NOVELSUncategorized

MUTUM DA DUNIYARSA 14 -15

*_????HASKE WRITER’S ASSO…._*
   *_????MUTUM DA DUNIYARSA….!!????_*
             _(ya dace ya gyara kansa)_
                 *_Bilyn Abdull ce????????_*
                *_[14➖15]_*


    
…………..Sosai Jiddah ke yaba k’yawun tsarin sashen hajia deluwa, dan bak’aramin kud’i aka narkaba gaskiya, gabanta ya fad’i saboda hango Hajia deluwa dake hamshak’e cikin kujera, taci kwalliya cikin wani ubansun leshi ruwan ganye, ga wani kamshi Mai kwantar da hankali datake zabgawa.
          Tunda Jiddah ta shigo itama Hajia deluwa kemata kallon k’asan ido daga k’asa har sama, sosai Jiddah taimata k’yau fiye da yanda hajia Hindu ta nuna Mata ita a hoto, dukda a yanzu cikin hijjab take kuwa.
         Gabanta Jiddah taje ta zauna a k’asa, cike da girmamawa muryarta a matuk’ar sanyaye tace, “Hajia ina yini”.
       Cike da yatsina hajia deluwa ta amsa da “lafiya amarya ya kwanan amarci?”.
      Shiru Jiddah tayi takasa amsawa, yayinda hajia deluwa keta wani ta6e baki tana gyara zamanta, cikin dakewar murya tace, “To amarya inason muyi magana ta fahimta dake, dan banason biyo miki ta hanyar da zaki gaza 6illewa, da farko dai kisani ina matuk’ar son mijina da dukiyarsa, babukuma wata danake k’aunar tazo ta haihu dashi bayan nawa y’ay’an, kullum burina dagani sai y’ay’ana mu mallaki komansa, a girme Na girmi Mamanki ma balle ke nasani, Alhaji kam inda su Yahuza auren wuri sukayi sun Isa Haifa masa kamarki matsayin jika, inason nabaki shawarar kibar gidannan tunda arzik’inki, Zan baki ko nawa kikeso domin kibarmin mijina, dan tabbas nasan dukiyarsa tasaki aurensa, dan Ku y’an matan yanzu duk inda naira take kuna a nanik’e, abinda yasa duk nake miki wannan jawabin cikin lalama saboda nakula kamar zakiyi hankali, sannan kece mafi k’ank’anta a matan da Alhaji yata6a aura adukkan aure-aurensa. Kifita kisamu saurayi dai-daike ki aure, inma baida kud’in aurenki Zan iya masa komai, ke nama tak’aita miki zance koda cikin su Ashir kikeso ki za6a (yayanta fa????????).
      Duk wannan maganganu da Hajia deluwa keyi kan Jiddah Na k’asa tana mamaki da al’ajabinta, gaba d’aya takasa fahimtar inda surutanta suka dosa, wannan wace irin macece?……..
      Kafin Jiddah tasamu zarafin amsawa sallamar matashin saurayi dazai iya kaiwa shekaru 29 ta karad’e falon.
      Cikeda washe hakora Hajia Deluwa ta amsa masa tana fad’in “Wai ina kashigene haka Ashir?”.
      Idonsa akan Jiddah yace, “Mami wlhy ina d’aki kwance abuna, wannanfa?”. ‘Yak’are maganar yana lasar la66a da nuna Jiddah’.
        Baki hajia deluwa tad’an ta6e, ”Amaryar gidance”.
        Sosai Ashir ya zaro ido waje yana kuma lek’a fuskar Jiddah, “wai mami dama wannan karon karamar kaza Dad ya d’akko mana? Kai dad yana yarfamu wlhy, inma auren zaiyi ya d’akko wadda kowa yagani zai yaba mana”.
      Harara Hajia deluwa ta watsa masa, amma batace komaiba.
      Jiddah kam gabanta saikuma fad’uwa yake, ga maganganun Ashir na sukar zuciyarta amma batako motsaba………
       “Kinga tashi ki tafi, kije kiyi nazari akan maganata”.  Maganar Hajia deluwa ta katsema Jiddah tunani.
      Dak’yar ta iya mik’ewa ta fice jikinta Na rawa, yayinda Ashir kebinta da kallo tamkar tsohon maye..


✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

         Ango Ali baisamu damar shiga gidan nasaba sai wajen sha d’aya, Malam Mustafa ne ya kaishi har gida, batare daya shigaba ya juya yana tsokanarsa wai asha angwanci lafiya.
     Murmushi kawai yay bai iya bama malam mustafa amsaba, danshi ba mutumne Mai yawan maganaba inhar baisoba, idan kuma yaso zakaji yanayi sosai mussaman ma idan tashafi addini.
       Cikin sanyin nan nasa tamkar mara laka a jiki ya k’arasa cikin gidan,  a hankali ya furta “Masha ALLAH” akan la66ansa saboda k’yawun da falon yayi, komai yayi cikin tsari dai-dai gwargwado, bai zaunaba ya nufi bedroom d’in Maimunatu.
     Cikin sassanyar muryarsa yay cikakkiyar sallama.
      Maimunatu dake kwance tad’ago idanu tana kallonsa da amsa sallamarsa akan la66a, sanye yake cikin wani lallausan yadi kalar madara, sai hularsa kube ruwan makuba dad’an ratsin kalar madarar, jikinsa Na fidda wani sassanyan kamshi maisaka zuciya nutsuwa.
       Shikam kallo d’aya yaymata ya janye idonsa tareda ajiye ledar hannunsa saman madubi sannan ya zauna a bakin gadon d’an nesa da ita. Tashi tayi zaune tana fad’in “Yaya Aliyu ina yini”.
        A sanyaye yace, “Lafiya lau Maimunatu, ya gajiyar hidima?”.
        Murmushi tayi kawai amma bata iya bashi amsaba sai wasa da gefen gyalenta da takeyi.
      Kuma kallonta yad’anyi kafin yakuma d’auke idonsa, “Ga abinci nan nasan kina buk’atarsa, danku Mata idan kuna hidima nakula bakuda lokacin cikinku”.
       Murmushi tayi idonta  akan bakinsa dake motsawa a hankali tamkar bashi ke maganarba….
    Jin tayi shiru saiya juyo ya kalleta, saurin janye idonta tayi akansa ta amsa da “to, nagode”.
       Karan farko daya d’an murmusa, ya mik’e yana fad’in “Bara nad’an watsa ruwa, kafin Na dawo kici abinci kiyi alwala…”. Kafin tabashi amsa tuni ya fice.
     Ajiyar zuciya ta sauke a hankali, tajawo ledar daya ajiye ta bud’e, gasashshen namane sai kayan fruits da abinda ba’a rasaba. Bata wani kwari kantaba taci abinta tayi nak sannan taje tayo brosh tadawo ta zauna.
         Kusan mintuna Arba’in saiga malam Aliyu ya dawo, sanye yake da kananun kaya wando dogo fari da riga t-shirt ruwan hanta, abinda tunda maimuna take bata ta6a gani daga gareshiba kenan, saka kananun kaya, gaba d’aya ta shagala da kallonsa saboda wani mugun k’yau dayay Mata, Yakuma komawa yaro d’anye sharaf, a ranta tana ayyana dama yana saka k’ananun kaya haka?……
      Malam Aliyu da yaga ta shagala da kallonsa ne yay murmushi yana zama kusa da ita gab tareda kai yatsansa tamkar zai tsokale Mata ido.
      Da sauri ta sauke ajiyar zuciya tana rufe fuskarta saboda taji kunya sosai.
     Murmushi yad’anyi, yana cewa, “Na canja mikine?”.
      “Sosaima”. ‘Ta fad’a har yanzu Idonta a rufe’.
      “Humm dama can kallon tsoro kikemin shiyyasa kike ganin Na canja yanzu. Ina fata kinyi Alwalan?”.
        Batare data bud’e fuskartaba tace, “Nifa Yaya ina up”.
      Baice komaiba sai d’auke kai dayay daga dubanta yana d’an sauke numfashi, kusan mintuna biyu yana mulmula maganar dazai mata a ransa kafin ya gyara zama yakuma fuskantarta.
        “Yaushe yazo?”.
    Tamkar zata nutse dan kunya haka taji, gyalenta taja takuma rufe fuskarta sosai kafin ta iya bashi amsa, “Yau”.
       “Babu k’yau k’arya, yau kwannansa biyu, nanda kwana hud’u zaki samu tsarki”.
    Babu shiri ta bud’e fuskarta tana ware idonta a kansa, “Yaya ya akai kasani?”. ‘maganar ta su6uce Mata batare da ta saniba’.
         Jikinsa kawai ya jawota batareda ya bata amsaba, cikin kunnenta ya rad’a Mata “Kinason sani?”.
       Gaba d’aya kunya ta rufeta, ga jikinta sai tsuma yake saboda jinta a jikinsa, shikansa hakance ke faruwa daga gareshi, amma ya daure kamar bayajin komai.
    Kusan mintuna biyu suna a haka kafin ya d’agota zaune sosai. “Tashi muyi magana”.
      Gyara zamanta tayi, taja gyalenta takuma rufe fuskarta sosai. 
        “Maimunatu da farko dai nasan kinada ilimin addini dana zamani, kinkai shekarun da zaki iya banbance dai-dai da sa6anin haka, inaso kisaka a ranki zamuyi tsaftataccen zaman aure tamkar yanda Manzon ALLAH (s.a.w) ya koyar damu, insha ALLAH Zan sauke dukkan hak’k’ok’inki a kaina iya iyawata, kema ina fatan hakan daga gareki. Nasan tunkan ki shigo gidana kinsan inada lalura wadda itace sanadin rabuwata da matata ta farko, to kisanifa har yanzu banida tabbacin samun waraka, sai dai muna fatan dacewa, wannan kuma saikin samu tsarikine zamu tabbatar, idan babu wani canji game da lafiyata to lallai bazan cutar dakeba Zan sallameki insha ALLAH, idan kuma an dace Alhmdllh, zaki zama Aliyu, Aliyu zai zama ke, mallakar Aliyu gaba d’ayansa kuma saikin zama jaruma wajen fahimtar abinda yakeso da Wanda bayaso. Nabaki satar amsa”. ‘ya k’are maganar da yaye gyalen data lulllu6a’.
      Saurin kife kanta tayi a cinyarsa saboda kunya, yayinda shikuma yay murmushi.



????ta gidan Sheikh Ali ina tayaki murna????⛹‍♀.



✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

               A gidan Umma kam bayan biki da kwanaki uku kowa ya Kama gabansa, aka barsu su kad’ai, daga ita harsu Walida babu Mai isashshiyar lafiya, kowa damuwa da tausayin Jiddah da kewarsa ta isheshi.
     Washe Gari dole Uncle yahaya yanemo likita yazo har gida ya sakama Umma k’arin ruwa saboda batajin dadi sosai.
      Bayan la’asar Zarah ta cire Mata saboda ya k’are, ruwa Mai d’umi suka had’a Mata tai wanka, suna tsaka da gyaran gidan saiga Abba.
      Kowacce kai a k’asa ta gaidashi.
       Bakinsa ya ta6e ya wuce d’akin Umma, dan ya lura yau su Zarah awani yanayin jin haushi suka gaidashi.
     Umma na zaune tana cin faten waken da Maman Sadiq ta aiko Mata Abba ya shigo, kallo d’aya taimasa ta d’auke kanta.
     Zama yay shima yana wani kumbura. Umma tace, “Ina yini”.
    Bai amsaba, sai tambaya daya jefoma Umma.
     “Yagana waike aurar da y’arne yasaki maida kanki haka? Lallai aiki ya sameki ashe”.
      Wani murmushin takaici Umma tayi kafin ta d’ago ta kalleshi ido cikin ido, “Koma minene ya maidani haka wannan ba matsalarka baceba, saidai inason maka tambaya d’aya. Shin nawa Alhaji Garba yabaka kabashi Jiddah?”.
      Gaban Abba ne ya fad’i, bakinsa Na rawa yace, “Yagana ban gane wannna maganar banzar takiba? Dan Zan bada auren y’ay’ana sai an biyani kud’i?”.
       “Humm Alhaji kenan, bar ganin ka fini shekaru wlhy kar nake kallonka, a ina kasamu kud’in biyan banki bashin da kaci musu?”.
      Harara ya watsa mata yana huci, “Shak’eni Na fad’a miki mana yagana?”.
         “Aiba saina shak’eka bama, zaka fad’ane cikin kwanciyar hankali. Wlhy Alhaji ka farka daga nannauyan barcin daya d’aukeka, wato ka ciwo bashin kud’i a banki lokacin da suka baka Na kar6a yayi bakadashi ko? Saboda kakashe kud’in akan matarka da y’ay’an Sonka yanzu anema kabada kud’in ko kaddarorinka hankalinka ya tashi ko? Karasa ina zaka nufa matarka tabaka shawarar Neman bashi wajen Alhaji Garba. Shikuma dayake tsohon banzane kaje da buk’atar kud’i yabuk’aci musanyarsu da yarinyata saboda ta tsole idonsa, wlhy danasan auren manufa kayi da Jiddah ko sama da k’asa zata had’e baza’ayi aurennanba. Amma ko yan………….”
      Wata razananniyar tsawa ya daka Mata yana mik’ewa a zabure, “Daga bakin wane mak’aryaci wannan zancen ya fito? Ko rantsuwa nayi babu kaffara nasan yahaya ne……..”
          “Kwarai kuwa nine?”. ‘Cewar Uncle yahya dayake shigowa yanzu’.
    Daga Umma har Abba juyawa sukai suna kallonsa, fuskar Uncle yahya a matuk’ar d’aure yacigaba da fad’in “Wlhy ko’a mafarkina ban ta6a zaton rashin son gaskiyarka yakai hakaba Yaya, yanzu dan ALLAH har nawa Jiddah take da zakayi wannan kulla-kullar akanta? Ashe har mutane masu mutunci sukazo Neman aurenta amma ka shirya musu k’arya? Namaka magana ka gaggayamin son ranka, Anya Yaya kana tsoron gamuwarka da ubangiji kuwa?”.
        “A’a bana tsoro dan Ubanka, shin komadai kaine Ubansu Jiddah ban saniba?”.
     Daga Uncle yahya har Umma a tsorace suke kallon Abba.
      Muryar Umma Na rawa alamar tahowar kuka tace, “Alhaji kana cikin hankalinka kuwa? Mu kake jifa da wad’annan munanan kalamin?”.
      Shiru yay yakasa bata amsa saboda ya fahimci 6acin rai ya sakashi yin kato6ara…..
     Uncle yahya yay murmushin takaici yana fad’in “Karki wani damu kanji da kalamansa Yagana, idan yamana sharri wannan yarage tsakaninsa da Ubangijinsa, dan shine zaimana hisabi, wannan kuma ni bazaisa naji komaiba saboda ban ta6a kwatanta aikatawaba koda a zuciya balle zahiri, ka saka a ranka kuma alhakin wad’annan bayin ALLAH kawai ya isheka ishara inhar baka rok’i gafararsu ba ka gyara mu’amularka dasu. Maman Nafisa ga magungunanki nan, ni nawuce gida”.
       Uncle yahya nagama fad’a ya fice abinsa.
     Umma ma tashi tai ta shige uwar d’aka abinta. Da sauri Abba ya bita.
          Da sauri tace, “kaga fitarmin a d’aki zakari, idan kuma ni kake buk’atar nafita to lallai yanzu Zan barmaka gidanka tafiyarda har abada bazan dawoba koda hakan yana nufin Zan mutu da igiyar aurenka a kaina”.
     Baki ya bud’e zaiyi magana tai saurin janyo hijjab d’inta “ALLAH ya baki hak’uri nizan fita”.
      Bai jira amsartaba ya fice.

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button