DOCTOR HAJAR COMPLETE HAUSA NOVEL

Hajiya na zaune gaban me kitso ta juyo tace.
“Harka fito Junaidu, Allah ya kiyaye, kayi sauri kasan tun d’azu su Alhaji suka fita, kuma kasan baya son jira, ina ce ,cen d’in zakayi, yanzu”.
Cikin girmamawa Captian yace.
“A’a zan biya gurin Dr Samir”.
“A’a menakon ,ko bari sai kun dawo Junaidu?”.
Girgiza mata kai Captian yayi ,yace.
“A’a hajiya kibarni kawai naje, k’arfe biyu za’a masa dashen k’oda ,kuma gsky bazan iya tafiya ban yi masa, salama ba ,nidai addu’ar ki nake buk’ata”.
“Tow D’an lelena, Ubangiji ya tsare min kai yasa kuje a sa’a ku dawo a sa’a yayi maka ‘Albarka, sai ka dawo kuma ‘akula da tuk’i banda tuk’in gan,nanci”.
Mik’ewa yayi, yace.
“Ameen Hajiya nagode kuma insha ‘Allah ahankali zan tafi”.
*
Captian yaje ya samu su Khadee sai had’a kayan aiki suke, kafun lokaci yayi, gurin ta yaje ya nemi Alfarman yana son yaga Dr Samir dak’er ta ‘amince masa don, dokar asibiti ce babu me shiga wanan d’akin sai ,iya likitoci.
*
Kwance ya sameshi ‘idanun shi biyu , yana kallon sama.
Kallo d’aya Captian yayi masa ya kauda kai, don baze iya kuma kallon shiba.
Duk ya rame yayi bak’i ya fita hayacin sa, kamar wani me ciwan H.I.V haka ya koma.
Jin k’amshin turaren Captian ya sashi kallon k’ofa , tsaye ,ya ganshi yana hawaye.
Cikin k’arfin Hali a hankali yace.
“Junaid lfy kake, kuka yau ranar farin cikin ,ka?”.
Maganar tashi ma dak’er take fita.
Saida Captian ya matsa kusa da, Dr samir ya tsuguna jikin gadon shi yace.
“Samir bana jin farin ciki, kamar yanda zakayi tsamanin zanji, naci Burin wannan auren kamar ba gobe.
Amman rashin ka gurin d’aurin auren yasa naji komai baya min yanda ,nakeso .
Tun jiya nake jin fad’uwar gaba Samir bana son katafi ka barni, inaji ajikina kamar akwai abunda ze faru Samir, inajin ajiki ,kamar akwai wani babban abuda ze faru da kai ko dani.
Da ina da hali Da nace bazanje gun d’aurin auren ba, kodon naga lokacin da za’a shiga dakai da kuma lokacin da za’a fito dakai, Amman hakan baze yuwu ba”.
Samir ayanzu kwata kwata baya iya Kuka baya iya hawaye saidai, ya d’inga jin zugi cikin zuciyar shi.
Wani abu yaji ya tsaya masa’a mak’oshin sa, lokaci guda yaji komai ya tsaya masa cak.
Dafa Captian yayi ,yace.
“Ka, kwantar da hankalin ka ‘Abokina ka d’auka cewa komai dake faruwa muk’adaddari ne, da kuma wanda ze faru.
Ina so kayi ‘imani da Allah kuma ya, yarda, da k’adaddara, ka d’auka cewa komai ba komai bane face jarabawa, idan Allah yayi zan fito dole ka dawo ka gani, idan Allah yayi zan tafi dole ka dawo ka samu babu ni.
Ko ,kana kusa dani ko baka, kusa dani dole indan lokacinane dole natafi.
Kuma ina so ka sani cewa cuta bata kisa, sai ‘idan kwana ya k’are, zakaga me lfy ya tafi yabar mara lfy kaga wanan yana, nuni da cewa bafa sai baka da lfy zaka tafi ba.
Da wanan ,nake rok’on ka da katashi, ka tafi gurin d’aurin Auren ka, kad lokaci ya k’ure, Allah ya baku zaman lfy”.
Jiki a sukwane Captian ya tashi ya fice batare da yace wa Samir komai ba.
A k’ofar d’akin ya iske Salma fuskar ta ya kunbura tsabar kuka, so take ta ,tsayar dashi tayi masa ,magana ‘Amman ta kasa tsaida shi ,harya b’ace ma.
Zama tayi ta cigaba da rera kuka, abunda ta gani yau ,ya balain d’aga mata hankali, ji tayi dama tun cen tasan da hakan da, duk Dr Samir be shiga halin dayake ciki ya’yanzun ba.
“Ya ‘Allah “.
Shine abunda ta iya furtawa, yayin data lalubo wayan ta don kiran Captian, ta sanar dashi komai tun kan lokaci ya kure musu…….
By Dija_Waziri
[18/12 7:33 pm] Dija Waziri: ????????????????????
DR HAJAR????????
????????????????
Second to the last
shafinan gabi d’ayan shi sadaukar wa ce gareki Miss XoXo ,Allah ya barmu tare ????
Mata mu tashi tsaye mu kula da tarbiyyar yaran mu. Aure yana shiga cikin wani hali, zarge-zarge na yawaita a daina don yafi yawa wajen mata nasiha wurin miji yafi zargi da habaici, makaranatar farko a wajen mata uwa ce.
Nashiha yana da matuk’ar muhimmanci iyaye su ,sani cewa nasiha babbar hanya ce na tarbiyyar yara.
me ake nufi da Tarbiyya a musulunci? Tarbiyya tana ,nufin gina cikakken mutum sannu a hankali ,don bin umarnin Allah da na manzonsa ,da neman yardar Allah, da samar masa da nagarciyar rayuwa duniya da hahira bisa tsari irin ,na musulunci.
hukuncin gina yaro Akan tarbiyyar Musulunci wajibi ne. Kuma hakki ne daga cikin hakkokin yaro akan mahaifansa, ko walliyansa ,dalilai akan haka.
daga kuri’ani fad’in Allah ta’ala yace.
Yaku wad’anda kuka yi imani .ku d’auki matakin kare, kanku da iyalinku daga wuta masu tsaronta, wasu irin mala’iku masu karfin bala’i da tsananin gaske ,basa sabawa Allah abin daya umarce su, kuma duk abin da ya Umarce su shi suke aikatawa.
Daga hadisi fadin Annabi yace
Kowa ya saurara yaji dukkaninku masu kiwo ne, kuma kowanneku sai an tambaye shi kiwon da ‘aka ba… Namiji makiyayi ne game da mutanen gidansa ,kuma sai an tambaye shi akan abin da ‘aka ba shi kiwi, mace ma makiyayi yace a gidan mijinta da ya’yansa ,kuma sai an tambayeta akansu….
Allah ya bamu ikon tarbiyyan tar da yayan mu bisa tafarkin tsira Ameen????
Chapter 49
KAFUN D’AURIN AURE
bayan Captian yabar asibiti , hanyar Zariya ,ya d’auka , gudu yake sosai kamar ze tashi sama don Lokaci ya kusa cika ,kuma yana son ya samu salar jumu’a, awan shi d’aya ya sadashi da garin zariya.
Ko daya isa ya samu an fara sahun sallah cikin Sauri ya d’aura ‘Alola shima yahau sahu.
Raka’a biyu sukayi, suna idar wa yaji wayan shi ya fara, ruri yana dubawa yaga Salma ce , beyi tunanin komai ba ya d’auka.
Bakin ta na rawa tace.
“Hello Captian, an d’aura, auren ,ne?”.
“A’a Salma ba’a d’aura ba yanzu ne dai ake shirin d’aura wa lfy kuwa?”.
Saida ta saki wani gauran, nufashi sanan tace.
“Akwai matsala Junaid “.
Cikin rashin Fahimta Captian yace.
“SubhanAllah wace irin matsala ce kuma Haka Salma?”.
D’an jim tayi kad’an sanan ta goge hawayen dake zuba cikin idanun ta, da kamar bazata fad’a masa ba , taga koda ta bari duk randa yazo yaji bazataji dadi ba, cikin rawar murya tace.
“D’azu da naje gida, d’auko wa Samir kaya , naga scret book d’inshi, ban so d’auka ba, alokacin.
Amman zuciya tayi ta ,tunzurani saida na d’auka, bayan ,nazo asibiti ne kuma sai na d’auko na fara karan tawa Captian abunda nagani yayi masifar d’aga min hankali.
Ban tab’a sanin Samir nada zurfin ciki ba sai ayau”.
Shiru tayi tana, goge hawayen da suka ,kuma wanke mata fuska.
“Ina jinki Salma kiyi sauri , ina son zan kashe wayata”.
Captian ya fad’a cikin tashin hankali dason, yasan meke faruwa.
“Captian kayi hakuri bazan iya barin abun cikin zuciyata bane shiyasa zan amayar dashi.
Dr Samir ya jima yana son Hajar tun kafun kasan zaku had’u da ita , yau wajen shekaru 8 ake nema yana dakon son ta.
Kuma bawai ya dena son ,nata bene har yanzu, dalilin dayasa ya hak’ura ,kuma yak’i furta mata shine, don yaga kariga shi furta mata shine babban dalilin dayasa, ya fasa ,yabar abun azuciyar shi.
Kuma , musababin yawan tashin ciwan zuciyar shi akai akai harda , rashin samun ta dabeyi ba, abun yana damun shi. Kuma yayi alk’awarin babu wanda ze fad’a ma koda hakan ze iya barazana da rayuwan shi”.
Captian jinshi yayi wani ‘iri kamar bashi ba, taka, k’afarshi ma kasayi ,yayi be jira ‘Salma ta k’arasa masa lbrn ba kawai ya kashe wayan ya cilata cikin mota , yanajin ranshi na balain b’aci zuciyar shi na suya.