SAMEEHA M

????SÂMÊÊHÂ????_*
(M)
“Mona na tsaye ta saki baki da hanci tana kallon ikon Allah momy ta katse ta,ta ce””” ƙaraso mana ki zauna indai Sameer ne kya kwana ki yini kina mamakin chanjawar sa mu kamu abin duk ya ishemu yanzu nan sai yace bai sani ba gaba ɗaya,mona ta dubi momy tana mai ƙaraso cikin fallon waje momy tayi mata nuni data zauna akan kujera mona ta zame ƙasan kafet ta zauna tana mai cewa””
“To ko bashida lafiya ne momy?
ƙwarai ma kuwa ke a tunaninki ina me hankali zai yi irin wannan abun mutum yace bai san nasa ba kwata kwata a rayuwa daga baya kuma ya dawo ya ce nasa ne ai ko ba afaɗa ba an san lafiyar Sammer da sauƙi Allah ne kaɗai yasan dalili amma muna addu’a kullum akai.
taɓɗijam amma ita kuma waccen data bishi wace ce ita ina kuma Ya Sameeha take?
duk a jere mona ta jefawa momy tambayar da yasa gabanta faɗuwa ta maze tace.
hmmm Zainabu abu kenan muna kiran ta da zee,ai ƙanwar sa ce ita ba anan tayi karatu bane shiyasa baku santa ba taso zuwa lokacin bikin Sameer Allah bai yi ba sai data kammala karatu,mona ta kaɗa kai ta ce
Allah ya bada sa’a.
Amin,momy ta amsa mona ta kuma cewa
“Ummm momy naji kuma ya Sameer yana ta tashi suje suga wajan da za’ayi bikinsu.
shiyasa nace miki kaɗan daga shiriritar Sameer gaba ɗaya ya susuce ya sauya daga yanda yake,kullum magana ɗaya yake nanatawa akan biki biki sai kuma ya juya akalar maganar tashi akan ƙanwar sa, ita kuma tana biye masa ne don asamu sauƙin abun dafari sharesa take tayi ta masa faɗa akan shirmen dayake yi data fara sai ya kwanta kamar yaro ɗan goye yayi ta kuka yana birgima har yasamu kuka gaba ɗaya ai wannan ma da sauƙi akan farkon abin ga lemo ki ɗauka.
Alhamdulillahi, Allah kuma ya bashi lafiya banga ya Sameeha ba ko tana ɓangaran ta ne,a hanzarce momy ta cewa mona.
Aa bata nan ma gaba ɗaya sunje amsowa Sameer magani wajan wani malami.
wayyo Allah zata dawo da wuri?
gaskiya banaji zata dawo da wuri dan fitar ta kanan kika shigo amma ki jirata mana ai bakya tafi baku haɗu ba.
wai Umma tace kar na jima idan nazo na koma gida da wuri kinga bana zauna jiranta ba,ban san sanda zata dawo ba gashi kin ce basu jima da fita ba.
wallahi kuwa ga wajan da nisa amma tunda Umma tace ki koma gida da wuri to gwara ki koma ɗin kar muma muyi laifin gaba ɗaya.
ai yanzu kuwa ga wannan saƙonta ne inji umma idan ta dawo abata ace ina gaishe ta sosai amma naso ganin yaya Sameeha wallahi mun jima bamu haɗu,”bazaku ki ganta ba sai dai kiga gawarta in Allah ya yarda kun rabu har abadah,a zuci momy ta furta fuskarta sawai sai murmushi takewa mona dataga mona ta miƙe tsaye, ledar hannunta ta miƙawa momy tasa hannu da sauri ta karɓa tana ƙara faɗaɗa murmushinta daga chan ta ce”
jirani ina zuwa akwai saƙon da zan baki ki kaiwa Umma da baba har da naki mona.
to dakin barshi wallahi idan na amsa duka Umma zatayi mun ta hanani amsar abu idan an bani.
ai ba wani abu bane mona kuma nasan kikacewa Umman ni na bayar abasu bazata ce komai ba saboda an riga an zama ɗaya mai da Alkhairi ga wanda ya baka sam bashida kyau kinji mona.
to shikenan,an gode Allah yasaka da alkhairi dan Allah in ya sameeha ta dawo a gaisar min da ita ace zan dawo nan kusa insha Allah in kuma ita tazo shikenan.
in Allah ya yarda zan faɗa mata wataƙila mu taho tare nima ina son zuwa mu gaisa da umma,momy na magana tana miƙawa mona turere guda biyu da rafar ƴan ɗari biyar bandir ɗaya,hannu biyu mona tasa cikin girmamawa ta amsa har da ɗan durƙusawa ta kuma yiwa momy godiya ta fito daga ɗakin,duban ɓangaran sameeha tayi taji gaban ta na faɗuwa a haka ƙafafuwan ta aske jikinta yai sanyi ta juya tayi bakin get ɗin baba me gadi ya miƙe da sauri zai buɗe mata ƙofa tace yabarshi ita da kanta zata buɗe.
Tun da mona ta shigo gidan Sameeha ta hango ta ta windon ɗakinta daya zama abokin hirarta a kulum anan take yini tana kallon duk wanda zai shigo ko zai fita dayake yana kallin get ɗin gidan har sanda mona tafito zata tafi sameeha na manne a jikin windon tana kuka da ƙanƙamar windon gashi kukan take da yunƙurin yiwa mona magana amma bakin gaba ɗaya ya riƙe sai rawa yake kamar me jin sanyi nan da nan hawaye da gunjin yasaka sameeha maƙyar ƙyata.
Sai da momy ta tabbatar Mona ta fita daga gidan dan har bayan ta ta biyo tana tunanin zatayi ɓangarna sameeha sai kuma taga tayi tafiyar ta,momy ta farke ledar da mona ta bayar abaiwa sameeha cikin sauri dan ganin abinda aka kawo,hannu tasaka ta fara ciro gyaɗar suya kusan rabin kwano da daddawa da kuka sai kuɓewa da kayan ƙamshi duk a dake momy tayi tsaki ta ce”””
“Duk ashe safgar tsiya ce aciki babu abu guda ɗaya da zai amfane ka talakawan banza ƙwaɗayayyu kun kawo ƴa kuna bibiyar ta da kuka da daddawa wai nan tsaraba ba kuka ba ko meye kunyi asarar banza dan ita kanta ƴar taku asararta zakwi tunda kuka so wa zuciyar ku,tana gama faɗin haka ta miƙe ta fito da ledojin a hannu tayi ɓangaran sameeha.
a ƙanƙame da windo ta isketa fuskar ta cike da hawaye,momy ta saka dariya har da tafa hannuwa ta tako daf da sameeha,ledojin kukar da kubewar ta ɓarke su akan sameeha ta zazzaga mata,cikin sauri sameeha ta rintse ido ta kara fashewa da kuka sai dai ayanzu muryarta zaƙwai ta fito saɓanin da,momy ta daka mata tsawa ta ce””
“Ashe kin ga matsiyaciyar ƙanwar taki gashi kuma babu halin yin magana,tura wa sameeha ledar gyaɗar momy tayi gabanta da ƙafa ta ɗora”””ga sauran tsiyar taki nasan zatayi miki amfani ko da ruwa kya kora daga gyatuma mai idon cin nira,bata ƙarasa rufe bakin ba ta fakaici idon sameeha data fara ƙoƙarin janya ledar tana ƙoƙarin sakata a jikinta tunda taji momy ta ambaci Ummanta tasan daga hannunta ledar ta fito,babu zato babu tsammani momy ta farka ledar kayan ƙamshi ta zazzagewa sameeha aka har cikin idanun ta,wani mugun ƙara da zabura sameeha tayi zata miƙe momy tasa ƙafa ta daketa ta koma ta zauna a jikin ledar da momy ta tura mata,sameeha na kuka ta kuma rarumo ledar ta ƙanƙameta a ƙirjinta kamar wacce za’a ƙwacewa ta shiga kiran.
“”Umma!!!,Umma!!,”kizo ki ƙwace ni zan mutu umma ido, hancina Ummata zata kasheni ban gankiba Umma…….
sake tura ledar jikinta take tana ƙara ƙarfin sautin kukanna ta,momy ta ke ce da dariya tana,”””
“Kafin uwarta ki tazo nayi yanda nakeso dake,bari kiji suma basu tsira ba dan daf suke da faɗawa komata shegiya matsiyaciya talaka sai na makantaki na kurmantaki sannan na nakasaki yanda babu mahalukin daya isa ya shaidaki,tayi ficewar ta tanayiwa sameeha dariya.
Cikin kuka da azabar yajin da sameeha takeji ta rarrafa ido rufe ta fara laluban banɗaki,cikin ikon Allah ta shafi ƙofar da kokawa ta murɗa key ɗin ta rarrafa banɗakin ta shiga,neman wajan da kan famfon yake take ido a rufe ga hajin da kamar ƙara zuba mata ake garin lalube taje ta daki jikin bango da goshinta dayasa ta zubewa a ƙasan banɗakin tasaka sabon kuka tana shafa wajan daya fara tashi,sai data ɗan huta ta ƙara rarrafawa tashiga shafa ko ina a hankali tana bin bango har Allah yabata sa’a ta kama famfon ta miƙe tsaye da sauri ta kuna kan ruwa ya fara zuwa, fuskarta ta ɗora a ƙasan famfon tasakar mata ruwa haɗe da gwale idanuwan ta duka biyun……………