FITAR RANANOVELS

FITAR RANA 19

FITAR RANA 19.

HBDSUSU

Ajiyar zuciya ya sauƙe sann ya turo kofar Dakinsan hankli snn ya shigo ciki,tun Daga bakin ƙofa ya tsaya Yanamai kallonta, jikinta data dukunkuneshi waje guda rawa yakeyi sosai tana fidda sautin kukanta a hankli tana maida ajiyan zuciya mai zafi.

Wani haɗe ranshi yay tamkar mala’ikar daukar rai,ransa na dada turmusa sabida a duk sanda ya kalleta sai hotonan saheeb ya bayyana masa a mind dinsa a yadda suka kasance dashi dazu.

Wani fuuu kishi ya debesa ya karaso gefen gadon,wani tukukin tsaki yaja snn ya yaja bargon data dunkule ajikinta dashi ya watsar kasa.

“Ke dalla ki rufamin baki
And Get down from my bed stupid.

A rikirkice ta sauƙo kasa jin tsawar daya daka mata,caraf sai idanuwan sa suka lura da inda tayi fitsari duk gadonshi ya jika shataf

Kallon wajen yakeyi da mamaki kamar wanda bai fahimci abunda yake gani ba,snn ya juya ya kalleta lokcin harta sunkuyar da kanta can kasa tanajan ajiyar zuciya cikin matsanancin tsoro,yanata kallonta yaga jikinta itama duk ajike yake,da mamaki sosai ayanayinsa ya matso inda ta tsaya a rakube tana karkarwa.yace ke meye wannan ajikinki?kirjinta ne ya tsananta bugu ta kasa iya budan baki tay magana danji takeyi kamar ta saki fitsari ajikinta dan tsoro

Wani fizgota yay ya matseta da hannun shi acikin yanayanin rudani tana shirin rusa ihu yace Am talking to u,nace meye wannan ajikinki?…
Sabuwar kuka ta rushe dashi cikin daburcewa da i i na tace kayi hakkuri..
Dan Allah kayi hakuri karka bugeni,ai zan fada maka..Saketa yay a hankli ya harde hannun sa a kirji ya tsaya Yana kallonta alaman yana sauraranta

Kuka takeyi sosai jikinta yana rawa rawa bakaramin tsoro takeji ba…

Tausayi take bashi har cikin ranshi saidai yanayin sa bai nuna hakan ba ,cikin tuno da abunda mahaifiyar sa ta fada masa akan cewa yanabinta a hankli yarinyace yay lumui da fuska ya sauke sihirtaccen ajiyar zuciya, cikin sassauto da muryan sa kasa kasa
Ya hade ransa Yace “Fitsari kikayi min akan gado na ko?…”tsoro ne yasata gyada mishi kai.
Gwalo idanunshi waje yay”Are u mad?wa uban wa kike gyada ma kai “answer me,nace fitsari kikamin akan gadona?

Cikin hanzari bakinta na rawa tace, eh fitsari nay,amma dan Allah karka bugeni,
Wani matsanancin kuka ne ya kufce mata data furta hakan fincikota yay a bazata yace “kimin shiru konayi miki shegen duka marar kunya kawai kiyimin shiru nace miki…

Bakinta ta rike a daburce batare datasani ba,acikin rudani ta matse gunjin kukan ta tanamai kallon cikin kwayar idanun shi daya zaro mata kirjinta kamr zai fashe ya ballo waje tsabar firgita da tsoro,wani kakkanme jikinta tayi kafufuwanta datakejin kamar bazasu iya motsi ba sai rawa rawa sukeyi dakansu

Saketa yay ta tsaya a tsomare tana karkawa ta rufe bakinta da hannu tana toshe kukanta da karfi.

Yaye zanin gadon yay ya watso su agabanta sann ya dudduba bargon ganin fitsarin bai tabashi ba ya nannade shi ya ajiyeshi acan gefe.
Kallo daya ya mata ya dauke kansa fuskan sa a murtuke yace Dauko zanin gadon saiki cire harda kayan jikin ki kibiyo ni.Cikin sauri ta sake bakinta ta tsuguna a hankli ta tattaro zanin gadon tabi ta cire kayan jikinta ta daura dan kwalin dabai jike ba, ta rikesu a hannu tana sauke ruwan hawaye masu sanyi, Gaba yay snn ta hau binshi a baya baya ya bude musu kofa suka sauko kasa gabaki daya bata cikin hayyacinta.

Bilti tana kan shirya musu abun kari akan madaidaicin dinning table dinsu can taji motsi ta daga kai sai ta hangosu sun doshi hanyar waje..

Barin duk abunda takeyi tayi tabi bayansu backyard suka nufa inda suke wanki da pumping ruwa a tanki.

Suna isa wajen wasime taja ta tsaya tana kallonshi,babban baho ya saukar ya dauraye ya saka abakin tap ya kunna ruwa yana zuba aciki,agefe ya lalobo omon so klin mai qamshi ya zuba acikin ruwan,yana kaiwa half ya kada snn ya kashe tap din yanemi waje ya zauna ya jawo bahon agabansa..

Wani matsiyacin harara ya bita dashi..batare da yace mata uffan ba tasha jinin jikinta ta kawo mishi kayan da bedsheet din hawayen tsoro ya gama wanke mata fuska

jikinta duk na rawa rawa a mugun tsorace ta mika masa,wani difff diff ruwan hawayen nata ya diga masa a hannun wani fauce kayan yy da karfi snda ta razana taja da baya …cikin zaro mata ido da comanding voice dinshi dake nuna isa da mulki yace “ki goge wannan abun kafin na wanka miki mari a fuskanki”..nace ki goge hawayenki kimin shiru ko?.. cikin sauri ta goge hawayen tas ta tsaya a tsaye kamar soja babu abunda takeyi sai jajjan zuciya,jikinta na rawa kamar mazari…

Tsayawa a bayansu Bilti tay tanamai lura da su.
Ta tuna yace mata karta kara shiga harkansa.
Kuma tafi kowa sanin halayarr taheer sarai,Sumtimes he can make her feel like she is nothing musamman in ransa yay matukar baci da ita..but still she can deny d fact dat koma meye zai faru baxata taba iya kyalesa ba yana abunda yaga dama ba domun kuwa kamar dan data haifa haka take jinson shi acikin zuciyarta.

Tausayin wasime ne ya kashe mata jikinta sosai tarasa ta ina zata fara tsoma musu baki.

Tsoma kayan yay acikin ruwan kumfa ya jika snn ya daga ido yana kallonta,sam bata iya hade idanunta dashi, atake ta nitsu tayi narai narai kamar wata yar baiwa ta sunkuyar da kanta can kasa tana sauke ajiyar zuciya..da gefen idanunshi ya harareta “Tun yaushe kike fitsarin kwance ko dan tsabar iskanci akan gado na kawai kikaga daman yi yau”…shiru tayi..ina miki magana kina min shiru ina wasa dake ne..?

Idanunta cike da hawaye masu ban tausayi ta dago zata gyada masa kai caraf suka hada ido saita tuna yace bayason hakan dakyar ta tattaro nitsuwarta muryanta na rawa sosai tace “..wallahi, tallahi na rantse…”shut ur mouth! Ya daka mata tsawa ya mike tsaye cikin masifa

Wannan rantsuwa duk na nemene ne?waya koya miki rantsuwa..just answer d damn question,nace tunda kikazo gidan nan kike fitsarin kwance koyaune kawai kikayi sabida kin rainani?

A rikirkice tana fidda sabbin hawaye tace a’a.
A’a Dama…dama…kuka ne yakeson kufce mata tay saurin toshe bakinta

Tsaye ya dada mikewa yana kallonta tayi saurin ja da baya a tsorace,tana cewa,zan fada zan fada
Kayi hkri wallhi zan fada

Banace kidena min rantsuwa ba.ke Na sakejin wallahi abakinki saina wanka miki mari.

Hawaye ta dinga saukewa duk jikinta yana rawa,motsi tajiyo ata bayanta ta juya tana hade ido da bilti ta ruga a guje taje ta rungumeta tare da sakin wani tsorataccen kuka

Jikin bilti yy sanyi idanunta sun cikka da ruwan tausayin wasime
Shafo kanta takeyi sosai tana rarrashinta kiyi shiru mama na…kiyi shiru abunki…cikin kuka gwanin tausayi tace bilti dan Allah ki cece ni. Nifa ba da sanni na nayi masa fitsari ba kema ai kinsani bana sonyi,yo ba shine yake zuwa dakashi ba,nifa bana so,banayi a garinmu ..ai nayi nayi na dena anan dinma amma yaki…wayyo Allah na na higga uku…bilti ki cece nim

Matsowa kusa dasu yay yace…”Are u done?
Dada kankame bilti yay
Babu kunya ayanayin sa yasaka hannu ya fincikota daga cikin bilti wani gigitaccen ihu ta sakar masa ya tattareta

Atake ta rude tana ihu tana neman fita hayyacinta.

“wayyo Allah na bilti ki cece ni,wayyo na higga uku,anono na anono na,
Ɗahiru dan Allah kayi hakuri karka kasheni,ɗahiru kayahakuri Wallahi bazan kara ba.

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button