BAK'A CE 1-END

BAK’A CE Page 41 to 50

Nan suka wuni a ranarma, sai a wannan ranar da zasu tafi Khadija ta bi su, rabonta da gidanta tun fitar da Mu.azam da aka yi,

Suna zuwa ya sauke su ya yi tafiarsa masaukinsa

Bayan gama al.adunsa na yau da kulun ya mike saman bed hankali kwonce ya shiga wayarsa,

Whatsupp ya fara shiga, nan ya nutsu ya yi ta yiwa mutane response kan message dinsu, harda su voice,

Yau kam Basma ta ja ra.ayinsa, dan ya ga dan kokari harda su voice,

Shiga ya yi ya kunna voice din nata yana saurara,

Kansa ya girgiza yana murmushi kafin a fili ya ce” Mata kennan,

Fita ya yi ya shiga wajen message dan daukan number da sergent ya turo masa na mutumen da zai canzawa su Mu.azam gida, dan angiwar batai masa ba,

Nan ya ga message din Mu.azam har guda tara, 

Shiga yayi yana fadin” shi kennan tun ina Niger ya tura min wasiyoyi dan ya kashe ni lokacina bai kai ba ko? 

Murmushi ya yi yana mai jin nishadin da ya kwana biyu bai ji ba tunda aka yiwa Mu.azam aiki,

Message din ya fara karantawa kamar haka 

*Na yi shigar wuri, sauri sauri nake na dandanna zakin aure kafin na tafi*

*Ni mai laifi ne, ban san ya zaka dauki lamarin ba*

*Kar kai hukunci cikin fushi, kamar yanda na jima ina neman shawara da bin lamarin a hankali , ban aikata ba sai da na yi zurfin binkice da neman zabin Allah*

*An ce abinda ka ji hankalinka ya fi karkata ya fi kwonciya idan ka kasance ka barwa Allah zabi ta hanyar yin stihra, Wardugu a kulun na kwonta da barwa allah zabi na farka wannan dai shi ne zabin*

*ban rainata ba, hasalima na sota fiye da tunaninka, sai dai a lokacin ban gani ba, sai da muka dawo na fahimta*

*Wardugu, gagawa na yi, na yi gagawa, na yi mugun gagawa, ka yafe min*

*ni wani sadaukarwa na tabai maka? Ka mini da yawa wardugu ciki harda kudin karasa karatuna, ka mini dayawa*

*Wardugu, na bata a rubuce, shaida, zan kuma turo maka…..Ni Muhammad Mu.azam na sawakewa matata Agaishat aurena dake kanta, wato na tsinke igiya daya cikin uku, ba dan ta min laifi ko wani abin ba, zamanna da ita ne ya kare*

Daga nan Wardugu ya tsaya a bin messages din Mu.azam wanda sauranma na ban baki ne,

Wayar ya saki ya mike tsaye cir daga kwoncen da yake,

Gabansa ne ke wani irin dokawa , hankalinsa ya tashi,

Wani irin ihun bakin ciki ne ya saki wanda da a lokacin Mu.azam na a gabansa ba abinda zai hana ya shake shi har sai ya shaka masa kanshin mutuwa,

Daga shi sai singiletin nan ya fito rai a mugun bace hankali a tashe ya karbi kys dinsa ya fitar da motar a garaje ya…….

                   Comment comment

???????????????? *BAK’A CE* ????????????????

https://www.facebook.com/Idan-rana-ta-fito-writers-association-114558343535568/?referrer=whatsapp

*☀IDAN RANA TA FITO WRITER’S ASSO????* ____________________________________________

             

*Fad’akar da al’umma tare da nishad’antar da masoya shine fatanmu*????????????????

                            Na

                     *SAJIDA*

                          5️⃣8️⃣

Tuki yake na garari, ba bin doka , ba tsare iyakar gudu da mota a cikin garin paris, wanda hakan ya saka motar police bin bayansa tana mai nunin ya tsaya aman fir ya ki ya tsaya,

Bai zame ko.ina ba sau gidan Mu.azam,

Yana fitowa daga motar police din ta fito da sauri tana mai nuno shi da bindiga da fadin ya tsaya ko ta harbe shi, 

Hakan ya janyo hankalin daidaikun mutanen dake anguwar, wasu na dan lekowa ta takarsu, wasu na fitowa dan ganninnko barawo ne aka biyo har anguwarsu? Ciki kuwa Harda Khadija da ta ji haya hayar ta yi yawa,

Rai bace ya ja ya tsaya ya juyo yana mai saka hannunsa cikin aljihunsa na wandon dake jikinsa hakan ya saka ta kwala karan ya tsaya kar ya kara wani motsi a yanda yake!

Tsayawa wardugu ya yi, dan ya san in ya kara motsin a hakan hukuncin harbi ya hau kansa,

Da gudu ta karasa tana fadin ya daga hannayensa sama,

Kansa ya girgiza da yaren french ya bude baki rai bace ya ce” sunana General Wardugu Marahutt, ki barni na ciro maki shaidar hakan, kar ki saka min hannu a aljihu! 

Ya karasa yana mai kuwa a kanta,

Da sauri ta ja ta tsaya daga niyar caje aljihun nasa ta dan ja baya still dai bata sauke bindigar ba, ta shishiryawa ko ta ware ko ta walare,

Ciro mata baje dinsa ya yi ya mika mata a dake, 

Da sauri ta karba ta karanta, ta ga hoton sama da komai,

Da sauri ta sara masa, domin karatun da wardugu yayi na bashi power a kasashen wajema ba a iya niger kadai ba, dan haka ta bashi hakuri tana mai fada masa ta biyo shi ne daman dan ya taka dokar fice ka.idar gudu a cikin gari 

Karba ya yi ya juyo inda itama ta shiga magana da wayar hannunta tana fadin shikennan kar a turo mata kowa General Wardugu Marahut ne na Niger .

Ko kallon Khadija dake masa magana bai yi ba ya shiga gidan ya karasa ya shiga danna karaurawar dakin ba tare da ya bari ta numfasa ba ya ci gaba da dannawa,

Dirowa ta yi daga bed, kayan baci masu santsi sakaku ne a jikinta dogon wando da riga har gwuiwa, kanta ta kunce shi ya bazu a gadon bayanta sai turaran ruwa da ta shafa a jikinta ta kwonta ta huta bacin da bata yi ba wannan karan haka ya firgitata,

A firgice ba tare da ta tuna da wani rufe kanta ba ta fito da gudu gudu ta zo ta bude dakin

Bata shirya ba, bata san zata ji ba, kai batama san wai hakan zai faru ba sai jin saukar wani fitinanen, gigitacen hautsinanan mari da ta yi imanin da bata yi fitsari kafin ta yi shirin kwonciya ba da ta sake shi ba wani ja.

Jinta da ganninta ne suka dauke na wani dan lokaci kafin take samu su dawo, a tsorace ta shiga ja da baya jikinta ya kwashi bari tana dubansa ba tare da ta yi masa magana ba, Khadijama a tsorace take biye da bayansa tana mai dora hannu a kai da fadin” Wardugu?

Wardugu da har jikinsa ke rawa shima na bacin rai ya ce” ashe ya sake ki kike zaune a gidansa? Wannan wani irin natacen so kike masa da har zai sake ki , ki ci gaba da zama a gidansa kina shan ruwan gidansa? Tir tir tir da wannan zuciyar Agaishat sai yaushe zaki fadi cewar ya sake ki? Ko jira kike ya dawo ki lalabe shi ki bashi hakuri ya mayar da ke? Tambayarki nake kike kallona tamkar kin samu sabuwar halita? 

Bakinta na rawa tana kankame jikinta dan har lokacin marin na ratsata, sannan wani mahaukacin tsoronsa ne ya diro mata wanda bata taba ji ba, a yanda ya zo bata taba ganninsa daga shi sai yar rigarnan ba, ga abin bacin rai gaba daya wani yannayi nasa dake boye sai ya bayanna, kirar jikinsa, jijiyoyin jikinsa, gashin kansa ba a nitse ba aman a waje guda sama saman ne ya tatashi, 

Bakinta na bari ta ce” ban ban gane me kake nufi ba Ya Wardugu, ban gane me kake cewa ba, wa aka saka? Me me 

La ferme Agaishat, (churup Agaishat) ki min shiru kar ki fada min karya a nan, bai baki takardar saki ba? Ko don son da kike masa zaki ki gwadawa ne? Na tashi na je gidanku mahaifiyarki ta damkan amana gashi ba.a je ko.ina ba har na ci? Ina takardar da ya baki tun kafin na karya ki gida biyu!?

Zubewa ta yi kan gwuiwoyinta ta hade hannayenta inda tuni kuka ya kece mata, tana kukan ta ce” sai nake jin kana nufin kamar mijina ya sake ni? Ya sake ni? Me na masa? Yaushema aka yi auren da har ya mayar da ni karamar bazawara? Wani umarninsa na taka? Sannan ni dake zaune a gidansa ban san da ya sake ni ba? Har aka tafi da shi asibiti *yana shigowa har dakina*,

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button