Uncategorized

A Bakin Aurenki Complete

baya,kamar dai da alamun an mata abu daga

gida. Murmushi Baban yai kan yace tazo.. _”mey

aka miki uwata?_ Hawaye ta dan matso halamar

6aci. _”Mama ce ta hana ni kud’in tara_. Kai

Abban ya k’ada yana murmushi kan ya sa hannu

a aljihu ba chanji,gudar naira dari ya fitar kan ya

nuna mata shagon kusa dasu taje tai chanji. Da

sallamarta ta shiga,ta gaida shi,shago ne na

kayan k’yallin mata na sawa, attamfofi da

laces,ga materials kala kala,d’uk zuwanta bata

ta6a shiga shagon ba sai yau. _”Salamatu y’an

mata,ina su Ummi?_ Murmushi tai mishi,dan tana

ganin shi gun su Baba, dattijon na da kirki da

fara’a, banda yaron shagon shi da koh k’allo bai

mata ba, _”suna gida,Baba ne yace aban chanji_.

Kai ya k’ada, kan ya k’allo na zaune a acikin

shagon rike da littafi halamar yana dubawa.

_”amm *Ja’afar*_.. Kai ya dago karon farko,

_”Na’am Abba_,, sai lokacin ya kula da Salma,

_”Ba wa Salma naira ashirin ta tafi kar tai latti_.

Kai ya k’ada kan ya kara k’allo Salman wacce sai

hange take koh za taga wani dan islamiyar su

tana mika hannu. _”k’ar6i man_.. Juyo wa tai

taga yana miko mata kud’i fuska ba fara’a, da

sauri ta k’ar6a tana tafiya tana fad’in _”na gode

Abba_. Da k’allo Ja’afar ya bita,yana ganin Ummi

ce mai rawar kai ashe sauran ma haka suke.

_customers_ ne suka tada shi ya shiga shagon.

Washegari ma sai ga Salma,wannan karan koh

shagon su Baba bata je ba tai shagon su Ja’afar.

Da mutane da kusan d’uk y’an mata ne suna

siyayya, yana ganin Salma ya had’e rai, sam yaki

jinin a 6ata yaro da kud’i, ita kam Salma harda

mishi murmushi tana dago mishi hannu da kamar

abu aciki. T’saki yai,kan ya cigaba da abinda ya

ke,sai da ya sallami kowa kan ya ganta tana

gaida Abban shi da ya fita yana nuna mata cikin

shagon. Da dan gudinta ta shigo,a tunanin shi

kud’i Abban yace ta kara k’ar6a gun shi,dan da

zumudinta ta gaida shi. _”dama Abba ne yace

in_….. Cikin fad’a-fad’a ya katseta, _”bani da

chanji nima yau,jiya an baki kinji dad’i shin_….

Shiru yai sakamakon idonta da yaga ya cika da

k’walla tana k’allonshi. D’uk kuma sai jikinshi yai

sanyi.. A hankali ta ajiye masa gudar naira

ashirin akan benci ta juya tana goge hawaye. Ba

dai kud’in shi ta biya shi ba dan ya mata fad’a?

Da sauri ya d’auka da niyar k’wada mata kira ya

mayar mata sai dai tuni tai nisa sosai. D’uk

kuma sai yaji bai k’yauta ba. Yana nan zaune har

Abba ya dawo, _”kaga Salamatu wai kud’in ka na

jiya ya hau shine ta dawo ma dashi ba”_.. K’allon

Abban yai da sauri, _”Abba kud’i kuma?_

K’allonshi yai kan ya k’ada mishi kai, _”sai da

nace ta tafi wai A’a tana da wani,Salma ak’wai

hankali, ashe batai ma magana ba?_ Shi dai

Ja’afar yai shiru yana jin Abba,sai ya kara jin

wani iri.

Download

[ad_2]

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button