Babban Burina A Yanzu Na Samu Miji Na Gari Nayi Aure >Fati Zinariya

Bayan nan kuma ya hada ni da mutane sosai wanda suka sassa ni a fina-finai abokanansa ‘yan uwansa duk dai gashi nan dai, gaskiya ba abinda zan gaya masa sai dai na ce masa Allah ya saka masa da gidan aljannah, babban addu’ar da zan masa kenan, Allah ya raya masa zuri’ansa, Allah ya kara masa zaman lafiya da shi da matarsa da ‘ya’yansa gaba daya, Allah ya bashi arziki dauwamammiya duniya da lahira. Ba zan manta da shi ba kuma ni abinda yake min dadi daman ta wafarsa na fado sai kuma Allah ya sa ta wannan kafar nan nasa kuma Allah zai daga sunana na yi suna a duniya har kowa ya gane ni ya san wacece ni ba zan manta da kai ba Yaya Lawan ina alfahari da kai, ba abinda zan ce maka duk inda kake alkhairin Allah ya kai maka, duk inda kake Allah ya rabaka da masifa ya rabaka da iyayenka duniya da lahari.
Kamar Yadda kike tashe a yanzu, idan miji ya fito za ki iya barin fim ki yi aure?
(Dariya) A guje ma tab! Tabijan ai raya sunnar Manzon Allah (SAW) gaba take da komai, ai ba abin da ya fi aure a duniyar nan, kuma duk wani dan sunnah shi ma zai so ya yi auren sunnah saboda shi ma ya fi dan sunnah ko babu komai na ga ‘yan ‘ya’yayena ‘yan dagwas-dagwas in musu kwalliya in gyara su in gan su tsaf-tsaf! in kale su na ce wannan ‘ya’yana ne? na daga hannu na gode wa Allah, tab! ai wallahi ba abin da nake so yanzu duk duniyar nan babu wani abu da yake gabana babu wani abu da nake so Allah ya nuna min shi da idona a ce yau na bude idona na ganni a gidan mijina auren raya sunnar Manzon Allah (S.A.W), ba ni da alfaharin da ya fi wannan wallahi shi ne babban burina duniya da lahira.
[ad_2]