BAK’A CE Page 51 to 60

Gabanta ne ta ji ya fadi, tunda suka dawo daga Paris bai fi sau a kirga ba suka hadu, ya yi tafia kan aikinsa, da ya dawoma baya wani yawan zuwa gidan sai jifa jifa sai matarsa dake dan lekowa a tsatsaye ta fice abinta,
Kallo daya ta yi masa kafin take juyar da kanta ta nufi wajen Alhinayett ta fada mata cewar Wardugu ne, ita kuwa ta dauki lafayarta ta nada a iya kugunta ta juya neman abin hura wutar,
Alhinayett ce ta sanyo shi gidan, inda yan matan du suka shiga watsewa a hankali dan kowace ta san shi farin sanni basa son abinda zai hada su da shi, ya rage daga Alhinayett dake zaune facing dinsa, sai Agaishat da Jida dake dan nesa da su suna aikinsu na dafa shayi da Barbecue.
Gilashinsa ya cire yana duban Alhinayett kafin ya sakar mata murmushi ya ce” inyeh amarya,
Alhinayett ta turo baki ta ce” kafa ce ba zakana tsokana na ba.
Murmushi ya sakar mata ya ce” ai ba tsokana bane ,
Alhinayett ta ce” War, wai dan Allah da gaske an karbi kudin?
Wardugu ya kanance idonsa guda ya ce” ke baki da kunya ko? Da ba.a karba ba ya zaki yi?
Kafadunta ta daga ta ce” ba sai in ci gaba da zama a gidan ba, kai kuma in ci gaba da damunka ba, ????????♀️
Ya miko hannunsa zai lalace hancinta yana murmushi dan wani nishadi yake ji Aminiyarsa kanwarsa zata yi aure kwana kusa kennan jiddah ta kwala ihu ta shiga bura tana kokarin dage lafayar Agaishat
Agaishat din kuwa ta rintse ido ta kasa motsi inda take tsugune
Da sauri Alhinayett ta nufe su tana tambayar lafia?
Jida ta nuna mata cinyar Agaishat ta ce” ina ziga shayi ne ashe ta kawo hannunta ni kuwa na juyo shine ya zubun mata a nan,
Alhinayett ta aniya janye lafayar bayan ta dungure kan Jidda tana fadan ke komai zaki yi ba zaki yi shi hankali kwonce ba sai da katsamniya tamkar wata saniya?
Agaishat kam zufa ce ta ji a goshinta inda idonta ke rintse, dan Walahi bata ji zuwan abin ba sai zubarsa ta ji saman cinyarta , gashi ya gama tafasa kennan ga zafin shayi, ji take gaba dayama kamar kafar ce ta tsoma cikin ruwan zafi
Wardugu dake zaune bai san lokacin da ya rintse ido ba jin abinda ya faru, kokowa ya shiga yi da zuciyarsa da tunaninsa kan kar ya mike, kar ya je, kar ya je, ga kururuwar kanwar Alhinayett din nan dake kara caza masa kwakwaluwa, a hankali ya lalubi hanki yana kokari goge fuskarsa da bai san me zai goge ba wayarsa ta shiga kuka,
Lalubar wayar ya yi da sauri ya daga kiran baima tsaya gannin waye ba,
Walyn dake tuka mota ta ce ” Wardugu, gamu mun fito daga gidan su Alhinayett din an ce wai ba can take ba, ina ne gidan da take mu je?
Wardugu ya shiga yi mata kwatancen gidan kafin yake datse kiran ya tsurawa yatsotsin Agaishat ido domin Alhinayett ta kawota wajen tabarmar ta zaunar da ita da kyar ta samu ta bude wajen ta saka a kawo mata ruwan gishiri ta shiga tofa mata adu.a,
A hankali idannuwansa lumshe yake kallon yatsutsan kafar nata, dogayen yatsutsan kafa gareta, wa.inda suka kawatu da faratuna masu dan tsayi farare kar kar aman can samansu da dan jan lale, kafarta ta dama na dauke da dan karamin yatsa irin shidanin nan, sai yan kananun gashi dake saman kowace yatsa luflufluf da su,
Tsikar jikinsa ne ya ji ta tashi a hankali yake kokarin kawar da kansa sai dai ruwan gushirin da Alhinayett ta zuba mata ya saka ta jimke hannun Alhinayett da hannunta guda sannan ta kawo dayan hannun wajen kafar nata mai shidanin ta damki kafar ta cije lebenta kafin take kifa kan nata saman kirjin Alhinayett ta shiga sauke ajiyar zuciya,
Zabura ya yi ya karbe kofin ruwan giahirin kafin ya zabgawa Jida wata uwar hararar da ta sakata juyawa sumui sumui ta bar wajen ta koma wajen gashinsu a ranta tana ayanna kumurci!
Tsayuwa ya yi a kansu wanda ya saka Alhinayett dagowa tana dubansa,
Murmushi ta saki kafin ta girgiza kai a ranta tana ayanna zan ga gudun ruwanka gide, in sha Allah yar buzuwa ba zata bika ba kamar yanda sauran yan matanka ke binka, da yardar Allah zaka kawo kanka ne,
A hankali ya duka ya ci fuaka ya kai hannunsa ya daga wajen da ta kone din,
Wajen ba wani tashi ya yi ba aman ya yi duhu alamun jini ya kwonta,
A rayuwarsa ya ga ciwon da ya fi wannan girma, shi kansa a jikinsa ya ji mugun ciwon da ya fi wannan dan har harbinsa an taba yi,
Maganar zubuwar ruwan zafi kuwa idannuwansa sun ga abinda da za.a maimaita a yanzu ba zai iya fayacewa ba,
Sai dai abin mamaki wannan dan ciwo da ta ji ya ji hankalinsa ya yi mugun tashi, bai san lokacin da bakinsa ya buda ya dubi Alhinayett kan wada ya ji haushin tunda ya shigo gaisuwa daya kwal ta yi masa bata wani zo inda yake ba ta kara gaishe shi ba, ya ji bakinsa na fadin” mu kaita asibiti alhi
Alhinayett ta dube shi da mamaki, zata bashi amsa wayarsa ta kara daukan kuka,
Mikewa ya yi ya daga yana cusa hannunsa cikin sumar kansa ya amsa kiran,
Eh kawai yace kafin yake datse kiran ya juyo da dubansa wajensu inda ya sauko da gilas dinsa ya rufe jajayen idannuwansa wa.ina a yanzu ne suka dauki jan, labarin zuciyarsa ne ke isarwa gare su
Fitowa suka yi daga motar, ita da aminiyarta yar gidan gwomna matar minister,
Kowace ka duba sai ka kara duba domin tun daga suturun jikinsu zuwa kalar fatarsu da irin adon fuskarsu da takalman kafafuwansu da jakunkunnan hanayensu da irin kanshin da suke bazawa zaka gane manya ne ,
Fuska Walyn ta yatsina tana duban kawarta kafin suke bushewa da daria,
Kawar ta ce” wai ke da yarinyar yar gidan talakawa dangin talakawa ce har haka? Ke da Alhinayett din basu da komai a gari har kike tada hankalinki kar a je budurwar Oga ce?
Walyn ta yatsina fuska kafin take bushewa da daria ta ce” ba zaki gane ba, na rasa wani irin abu ne tsakaninsu, aman yau mu shiga mu keta mata rashin mutunci yar gidan taki zama!
Tafawa suka yi suka nufi yar kofar gidan da niyar shiga su shikawa Alhinayett rashin mutunci da ikirarin ta rasa wardugu sai dai yaransa (han)????
Wayo azumi na matsowa, ni kam kamar nace da ku da sai mun hade in da ranmu bayan azumi????
???????????????? *BAK’A CE* ????????????????
https://www.facebook.com/Idan-rana-ta-fito-writers-association-114558343535568/?referrer=whatsapp
*☀IDAN RANA TA FITO WRITER’S ASSO????* ____________________________________________
*Fad’akar da al’umma tare da nishad’antar da masoya shine fatanmu*????????????????
Na
*SAJIDA*
6️⃣4️⃣
Zaune yake cikin talakawansa ana shari.a kan wani datijo da ya karbi kudin auren yarinyar wajensa sai da aure ya zo yace ai sai an linka kudin idan ba haka ba ba zai bayar ba,
Wannan rigimar suke ciki tunda safe inda ya umarci a je a kawo masa shedun da aka karbi kudin auren a gabansu ,
Daga inda yake zaune yana iya jiyo kukan Sultan, yaron wajen Gaishata , yaron akoy rigima, baya baci kuka ne da shi sosai wanda duda da yarinya mai tayata raino aman baiwar Allah sai ramewa take dan bata son tsotsa da kuma rigimar,
Gaban goshinsa ya dan dafe yana mai jin tausayinta a ransa, shi kam Allah ya jarabe shi da son yarinyar nan a ransa, hakan ya sa komai nata ke shigarsa ba tare da ya shirya ba.
Hangen Asadeek da rakumansa suke tun daga nesa abinka da waje a bude hayam ba a kasan rumfa suke ba, har ya matso kusa da su inda suka ga ai mutun ne saman rakumin,