kamar yadda ta saba a kowanne lokaci, ta riga ta san adadin su sai dai kirgawar na sake tabbatar mata da dole ne mahaifin ta ya dinga tunasar da ita a kowanne lokaci. Duk da shekarun ta ba wai sun ja sosai bane dududu a yanzu ne ta cika shekara ashirin da biyar sai dai yanayin yadda ake musu aure da kananun shekaru ya saka ake ganin ta tsofe a gida. Kannenta biyu da akayi wa aure karshe ,shekarar su sha bakwai dan haka idan zaa hada su da me shekara ashirin da biyar toh fa tabbas dole a dinga yi mata kallon taki aure.
Bata san kalar matsalar ta ba, dan ba zata iya tuna lokacin da wani ya tare ta ko a hanya bane. Ta kan zauna tayi ta tunanin ko dai ba zata taba aure ba a rayuwar ta? Kila bata da rabo shiyasa hakan ta kasance dan bata zargin kowa balle tace ko wani abu akayi mata. Ta bar hakan a matsayin wata jarrabawa ce a gareta wanda take fatan cinye wa.
Daga labulen dakin Ummah tayi, ta leko da kanta tana karantar yanayin ta kafin tace
“Ya kamata a dora girkin rana lokaci yana tafiya kafin yan makaranta su dawo.”
Da toh ta amsa ta mike, ta chanja kayanta zuwa karamar riga da skirt ta saka hula a kanta ta nufi kitchen rik’e da wayar ta a hannu, tana zuwa ta ajiye a saman cabinet ta dora ruwa a babbar tukunya sannan ta fito da kayan miya daga cikin ledar su ta soma gyarawa.
Maganar Abba taji a tsakar gidan nasu yana yiwa Umma magana akan dalilin dawowar sa bayan fitar sa kenan bata jin ma ya bar layin nasu
“H pollo upar fa mun hau titi sai ga kiran Yaya Asabe wai gasu nan zuwa gidan da wata muhimmiyar magana, dole nace ya juyo my dawo dan bansan wacce magana ce ba.”
” Gaskiya kam, toh Allah yasa muji alkhair”
Umma tace tana bin bayan sa suka shiga falo. Daina aikin gabanta tayi ranta na sake jagulewa jin Hajiya Mama zata zo, Itace mutum ta farko da abban su yake jin maganarta fiye da ta kowa a duniya, duk wani abu da tace masa toh fa an gama shi, ko da kuwa baya so zai amsa mata. Su biyu iyayen su suka haifa itace kuma take masa role din uwa dan tun yana karami iyayensu suka rasu suka barsu su biyu.
Turo gate din gidan yayi daidai da tsayawar bugun zuciyar ta, ta window din kitchen din da hange su suna shigowa ita da shi yana rik’e da handbag dinta ya makala ta a kafadar sa kamar wani mace. Daf da zasu karaso wajen kitchen din tayi saurin dukawa saboda kar su ganta, tana jin sanda Umma ta fito tana musu sannu da zuwa Abba na tsaye daga bakin falon sa fuskar sa na nuna jin dadin ganin Yayar tashi.
“Sannun ku da zuwa.” Abba da Umma suka dinga jera musu har suka dangana da falon sannan ta sauke ajiyar zuciya ta mike ta cigaba da aikin ta a nutse.
Tana cikin aikin wayar ta dake sama tayi kara, ta dauraye hannun ta a sink ta jawota tana kallon wayar, kawarta ce Safiyya take kiranta, ta daga tana saka wayar a handsfree ta ajiye ta suka koma magana.
Maganar da yaji ya sakashi dawowa da baya zuwa kitchen din, ya tsaya daga kofar yana kare wa halittar ta kallo wadda take sanye da dogon skirt da riga. Motsi taji, ta waigo sai kawai taga mutum tsaye a bayan ta har ya iso daf da ita yana kokarin taba ta.
“Lafiya!?” Tace tana matsawa da sauri har tana neman gogar tukunyar miyar dake saman gas din.
“Fine Baby, kin hadu.” Yace cikin muryar sa ta yan duniya, kallon sa tayi daga sama har kasa, zuwa kunnensa dake sanye da dankunne sai wani jibgegen takalmi da yake jibge a kafar sa, wandon sa irin wanda yake a yagen nan ne ta tsakiya sai askin kansa da ya kara nuna mata ainihin shi din waye.
Yaya Adam ne, tilon namiji a yaran Hajiya Mama kuma shalelenta, tun suna yara Allah be hada jinin ta da nasa ba dan ko haduwa akayi sai yaci zalinta, ya zage ta yace mata shegiya baka saboda duk yan uwanta sun fita hasken fata. Hannun sa taji a saman fuskar ta yana shafawa, tayi saurin bige shi tana watsa masa mugun kallo.
“Menene haka Malam!?”
“Comman sai kace wadda bata waye ba, kin ganki kuwa!? Haka kika chanja kamar bake ba.”
Hararar sa tayi tana sake matsawa baya, dan bata masa kallon me cikakken hankali ko a da ma, balle yanzu da yaje yayi rayuwar turai idon sa ya kara budewa.
Hayaniyar dawowar yaran daga school ya bata damar zamewa ta bar kitchen din tayi saurin zuwa daki ta dauko hijab din ta, ta saka sannan ta koma kitchen din, amma sai daga baya nan, tayi kwafa ta cigaba da aikin ta da sauri sauri karma ya dawo ya sake samunta dan ta lura bashi da kunya sam.
Fasa fita yayi wajen ya koma falon da ya baro su Abba yana zuwa zai shiga yaji Hajiya Mama na tambayar Abba akan maganar Asma’u ko har yanzu shiru, amsar da Abban ya bayar ya sakashi saurin fadawa dakin
“Uncle ni zan aureta.”
Duk suka bishi da kallo,
“Boy me kace?” Hajiya Mama tace fuskar ta kamar gonar auduga
“Yess Mom…”
Kallon Abba tayi, wanda shima yake kallon ta a daidai lokacin
“Kaji wani abun almara, Ashe Adam ne mijin shiyasa aka ta fama, kai Alhamdulillah nayi farin ciki sosai.”
Saurin sakin fuskar sa abba yayi duk da be san yadda zai misalta abinda yake ji a lokacin ba, farin ciki ko akasin sa? A zahiri babu abinda yafi so da ji kamar ace Ma’un sa ta samu miji, sai dai kuma be zaci haka ba, sannan be taba kawo mutum kamar Adam din a irin mijin da yake mata shaawa ba, amma kuma ta Yaya zai ki jinin Yaya Asabe!? Matar da ta so shi tamkar yadda uwa ke son dan ta?