NOVELSUncategorized

BARIKI NA FITO (BOOK 2) 20

BOOK 2
                      PAGE 20
Rannan saboda tsoro a toilet na kwana, koda asuba yayi da lambo na bud’e kofar toilet din naga bata nan, naje nasa ma kofata key,…  Tun daka ranan ban cika fitowa ba, wata rana naje kitchen Zan d’iba abinci sai gata ta shigo nan gabana ya fara fad’i amma sai naji Abu daban, inda ta

Fara bani hakuri Wai Wlh shaidan ne ba halinta bane, ita bata haka kaza da kaza tsautsayi ne wlh kunyan had’a ido takeyi dani, dan Allah in rufa Mata asiri Kar in fad’ama kowa…….  Ganin harda kuka sai taban tausayi tare da fad’in Ummi ki nemi gafaran Allah akan ya k’ara kareki daka fad’awa halaka, sannan babu wanda zan fad’ama wa, tunda har kin gane kinyi kuskure…..  Nan tai tamin godiya…….

Tun daka ranan na daina shige mata, dama ba wani shige mata din nakeyi ba, sai dai ita ce ke k’okarin jana a jiki……
Wata rana naje kitchen d’iban abinci, harna d’iba na fito naga Ummi a falo ita da wata kawarta na gaida kawar wacce ta kuramin ido kaman tsohuwar mayya,, ummi tace zainab Nayi coconut juice yana fridge Nasan kina so…..
Nace eh ummi tare da komawa kitchen na d’auko a cikin fridge, d’akina na shiga na fara cin abinci na, cikin kwanciyan hankali, nasha juice dina tunda ga lokacin ban San inda kaina yake ba, tun wajan karfe biyu na rana, nidai na farka wajan karfe goma na Safiya gabana Nata zugi kaman ansa min Reza an jimin ciwo, kafana duk ciwo suke min kaman anyi dambe dani, jiki na duk tsami, dakyar na tashi nayi toilet dan in samu inyi tsarki da ruwan zafi ko zanji sauki daka zugin da nakeji, bayan na shiga toilet Wanda ban Lura ba kawai naga jini na bimin kafana……  Abun yaban tsoro ya kuma bani mamaki nasan dai bana al’ada sau biyu a wata kuma baifi kwana Goma dana Gama ba, abun ya dauremin Kai, amma tunda nayi wanka tare da gasa wajan, nasa pad, na fito ina tafiya dakyar…..
Abunda Yaban mamaki shine yanda naga pad din bai baci ba, tunawa da nayi ance al’ada yakan Zoma mace tako wani siga, wannan abun ne yasa na basar duk da ban taba yin irinsa ba, ganin jinin baizo ba yasa nayi wanka na fara sallah
Lokacin da dad dina ya dawo daka saudiya baiko nemeni ba, gaba d’aya tunda ya dawo ya canza daka irin kulawan da yake min, da Farko Ina mamaki amma daka baya saina Fara tunanin aiki sunyi mishi yawa, gashi ina son mishi maganan karatu na, domin ni  saudiya nake son zuwa karatu ban son inyi a k’asar nan……  Wata rana naje d’akinshi na sameshi akan maganan karatu na, ya nuna bai yarda inje wata k’asa karatu ba, nai k’okarin in nuna mishi irin burina na son zuwa can fad’a ya bini dashi abunda bai taba min ba a rayuwa, kuka nasa ganin haka Ya fara rarrshi na akan inyi hakuri baya son yayi nisa dani ne, haka yaita rarrashi na, duk da ina Lura da irin canza min din da yayi Sosai…….
Wani Tashin hankali da damuwa daya rufeni shine rashin ganin al’ada dina harna wata biyu, ga nonona suyi ta faman min zugi da rad’adi, gashi sun k’ara girma na k’ara wani haske ……. Gashi gaba d’aya turare na da nake masifar so naji suna min wani irin wari, gaba d’aya na zubar nace hala sunyi expire ne, nasa driver yaje ya siyomin wasu irinsu ,shima dai naji warin yakeyi, abun bada ka nan ya tsaya ba nida bani da wani cin abinci Sosai amma minti Goma na fara jin yunwa gashi ci kaman jaka……   Duk wannan abunda ake ciki Dad dina baya k’asar yana Ghana.
Wata rana na fito ina zazzabi shima dakyar na fito na nufi kitchen dan naji yunwa na neman kasheni, ina zuwa falo Nayi d’akina da gudu Ina amai domin warin turaren wutan da aka sa a falon ji nayi kaman warin jaba……  Ina cikin amai saiga ummi da kawarta sun shigo suna fad’in sannu maike damunki bari in kira Dr, ban damu ba dama ina da bukatar ince a kira family Dr dinmu ta dubani domin dad baya Bari maza na dubamu……  Dr tazo tana tamin tambayoyi ina bata amsa Kai tsaye tace bari ta d’iba jini na, na mi’ka mata hannu na ta d’iba, tace zata koma tayi gwaji inta gwada ta gani zata Aiko da magani…..
Bayan Dr ta fita na koma na kwanta ina jiran a kawo min magani, ina cikin bacci naji an bugo min kofa da karfi, tashi nayi inga ko Waye dad na gani da Falmata, Dad dina kallon tsana yake min ina mamakin ya akayi ya dawo yau,
Katse min tunani yayi da fad’in uban wa ya miki ciki ??
Cikin razana da fargaba nace Dad mai….. 
Tas tas ya saukemin Mari har biyu tare da fad’in kin cuceni Zainab, nida nake ma jama’a wa’azi , yau gidana shine y’ata ta ciki na tayi cikin shege….  Allah ya isa tsakani na dake Zainab kin cuceni, duk irin tarbiyan dana baki, jiya sanda ummi d’inki ta kirani tace in dawo gida babu lafiya, Banyi zaton wannan mummunan labarin zan Tarar ba…..
Cikin kuka na fara fad’in Wlh dad ba ciki gareni ba, kuma Wlh muje asibiti a duba, Niko saurayi ma ban dashi W…….
Tas Falmata itama ta sakar min wani gigitaccen Mari tare da fad’in shairi likita zata miki, mutuniyar banza, wlh kin cucemu kaf zuri’ar mu babu wacce ta taba Abun kunya sai ke
Cikin kuka nace ummi Kema shaida ce banda K……
Tayi sauri ta katseni tare da fad’in Yimin shuru munafuka
Dad dina shidai shuru yayi inda Falmata take ta kalaman batanci akai na tare da fad’in na d’auko musu Abun kunya yanzu taya zasu kalla mutane da wannan abun nawa….. Falmata ta kalli dad dina babu ko tsoro tace naji kayi shuru kaman kana jin tsoran yi mata magana gwara ka yanke hukunci tun Kafin mu kasa fita
Dad dina yace in fad’i uban da yayi min ciki.
Ina tamai rantsuwa akan ba ciki gareni ba, dan dai nidai nasan ban taba kwanciya da kowa ba nida ko maza ban kulawa taya zan samu ciki, sai dai in a ruwa nasha…. Da sauri nace Dad Wlh hala a ruwa nasha d…… Falmata ta saki shewa tare da fad’in a ubanki gashi nan da yake gabanki kika sha…… Ko tsoran dad batai ba ta dinga zaginshi Wai shine ya dauremin gindi ai yana nunamin so ya d’auki dukiya masu yawa Yaban ba dole Inbi maza ba…..  Kuka nake Sosai tare da takaici na tabbata Falmata Nada wani mummunan Abu a kaina tun sanda Dad dina yace tun jiya ta kirashi akan ya dawo, toh ni kuma yau Dr tazo ta dubani kenan tasan wani abu ko ince ita ta kullamin shairi….. Tsawan da Dad dina yamin yasa na dawo cikin hankalina da hayyacina yace na baki nan da zuwa gobe ki fad’amin wanda yayi miki Inba haka ba za kiga fishina y’ar iska fuuuuuu ya fita……  Wannan itace mummunan Kalman dana taba ji Dad ya fad’a tunda nazo duniya kuma ba’a kan kowa ya fad’a ba sai a kaina, Kalman tayi min ciwo, nidai nasan namiji ko hannuna bai taba ri’kewa ba balle ince toh taya na samu ciki kwata kwata na kasa ganewa…..  Ina dai nan zaune inda nake ina kuka saiga Falmata ta shigo tazo gab dani Tana fad’in Zainab kiban had’in Kai Indai kina son Dad d’inki ya yafe miki…..
Wani irin kallo na Mata tare da fad’in da in aikata abunda kike bukata gara dad ya yankani d’anya ya soya Naman jiki na, akan in aikata wannan mummunan aikin wanda Manzon Allah ya tsine ma masuyi…..
Tace haba zainab sau d’aya kawai za muyi in mukayi sai mu tuba….
Zainab tace tir lallai tabewa da Asara sun tabbata a kanki, lallai irinku ne wanda ake cewa kuna fita daka addini baku Sani ba……
D’aura hannunta tayi akan nonona da sauri na wanka mata Mari Wanda dai dai lokacin dad dina ya dawo d’akin ganin na mareta yasa ya fara salati tare da fad’in munanan kalamai a kaina wanda zan iya rantsuwa sune suka bini harya kaini inda nake yanzu domin bakin iyaye dafi ne, sai yasa koda wasa karka taba aibanta d’anka domin addu’an iyaye kaman takobi take da kaifi….. Dad yaci gaba da fad’in daka yau bani bake bazan zauna da wannan abun kunyar ba, wlh saboda ke bazan fasa fita cikin al’umma ba , sannan harda marin ummi d’inki lallai wata rana Nima zaki mareni,
Kuka nake Sosai domin jin maganan dad nake Wlh kaman bashi yake  fad’ansu ba, mutum Mai tawakkali, da ilimi yau shine yake nuna da yaji kunyar duniya gwara ya rabu dani har abada, duk irin sonda yake min ban taba tunanin zai min haka ba, yau koda cikin gareni dagaske ina tunanin dad dina zai d’auka a matsayin kaddara amma gashi anyi min shairi ya yarda
Gashi matarshi sai zugashi takeyi shi kuma yana k’ara hawa yana aibanta ni……
Ranan cikin dare mahaifina yace in bar mishi gidanshi tunda naki fad’an uban da yayi min ciki, ina kuka inata rantsuwa akan banda ciki, inma ciki ne Toh a ruwa nasha, har al’qur’ani na d’auko na dafa akan ban taba saduwa dako wani namiji ba amma dad dina baiko saurareni ba, cikin kuka nace Dad na tabbata abunda kake min yanzu kana yinshi ne cikin rashin bincike, dad kafi kowa sanin wacece ni, kafi kowa sanin abunda zan aikata yau Dad koda ciki gareni ina tunanin zaka d’auka a matsayin kaddara….
Cikin murya irin ta fushi yace fita kibar min gida y’ar iska karuwa……
Lallai wannan Kalman ta dad’e tana Yimin ciwo Sosai har yau inna tuna ina kuka
Mahaifina ya’ki amsan kaddarata saboda Kar yaji kunyar duniya ace y’ar babban malami tayi cikin shege, duk da a lokacin ban San inada ciki ba dagaske…..
Tafiya nake cikin dare komai ban samu na d’auka ba, daka ni sai kayan jiki na,  wata babban mota na gani ta lodo wasu kwalaye na samu na shige duk da ban San inda za suba kawai Ina burin inbar garin abuja dan nasan motar wani gari zata, ban dad’e da shiga ba motar ta tashi kaman ni suke jira……  Aiko mukai ta tafiya……  Munyi tafiya Sosai Kafin motar ta tsaya inda na samu na fito na ganni a wani waje kaman kasuwa duk da darene ga mata birjit, cikina naji ya fara ciwo Sosai tare dajin wani abu kaman hanjin cikina zai fita, da sauri nayi wani wajan benci na zauna inata juyi ji nayi wani abu kaman ruwa na fita daka jiki na, ina dubawa naga jini Sosai ga wani irin ciwon ciki inaji Sosai, muryan wani naji a kaina yana fad’in na shiga uku an fasa aurena Mai zan gani haka y’ar uwa??
Ganin na kasa magana alaman ina jin jiki yasa ya kamani yana fad’in oh ni hjy babba sai ku tashi ku kwaso ciki kuzo kusha maganin zubar da ciki kuyi ta juyi, sai a nan na tabbatar da ciki gareni kuma Bari Nayi domin anyi mana bayanin jinin al’ada a islamiyya kuma yanda wannan jinin yake zuba nasan bana al’ada bane, na shiga rud’ani Sosai tare da tunanin a Ina na sami ciki, naci kuka tare da takaicin wannan abun…..  Wanna d’an daudun Mai suna hjy babba shine ya taimaka min harna warke na dawo normal Ina kwana a d’akinsa saiya koma d’akin abokanan sa y’an daudu……  Wannan shine silan komawa na gidan karuwai har na fad’a wannan mummunan harkan tunda banda wani abu da zanyi sai shi, sannan nakan je kofar gidan mahaifina ko in tura a ajiye Mai hotuna na da shigan banza dan in kuntata mishi sai dai ban sani ba koya gani ko bai gani ba oho, ina karuwanci ne saboda rasa mafita ko madafa iyayena sun koreni banda wani gata…. Komai ya fado min shi zanyi tunda banda mafita duk da ina aikata Abunne kaman dole sai dai banda wata hujja akai, amma na d’aura hujjata akan ina son in kuntata ma Dad dina, duk da wani zuwa da nayi na ajiye hoto naga gidan babu kowa , na tambaya akace sun tashi tun daka wannan ranan da naje naga gidanmu ban k’ara tunanin in koma Gida ba ko in nemi iyayena ba…… Dan Tsagaitawa tayi tana kuka tana rungume jikin Yarima taci gaba da fad’in Wlh Yarima Ina aikata zina amma Wlh harga Allah cikin raina Ina mamakin haka…..  Had’uwa na dakai shine yasa na daina, gaba d’aya, Yarima Nasan had’uwa na dakai had’in Allah ne, na tabbata duk wannan Abun daya faru dani kaddarace Wanda har yanzu ban son wanda yamin ciki ba, Yarima dan Allah kaima karka juyamin baya kaman yanda dad dina yamin dan Allah Yarima…….
Yarima Aliyu dan janyeta yayi a jikinshi ya kura ma fuskanta ido na wani lokaci sannan ya fara murmushi tare da fad’in wow wow nice story I wish dat am a director in had’a film da wannan labarin naki Nasan zan samu kud’i, zainab I will never ever trust you again,  komai zai fito daka bakinki karya ne, do you think dat I will believe you with dis ur fake story…….  Har kina danganta kanki da babban malami kina fad’in shine dad d’inki??  Wani irin murmushi yayi tare da fad’in you always lies to me……  Bazan k’ara yarda dake ba in my lyf……
Tace Yarima am telling you the truth……..
Yace truth??  Zainab komai naki karya ne, kina tunanin wannan labarin naki zai sa in yarda dake??  You are wrong,  this is not the same Yarima dat trust you before, today wen I see d truth about you I have change…..
Cikin kuka tace Yarima Wlh gaskiya na fad’a maka harga Allah, Wannan shine gaskiyan labarin rayuwa ta……
Yace koda gaskiya ne……. I won’t accept you as my wife……  Zaki zauna a nan a matsayin baiwa Mai min bauta……  I won’t accept you macen da kowa ya Santa, but before in baki aikin ki dole in miki HIV test in gani May be kina dashi tunda anbi wancan anbi wancan so Kinga in kina dashi sai in San Kalan aikin daya dace in baki……  Zainab I will make sure to hurt you, saina hukunta ki yanda nan gaba bazaki k’ara yaudaran wani ba, you r lucky I make promise to my dad da yau sai kin bar gidan nan but you will live here as my servant,  I hate to see your face, make sure to hide your face from me har sai na nemeki cheater, Yana fad’in haka ya ri’ke kirji dake faman mishi zafi ya fita tare da bar mata d’akin…… K’asa tayi tana kuka shikenan Yarima ya tsaneta duk da ta fad’a mishi gaskiyan ko ita wacece kuka ta saki mai ban tausayi……
Daka yanzu duk wacce take neman BARIKI NA FITO, daka farko taje ta duba Wattpad ko facebook page d’ina MARYAM OBAM NOVELS… Dan gskya daka yanzu babu wacce zan kara turamawa na gaji ga typing ga aikin ture ture haba Abun yamin yawa……
MARYAM OBAM

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button