NOVELSUncategorized
RAINA KAMA (BOOK 2) 26&27

_Writer’s namu ina mik’o gaisuwa da babbar murya_.????????
*_(takwara) Bily s Fari, (mamana) Maryam IG, (mamana) Ummu hanan, Hauwa’u A Usman (jidda????) Rufaida Umor, Qurratul ayn, Ai’sha Alto, Leemat, gwoggo????
Asykhaleel, miss Xakss, Jameela Janaf, (takwara) Ummie Garkuwa, Khadeeja Candy, Billy Sarki, Sister Naja’atu, Reefat yahya, Sad-Naf, Maryam wasagu, Maman Shaheed, classic Feedo, Mzzdady._*
???????? _Yawane da kufa. Alkairin ALLAH ya kai gareku aduk inda kuke, bilyn Abdull na nayinku wujiga-wujiga????????????????????_
___________________
~Book 2~ ????????2⃣6⃣
……………….MC yafara shelanta cewa wannan bikin sunafa an had’ashi da bikin birthdays ne, domin ranar haihuwar yaran tai dai-dai da ranar haihuwar iyayensu, dan haka suka had’e wannan biki a yau guri d’aya, dan a waccan ranar murnar haihuwar bata basu damar yanka cake ba????.
Dariya aka sanya, saboda a yanayin barkwanci mc yayi maganar, Galadima kam ai kod’an murmushin ma baiyiba, garama Yaa marwan ya murmusa.
Galadima ya kalli munaya, cikin maganar nan tasa mai kamada an masa tilas yace, “Kina da sa’a”.
“Sa’a kuma?”. ‘Munaya ta fad’a cikin yanayin mamaki’.
Harya bud’e baki zaiyi magana sai kuma ya basar. ganin haka itama Munaya saita sharesa, dan takula yau y’an mulkin ne a kansa.
Saida ya gama shan k’amshinsa sannan yace, “wannan ne karon farko da Sameer yata6a bikin birthday”.
Baki munaya ta d’an ta6e, tana fad’in “Humm, kodai y’ay’anka suna da sa’a?, domin dai a dalilin haihuwarsu ne kayi”.
“ko kina jealous ne?”. ‘yay maganar cikeda basarwa’.
tura baki tai gaba.
Idonsa akan yaransa yace “idan kika bari na kama wannan bakin a wajennan humm.” ya cije lips d’insa.
Sanin k’aramin aikinsane ya akaita abinda ya fad’a d’in ya sata saurin gyara bakinta , tad’an saci kallonsa, ya wani Fiske tamkar ba shine yay maganar ba ma. ita dai tana mamakin kasaita da izza irinna bawan ALLAH n nan, jinin mulki yana da matuk’ar k’arfi a jikinsa. tunaninta ya katse lokacin da hankalinta ya koma kan abinda ke faruwa a hall d’in
Khaleel da Aiyaan, Aryaan ne suka turo cake mai k’yau da tsari, Wanda yasha kwalliyar White and Golden, an saka sunan Galadima da shekarunsa 31years a sama, a jikinsa kuma daga can k’asa ansa Muhammad Sameer (Dadyn Triples), an d’ora candlestick????guda uku, Sai hotonsa da yay k’yau sosai cikin shigar sarauta.
Galadima ya kalli Sauban da Samha, yasan dai wannan aikinsu ne, k’in kallonsa sukayi sukam ballema suyi gamo da tsarabar harara????.
Ita Munaya ma sai yanzu taga Su Aiyaan, batayi zaton anzo da suba, tunda bataga yaran gidansu k’anana ba a waje, sai manya maza da matan Na ma’auri.
MC ya taso k’eyar su Khaleel har inda su Galadima suke zaune, kowanne aka d’ora masa yaro d’aya, suma mik’ewa sukayi bisa umarnin MC d’in, a tare suke takawa ita da shi, sai k’yastu ake zuba musu, masuyi a waya da masu cameras, sai gidajen TVs d’in da aka gayyata suna nuna live. Sun Isa gaban cake d’in hannunsa rik’e da sandarsa, kaikace sarkine da kansa (gaskiyar Munaya Galadima akwai k’asaita, Kodai sarkin da Kansa ya shafa masa lafiya????).
Bayan anmasa wak’ar happy birthday yayma munaya nuni waita hura candles d’in.
Cikin k’asa da murya tace, “yalla6ai bafa haka akeyiba, ka hura abinka da kanka”.
Hannunta ya kama ya matsa yanda zataji zafi, yace, “zakiyi?”.
Ai baima kai k’arshen maganarba ta risina ta hure wutar, hall d’in ya d’auki tafi. cake d’inma dan rigima wai saidai su yanka tare.
“haba yalla6ai, saikace Na wani aure?”.
Cikin ta6e Baku yace, “wama ya sani kona auren ne”.
Shiru tayi bata tanka ba, dan itadai fatanta a rabu lafiya, hannunta ta d’ora kan nasa dake rik’e da wuk’ar suka yanka taren. nanma dai tafin akayi. Ya lakata a d’an yatsa ya duk’o gasu Aiyaan ya daddan gwalama yaransa a hanci da kumatu, sannan ya juyo ga Munaya da haushi ya kamata, ai ita yakamata ma yafara sawa ba yaranba.
Itama akan hanci ya shafa mata yana fad’in “yalla6iya haushi kikajine?”.
Kafin tabashi amsa yakuma lakata ya shafama Aryaan Khaleel da Aiyaan suma.
Dole munaya ta had’iye maganarta. Amma ta kudiri saita rama.
Itama itada Munubiya k’aton cake nasu aka kawo kalar pink and White , Munu da Yaa marwan suka taso a tare.
Munaya da Munubiya suka rungume juna suna maijin dad’in tunawa da ranar haihuwar su, shekaru 20 cif da kwana 7. Sun yanka cake atare suka sakama juna abaki kad’an-kad’an, sannan kowacce cikin son tsokana ta lakatama y’ar uwarta a fuska suka rungume juna suna dariya da k’ananun hawaye, suncika shekaru 20 ranarda yaransu sukazo duniya suma.
Abin ya birge mutane, Munubiya ta matsa ga mijinta ta saka masa a baki kad’an, cikin murmushi yace, “happy birthday my heartbeat ”.
Tace, “Thanks you my luv” k’arasawa tayi ta sakama yaran munaya dasu Aryaan a kumatu, sannan ta sakama nata yaran.
Munaya danta rama abinda Galadima yamata, takai cake bakinsa kamar zata bashi, saida ya bud’e baki saita juya ta shafama yaran Munubiya a kumatu, sannan nata.
Yanda Galadima yay shock akan abinda Munaya tamasa sai mutane suka sanya dariya suna tafa mata, mai martaba da papi ma dai saida suka Murmusa.
Munaya ta dawo ta dangwalama Galadima akan hanci tana masa gwalo.
Shi kansa baisan k’asaitaccen murmushin ya kufce masaba, ya saka handkerchief ya goge yana dawowa mazauninsu ya zauna.
Daga nan aka fara gudanar da wasa, Comedian’s sukazo sukad’an saka mutane dariya, saikuma mawak’a da suka bada nasu salon.
Tun da Galadima ya fara yawaita kallon agogon hannunsa su Muftahu duk suka sake shiri, dan lokaci yana gab kenan.
Galadima yay k’asa da murya batareda ya kalli Munaya ba, yace “ki shirya, shirinsu na farko d’aukewar wutar hotel d’in nan gaba d’aya, na gaba kuma shine banida tabbas. Yara dai ALLAH yana tare dasu, gakuma su Aryaan suma”..
Cikeda mamaki Munaya ta kallesa, sannan ta kalli yaran dake gabansu a wani d’an gado mai k’yau.
Jikinta har rawa yake tace, “yalla6ai mi su Aryaan zasu iya? Please k…..”.
Hannu ya d’aga mata alamar karfa ta ishesa yace, “wani ilimin aduhuwar daji kawai ake laluboshi, kinsan kuwa dolene a gamu da had’arurruka Aciki”.
batada za6i sainyin shiru, ta kalli su Khaleel daketa wasa da abinci a teble da suke zaune hankalinsu kwance. Hawayene ya cika mata idanu, yama za’ayi wad’an can sakarkarun yaran ace suna masu bama yaranta kariya? Yaushe suka gama sanin ciwon Kansu ma balle na waninsu? gaskiya wannan gangancine kawai, tasa handkerchief ta share hawayen da ke k’ok’arin zubo mata.
Duk abinda take Galadima yana kallonta. duk tausayinta saiya kamashi, ya tuna da wahalar datasha, amma bashida za6in daya wuce hakan, kuma itace tabashi k’arfin gwiwa ai, yasaka aransa ko salwanta yaransa sukayi zaiyi tawakkali insha ALLAH.
Duk Wanda yake cikin shirinsu Galadima ya gama shirinsa, haka suma mak’iya masu buri a shirye suke.
Gaba d’aya saura mintuna 25 atashi, saboda gabatowar sallar magrib, a kuma time d’inne Sarki Abdul-fatah da Sarki jalalludden dadai duk wani babba Wanda sukazo tare suka mik’e domin tafiya, ganin haka Galadima yama Yaa marwan sigina da ido akan ya fita da Ameen and Ameena suma, yabi tawagar su papi, dan baya buk’atar a cuta musu..
Jikin Yaa marwan a sanyaye ya d’auki yaran ya fita cikin dabara, yana kallon y’an uku, shidai dan kawai Galadima ya dagene, amma bai kamata a saka yarannan a matsayin tarko ba.
Munaya ma dai ta danne zuciyarta tayi shiru, tanason bama Galadima kwarin gwiwa.
Su papi na fita y’an rawar k’oroso suka fara wasa, mintuna goma da aka basu ya k’are, sai wani mawak’i ya fara nashi, nanfa y’an mata da samari aka samu nayi, dama ganin su mai martaba ne ya sakasu nok’ewa, ana tsaka da cashewa hall d’in yay d’iff, wuta ta d’auke agaba d’aya hotel d’in, mutane aka fara hayaniya kowa na k’ok’arin damk’e dukiyarsa a hannu da k’ok’arin kunna fitulun waya.
Gaba d’aya jikin Munaya yahau 6ari, ta fashe da kuka tana laluben gadon da yaran suke, ruk’ota Galadima yay yasaka a jikinsa, muryarsa na rawa yace, “please ki nutsu”.
“bazan iyaba yalla6ai, karsu……”.
Yay saurin rufe mata baki, da tattausan tafin hannunsa….. A dai-dai wannan lokacinne kuma wutar hotel d’in tadawo.
Hall d’in ya kuma kaurewa da hayaniya, zaram Munaya da Munubiya suka nufi gadon da yaran suke ciki, wayam babu komai.
Munaya tayi luuu zata fad’i, saurin ruk’ota Munubiya tayi, Galadima yataso daga inda yake shima zuwa garesu. hall d’in yagama rikicewa da tsantsar hayaniyar rashin ganin yaran, sai kallon kallo akeyi. Securitys d’in da aka baza sun rikice da wannan tashin hankali, dan sune mutane na farko da za’a fara tuhuma.
Rufe hotel d’in akayi aka hana kowa shiga balle fita,
Galadima ya shafama Munaya ruwa ta kawo numfashi, fashewa tayi da sabon kuka ta fad’a jikinsa, hannu biyu ya saka ya rungume ta shima yana had’iye kwallar bak’in cikin dake Neman zuboma idonsa.
Tausayinsu ya kama mutane da yawa, innaro harda kukanta, hakama inno, abinda yabani mamaki shine tsantsar damuwar da mama Fulani ta nuna, dan itacema tabama Galadima ruwa ya shafama Munaya ta farfad’o.
Da farko Munaya ta d’auka ko Galadima wasa yake mata yasan inda yaran suke, amma ganin damuwar da yake ciki saita kuma rikicewa, dandanan numfashinta yafara gagarar k’irjinta, ta mik’e a kid’ime, dan taji a jikinta kuka sukeyi, nononta sai tsitstsirawa suke, wani jirine yafara hajijiya da ita da zuciyarta ta k’iyasta mata zafa su iya kashe mata yara, luuuu tayi baya Galadima ya ruk’ota. sume musu ta kumayi.
Hankalin Galadima kuma tashi yayi, dole ya d’auki Munaya aka sakata a mota suka bar hotel d’in.
Sauran mutane kam kowacce mota zata fita sai an binciketa.
Yayinda Securitys d’in suka bazu ko ina na hotel d’in ana bincikawa.
Gida aka wuce da munaya, har suka isa tana jikin Galadima, yanata murza tafin hannunta kozata farfad’o, har d’ora bakinsa yayi akan nata ya jawo iskar numfashinta amma a banza, hakanne yakuma tada hankalinsa.
Kai tsaye d’akinsa ya wuce da ita, ya shimfid’eta a kan gadon ya cire mata alk’yabbar jikinta, Akash suka k’araso da hanzari shima, taimakon gaggawa yafara bata shida doctor jalal, cikin amincin ubangiji saigashi takawo numfashi, bama su bari tadawo dai-dai ba suka mata allurar barci.
Suna fita Galadima ya cire rawani da alk’yabbar jikinsa shima, ya sassauta bottom d’in wuyan rigarsa.
Safa da marwa ya shigayi a tsakar d’akin yana Mirza agogon hannunsa Wanda daka gani kasan ba normal agogo bane,.
Wayarsa datai k’ara yay saurin d’auka, d’agawa yayi yasaka a kunne, “Muftahu ya ake ciki?”.
Cikin hakki Muftahu yace, “komai yana tafiya yanda ya kamata ranka ya dad’e, har yanzu gamu muna bin bayansu, amma munkai inda yakamata ka fara Controlling namu, yanzu mun…….”
Da sauri Galadima ya katseshi ta hanyar fad’in “karka damu ina kallon Ku, saidai kilometer’s d’in dake tsakaninku dasu fa yakai 1½, Saleem da Sauban sunfi kusa dasu, dan haka ku k’ara azama. daga lokacin da suka farga da abinda nasaka jikin Amaturrahman tabbas zasu cireshi, kuma zamu rasasune gaba d’aya”.
“Ok babu damuwa, ranka ya dad’e”.
Yanke wayar sukayi, Galadima ya bud’e wani k’aramin akwati ya fiddo kayan aiki wanda a ready dama yagama had’a komai, bajesu yayi akan gadon kusada Munaya, ya zauna yafara Control cikin matuk’ar kwarewa.
Saleem ya kira aunty Salamah wadda itama take tare dasu Ameer yaran da suka sace Muftahu, d’agawa tayi jikinta na rawa, “Saleem kuna inane?”.
“Aunty Salamah gamunan bayansu kad’an, amma mund’an basu k’afa saboda na kula sunfara fuskantar muna bin su, yanzu dai haka mun ajiye motarmu mun samu mashin”.
“Hakan yayi, insha ALLAH indai ta Anguwar da muke tsammanin zasu shigane kamar yanda kaji Harun d’in yay magana to tabbas mu dai mun iso, saidai suzo su iskemu, ka kira yalla6ai ka sanar masa yakamata ya fito yanzu”.
“no Aunty Salamah, bazai yuwu boss yabaro masarauta ba yanzu, saiya tabbatar mun Isa, saboda dukma inda suka shiga yana bibiyarsu, dan bazai saka yaransa a matsayin tarko ba babu tsaro k…….”
Tai saurin k’atseshi ta hanyar fad’in “yauwa ina zargin kamar gasunan a wata bak’ar mota sun wicemu fa”.
“Alhmdllh, su Ameer Susan yanda zasuyi su bisu bara na kira boss”.
“ok”. Kawai Aunty Salamah ta fad’a ta yanke wayar.
Kiran Galadima Saleem yayi, bugu biyu ya d’auka, “Saleem mike faru yanzu?”.
“Ranka ya dad’e gamu dai biye dasu, amma Aunty Salamah tacemin gasu tagansu”.
“wacece Salamah? ”.
Gaban Saleem ya fad’i, dan ya manta Galadima baisan Salamah ba, “Am sorry sir, idan komai ya dai-daita zan maka bayani”.
“Saleem!!!”. Galadima ya kirayeshi a tsawace.
Saida Saleem ya janye wayar akunnensa, muryarsa na rawa yace “ka yarda dani sir, wlhy itama ta kwarai ce”.
Ajiyar zuciya Galadima yayi, muryarshi cikin tsantsar damuwar yace, “wannan anguwar da kuke tanada hanyoyi da yawa, dan haka Ku fara amfani da live GPS navigation maps naku, yanzu zanyi settings komai yanda zaku ringa ganinsu duk layin da zasu shiga insha ALLAH, waye yake driving d’in a cikinku?”.
“nine sir”.
“ok bama Sauban wayar”.
Saleem ya mik’ama Sauban wayar, Galadima na fad’a masa yanda zaiyi, shikuma yana Controlling maps App d’in dake cikin System d’in cikin kwarewa, (dan shima Galadima bai barsa hakaba, dukda bashida ra’ayin karantar wannan fannin saida ya tsaya tsayin daka ya koyan saboda irin wannan ranar).
Saida Galadima ya tabbatar komai ya dai-daita, sannan ya kira su Nuren ma, suma suka dai-daita komai nasu, cikin sauk’i duk suka koma ganin inda yaran suke, saboda Galadima ya saka Abu jikin Amaturrahman, dukda bawai hotonsu ko video suke kalloba kai tsaye.
Duk da haka Galadima ke fad’a musu su shiga layin haggu, ko dama, kosu canja hanya dadai sauransu.
Duk Wanda yake a wannan masarauta yau hankalinsa a matuk’ar tashe yake, saifa kallon kallo da hasashen juna ake a zuciya, kowa yana zargin Wanda ya raina.
Hankalin Abie a matuk’ar tashe ya nemi ganin Galadima, koda sarkin k’ofa yazo yana knocking Galadima bai amsaba, kuma yana kallonsa ta CCTV.
d’an aike ya koma ya sanar Galadima ya kulle kansa a d’aki yak’i bud’e k’ofa.
Papi inno ya kira, yace maza taje sashen Galadima taga mike faruwa.
Ko kuyangi inno batajira sun mata rakkiyaba, hasalima babu Wanda yaga fitowarta a sashen mama Fulani, dan kowa a rikice yake da wannam bak’on lamari na satar yara.
Galadima daya ga sarkin k’ofa yabar wajen ya mik’e shima daga gaban kayayyakin da yake aikin, shaddar jikinsa ya cire yasaka bak’in wando da t-shirt, ya kawo bak’ar jacket mai k’yalli kamar rigar sanyi ya ajiye gefe, a bakin gadon ya zauna yana d’aura takalminsa yana cigaba damasu Sauban da Nuren bayanin hanya, a dai-dai lokacinne Inno ta iso sashen nasa, da hanzari Sarkin k’ofa ya bud’e mata k’ofar, bata jira wani isoba ko masa sallama ta turo k’ofar falonsa ta shigo, babu kowa a falon, komai ma a kashe yake. Bedroom d’insa ta nufa, nandai saida tayi knocking kam, saidai kafin yay yunk’urin tasowa ya bud’e mata ta turo k’ofar ta shigo, mik’ewa yay yana kallonta da d’aukar jacket d’insa zai saka.
Ajiyar zuciya inno ta sauke, saboda ganinsa normal.
“Ranki ya dad’e da kanki? lafiya dai ko?”.
“Inafa lafiya Muhammad? takawa ya aiko a kiraka ance ka kulle kanka, gashi baka sanar mana halinda yarinyar nan take cikiba”.
Galadima yace, ba kulle kaina nayiba, bansan kuma d’an aiken daga papi yakeba” ya juya yana kallon Munaya da cigaba da fad’in, “itama ta farfad’o, amma sun mata allurar barci”. ‘ya k’are maganar da daidaita zaman kwalar rigar jacket d’insa’.
Ajiyar zuciya inno ta kuma saukewa, tace, “to Alhmdllh. ina kuma zaka naga kana shiri?”.
Wani murmushin takaici yayi zuciyarsa dake gudun daya wuce kima da suya ya dafe, Inno dai ta zuba masa ido, takowa yay inda take ya kama hannunta ya rankwafo (dan yafita tsaho) ya d’ora bisa kansa, cikin murya mai nuna tsananin karsashi da alwashi yace, “kisamin albarka inno, zanje farautane”.
Da sauri ta janye hannunta daga kansa tana matsawa baya, “Muhammad mikake nufine? kana ganin tashin hankalin da muke ciki shine zaka k’irk’iro mana wani kuma? kana tunanin wad’annan mutanen zasu barkane? dama kai suke fako, shiyyasa sukayi tarko da bayin ALLAHn dabasu ji ba basu gani ba, su takawa cikin k’ok’arin d’aukar mataki suke, yanzu haka naga IG da kansa gashican ya iso bisa umarnin kiransu”.
Galadima dake tattara abinda zai amfani dashi yana zubawa a aljihu, yace, “inno Muhammad Sameer d’inku ba ragon namiji bane da zai zauna jiran Police d’in da suka gaza gano wad’anda suka durk’usar masa da mahaifi tsawon shekaru a yanzu kuma nayi tunanin zasu iya dawomin da gudan jinina har uku, ba sune sukamin tarko ba nine namusu tarko, idan tsoron na mutu kuke, Ku cire inno, ko babusu mutuwa tabbataccen abune rubutacce a kundina, kimin addu’a saina saina dawo”..
Biyosa inno tayi har babban falo tana Kiransa amma yak’i dakatawa, saima d’aga mata hannu da yakeyi, yana gab da zai fita ya juyo yana fad’in “karki d’aga murya da yawa ranki ya dad’e, dan kunnen magauta a bud’e yake”.
Yana fitowa Sarkin mota ya taso, dan suna zaune jigum-jigum a rumfar bunun dake sashen na Galadima, duk gaisuwar da suke masa babu ta wacce ya amsa, yau kam ko d’aga hannun basu samuba ma.
Basu damuba dan dolene kowa yamasa uziri.
Da kansa ya bud’e mota ya shiga mazaunin driver, Sarkin mota daya k’araso yace, “ranka ya dad’e ka gafarceni gani”.
Da hannu yamasa nuni da gefen mai zaman banza batareda yace uffan ba.
Sarkin mota bashida za6in daya wuce zagayowa ya shiga.
A 360 Galadima ya ja motar, kamarma ya manta yana cikin masarautane, saida suka fito gaba d’aya sannan ya bud’e baki da k’yar yace, “ka dinga kallon bayanmu, dan nasan dole za’a samu masu binmu”.
Da “to” sarkin mota ya amsa cike da girmamawa.
Sarkin mota yace, “tabbas ranka ya dad’e ana binmu”.
Cije lips Galadima yayi, ya canja hanya, cikin salon iya taku suka 6acema su Harun dake bin su tundaga masarauta.
Hankalin Harun ya tashi kwarai da gaske, dan bai shirya fito na fito da Galadima ba yanzu, saiya cimma burinsa, daga nan komai ta fanjama fanjam, iya zagaye-zagayensu baiga ko motar datai kama data Galadima ba.
Shima yana 6ace musu ya dawo kan titi sosai, Maps d’in GPS ne yazama jagoran Nuna masa hanya, da taimakon Sarkin mota kuma dayasan gari. Danshi Galadima ba tuk’i yakeba idan yazo 9ja, saidai idan ta kama tilas babu yanda zaiyi kamar irin haka.
Sunyi tafiya mai tsawo, yayinda yake Communication dasu Nuren dasu Saleem. A haka ya iso inda suke, duk fitowa sukayi daga motocin, shima Galadima ya fito, idonsa akan agogon hannunsa, yad’an kallesu sannan ya koma kan waya yana fad’in, “maps d’in ya nuna suna a wajennan, kunga kenan tsakanin gidajennan guda hud’une dake kallon juna?”.
“kwarai da gaske suna nan”. cewar Muftahu yana furzar da iska.
Galadima yace, “Sauban da Saleem zaku cigaba da Control namu”. ‘yay maganar yana ciro agogon hannunsa ya mik’a musu, “ga wannan kuci gaba da using dashi”.
Suka amsa da “to” suna kar6a. ya mak’ala abinda zai taimaka masa yaji magana, suma su Nuren duk yabasu suka saka.
Har zasu bar wajen ya dakatar dasu ta hanyar d’aga musu hannu, takawa yay gaban k’ofar gidan farko ya haska gaban gate d’in da fitilar wayarsa, babu abinda yake nema, ya matsa na biyu ma haka, komawa yay d’ayan 6angaren, yana haskawa saiga sawun tayar mota data shiga gidan, duk’awa yay ya d’iba k’asar wajen ya shinshina, ya d’ago ido ya kalli gidan yana jizar lips, saiya zubar da k’asar daya d’iba ya mik’e, da hannu yayma Nuren da Muftahu nuni nan ne.
Tahowa sukai garesa, Aunty Salamah datun d’azun suna daga cikin mota suna kallonsu suma suka fito ita da su Ameer.
A tare suka rissina suna gaida Galadima ya amsa yana bin su da kallon mamaki.
Da yake su Saleem sun sanar dasu Muftahu su Aunty Salamah d’in sai Nuren ya kuma yima Galadima bayani.
Aunty Salamah tace, “ka gafarcemu ranka ya dad’e, nasan zakayi mamkin mun shigo abinda ba’a gayyacemu ba, insha ALLAH zakaji dalilin shigowar tamu nan gaba. game da shiga gidan nan mungama komai, maza 5 ne da mata biyu, wad’anda shigarsu ta tabbatar min suna cikin hadiman masarauta su matan kenan”.
Kai kawai Galadima ya iya jinjina masa. daga nan yaymata nuni da zasu iya farawa.
Da taimakon su Ameer suka shiga gidan.
★★*★★★*★★★*★★
Fitar Galadima da kusan awanni hud’u, around 2am Munaya ta farka a firgice, Inno dake zaune akan Sofa, mom da Aunty Mimi kuma a gefen gadon suka kalleta, tashi Mom tayi da sauri ta nufeta tana rik’eta, itama Aunty Mimi ta taso.
Kuka munaya ta sanya tana fad’in “Mom sun mutu ko? Nasan dama kashesu zasuyi, Aunty Mimi dan ALLAH miye laifinsu su? kwanansu 7 fa kacal yau a duniya, mi suka sani game da abinda ake tuhumarsu? An durk’usar musu da kakansu, an hana mahaifinsu nutsuwar zuciya data rayuwa, shin wannan tabon bai Isa a barsu su taso da shiba a rayuwarsu? Har sai an had’a da salwantar dasu kenan?”. ta fashe da kuka maiban tausayi.
Tasowa inno tayi ta zauna a bakin gadon itama, kamo hannun Munaya tayi ta kwantar da ita a jikinta tana shafa kanta, yayinda itama kwallar kebin nata kumatun.
Aunty Mimi da mom ma duk hawayen sukeyi, kalaman Munaya sun ta6a zukatansu.
Lallashinta da magana mai dad’i suka shiga fad’a mata, sai sauke ajiyar zuciya takeyi, ga jikinta yayi ringim da zazza6i saboda nononta sun mata hak’e-hak’e, rabonsu da shansa tunda rana, tausayinsu ya kuma kamata, tasan yunwa da k’ishi ma kawai sun Isa su k’arar da numfashinsu, hawaye masu d’umi suka kuma gangaro mata a kumatu suna sauka jikin inno dake shafa kanta.
Shayi Aunty Mimi ta had’o mata, amma fir tace ta k’oshi, da k’yar inno ta samu ta lalla6ata tasha Quarter d’in kofin.
Mom tace, “wannan nono kid’an matsesu kozasu rage miki nauyi, dan shine yakawo wannan zazza6in”.
Bata musaba aka kawo k’aramin bowl ta matse aciki, Aunty Mimi ta zubar a bayi”..
Tanason tambayar ina Galadima tanajin kunya, sukuma babu Wanda ya sanar mata komai, kodan gudun k’ara tada hankalinta.
Magani suka bata tasha takoma ta kwanta, yayinda sukuma suka mik’e duk suka d’aura Alwala suna mik’ama Ubangiji kukansu, danshi masanin sirrin 6oyene, yana kallon komai, kuma shine zai kawo iyakar komai d’in.
★★★★★★★
Duk wannan abun dake faruwa su Momma babu Wanda ya sanar musu, saidai sukaji a jikinsu tamkar akwai matsala, sunta kiran numbers amma daga wadda zasu samu a kashe sai wadda network zai hanata shiga.
Sai suka d’aura ko shagalin sunan ne yakawo hakan.
*******************
Tunda Munubiya suka koma gidan kuka takeyi, ko kad’an tak’i sauraren yaran da keta tsula kuka suma, balle tabasu nono.
Ba itaba hatta su Ayusher dasu feena kukan sukeyi, hakama Samha harda shid’ewa, dan itama su tabi bata koma masarauta ba, Yaa marwan da mama Rabi’a ne kawai ke k’ok’arin danne nasu suna lallashinsu.
Yayinda dare yay nisa duk sai suka d’aura alwala suka zo suna mik’ama Ubangijin talikai kukansu da k’ok’on barar bama wad’annan k’anan alhaki kariya da fatan ku6ta.
A 6angaren gidan su Munaya kam duk hassadarsu yau dai sun tausayama gudan jininsu da yaranta, sundawo gidane kowa yana sharar kwalla da addu’ar ku6tar yaran.
Ita innarsu Munaya ma ai ba’a magana, ALLAH kad’aine yasan halin datake ciki, ta shige d’aki ta rufe kanta tana jera nafilfili, dan wannance kawai gudunmawar dazata iya bayarwa a garesu akan wannan lamari mai sark’ak’iya da yawa.
Abban su munaya ma yau harda hawayensa, dukda bashi da tabbas akan hasashensa yasan komai zasu iya, saboda SD yanada kusanci da wannan masarautar sosai, duk abinda ke hannunsa da bayanan daya ajiye ya shiga tattarasu waje d’aya……………✍????
????Duk nisan jifa dai k’asa zai fad’o, kwana 99 na 6arawo, 1 kuma tak namai kaya.????????
Fans insha ALLAH dai abuwa sun fara warwarar zare, sai mubi su Galadima muga yanda zasu dawo mana da triplets d’inmu gida????, yau Munaya tabani tausayi daga ita har Galadima, dan shima dai dannewa kawai yake saboda jarumta, ALLAH ya rabamu da sharrin mak’iyi komai k’an k’antarsa, Harun da sauran munafukai MAZA BISA KANKU????????????????????????????????????????.
Barkanmu da dawowa my sweet fans????????.
Yau bana cikin yanayin dariya????
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*????????????
*_typing????_*
???? *_HASKE WRITERS ASSO….._*
*_♦RAINA KAMA…..!!♦_*
_(Kaga gayya)_
*_Bilyn Abdull ce????????_*
~Book 2~ ????????2⃣7⃣
…………….Tunda suka d’akko yaran suketa kuka, musamman Abdurraheem dahar shid’ewa yakeyi, ALLAH dai yabasu sa’a ne saida suka fito suka fara kukan, neman haukatasu ma sukaso yi tun amotar, jisukai tamkar su rufesu da duka, saidai babu damar hakan, dan basuga abin duka jikin wad’annan kwad’unan yaranba.
Da farko sunga kamar ana binsu, sai daga bisani ne sukaga ba haka baneba, har dai suka iso gidan y’an uku basu barsu sun shak’i iska ba.
Suna shiga suka danna musu wasu allurai, cikin mintuna k’alilan jikinsu dukya saki sukayi luf.
ganin lokaci yaja har kusan 10pm babu alamar wani motsi hankalinsu ya kwanta, dan sunsan dai tabbas sun tsira, wayar wadda ta sakasu aikin suka kira, amma tak’i yin picking.
Cikin matan d’aya tace, “kusan dai bazata d’aga ba, saboda nasan masarauta a haukace take yanzu, saidai mubari zuwa safiya”.
Tsaki d’aya yaja, “kai nifa gaskiya a tsorace nake, gara ta d’auka asan mafita, bana buk’atar gawar yarannan takwana a hannunmu, kunsanfa babansu mayene wlhy, tsaf zai bibiyemu”.
“kai dalla ai yanzu bashida wannan damar, caza’ayi a fad’ama police, sukuma aikinsu zai farane zuwa safiya, kafin sannan munma gama binne gawar yaran mun kama gabanmu”…..
“eh kumafa hakane”.
Suna tsaka da wannan hirarne su Galadima suke shigowa, gidan k’aton gaskene dan haka suka kasa fahimtar INA zasu dosa, Galadima Yakuma danne abin kunnensa da d’anyatsa d’aya cikin murya k’asa-k’asa yake fad’in “Sauban kufara muje”.
“yauwa Yaya zaku shiga hannunku Na haggu, duk sunajin maganar dan haka sukabi hannun haggu, yayinda su Ameer ke binsu a baya suma. Galadima dake gaba ya bud’e k’ofar a hankali duk suka shiga, daga can Saleem yace, “duk Ku rarrabu sir, dan abin ya nuna yaran suna ainahin tsakkiyar gidanne”.
Batare da sunyi magana ba duk suka rarrabu.
‘Daya acikin 6arayin yace, “kai nifa kamar motsi nakeji gaskiya”.
“to sannu mai kunnen maciji”. cewar d’aya aciki.
Cikin matan d’aya tayi dariya tana fad’in “nakula kaidai bibo matsoracine halan?”.
Hannu ya d’aga zai kwad’eta, a harzuk’e yana fad’in “k wlhy kacaccalaki zanyi, bar ganin kinfito daga masarauta, kubadan ma an had’amu aiki dakuba kun Isa saninmu ne? jimin y’ar iskar mara kunya”.
Hak’uri y’an uwansa suka bashi, ya mik’e yana jan tsaki ya fito danya duba.
Galadima dake la6e cikin labule yay saurin fitowa, abinka da dogon mutum dan danan yasamu damar shak’osa ya shaka masa abin hannunsa, tun yana k’ok’arin kare kansa har jikinsa ya saki ya kwantar dashi a k’asa.
Jinjina Muftahu dake kusa dashi yamasa, sannan suka cigaba da shiga.
‘Dayar baiwar tana kitchen tare da wani suna iskancinsu Nuren yasamu damar sad’ad’awa, (kunsan dai shahararren kidnapper ne????????) yauma tsiyar ya aikata wajen jefa ma namijin handkerchief a fuska, macen tai yunk’urin zuba ihu yasa k’afa ya tad’ota ta fad’in, sannan ya danne bakinta da ya shak’a mata itama.
K’arar fad’uwarta taso fargar da sauran, dan haka duk suka mik’e suna fara lek’e-lek’e, aikam Muftahu yasamu ya tad’e d’aya ya fad’i, Ameer dake bayansa shima ya shak’a masa, harda mangareshi yana fad’in “kwallon shege taka ta k’are, inakai ina satar sarakunanmu insha ALLAH”.
dariya taso kufcema Muftahu amma ya danne bakinsa da hannu yana girgiza kai saboda tsiyar Ameer.
Fad’uwar wani da suka juyo ya sakasu kuma saurin waigawa wajen, Galadima ne ya sakeshi ya fad’i, “shegen k’arfin jinine dashi dak’yar abin yay masa tasiri”. Galadima ya fad’a yana halbinsa da k’afa.
Gaban d’ayar baiwar dake la6e jikin labule ya fad’in, dan tabbas wannan muryar Galadima ce, kowa yasan bai iya R ba, zuface tashiga keto mata jikinta na 6ari, ta to she bakinta saboda kuka daya kufce mata, saigata tana tsilala fitsari saboda ganin Galadima yanufo ta wajen, shikenan itakuma tata tak’e, wannan zakin gagara badau d’in binneta kawai zaiyi da ranta.
Waige-waige Galadima ya fara saboda jin numfashin mutum dayakeyi kad’an-kad’an ta wajen, har yayi gaba ya dawo baya yana yaye labulen wajen. shi da farkoma ya zata aljanace saboda yanda ta zazzaro masa ido. fincikota yayi ya Watso tsakar d’akin, mamaki ya kamashi ganinta da kayan manyan kuyangin gidansu.
“tashi tsaye”. ya fad’a cikin matuk’ar d’aure fuska, kad’an yarage kashi ya kufcemata.
“ina suke!!!”.
Yafad’a cikin matuk’ar tsawa daya firgita hatta su Sauban dake saurarensu a waya.
Wannan tsawar tasa ce ta saka d’ayan fitowa a tsorace da gun a hannu, Aunty Salamah dake bayansa bai saniba ta hankad’ashi yay gaba zai fad’in, Nuren ya ida tad’eshi da k’afa.
Gun d’in data fad’i ta silalo gaban Galadima ya taketa da k’afa yana huci da taunar lips. Handkerchief d’in hannunsa yasaka ya d’auki bindigar, ya saita namijin da ita.
Mazari jikinsa ya fara yana d’aga hannu sama, “dan ALLAH ranka ya dad’e karka kasheni, wlhy bansan komaiba, oganmu ne yasan komai da wannan baiwar”.
Kunamar bindigar Galadima ya d’ana, nanfa su Muftahu duk suka rud’e, Nuren yace, “Brother please karkayi harbi, nasan zasu fad’a mana, dan ALLAH kayi hak’uri”.
Gaba d’aya jijiyoyin kan Galadima sun mimmik’e, sai fidda huci yakeyi a wahalce.
Muftahu ma yashiga rok’onsa, Su Saleem dake sauraren komai dagacan duk suka rud’e, Sauban yace “yaa Sam ALLAH ya huci zuciyarka, amma idan ka aikata haka a wajenwa Zamu samu hasken sauran abubuwan?, dan ALLAH kayi hak’uri badan mun isa mu saka ka ba, saidan halin da mahaifinmu ya tsinci Kansa tsawon shekaru, gakuma dama tazo mana ta Sanin sirrin 6oye, muyi amfani da ita ta sauk’ak’ak’iyar hanya….”
Sakin gun d’in Galadima yayi ak’asa yana dafe k’irji, wani mugun bugawa zuciyarsa keyi, da baya-baya yanemi zubewa a k’asa, cikin hanzari Nuren da Muftahu suka taresa, da taimakonsu ya zauna akan kujera. Yana nuna baiwar da d’ayan hannusa.
Aunty Salamah data fahimci mi yake nufi tace, “ina yaranne?”.
Jikin baiwar Na 6ari ta nuna k’ofar wani d’aki, shiga Aunty salamah tayi itada Ameer suka d’akkosu.
Saidai duk a firgice suke, dan yaran babu alamun rai tare dasu, zufa ta shiga ketoma Aunty Salamah, haka ta fito rungume da Abdurraheem da Amaturrahman, shikuma Ameer ya d’akko Abdurrahman yana fad’in “Aunty kamarfa yarannan sun mutu”.
Wannan kalma caraf a kunnen Galadima.
Wata muguwar zabura yayi yamik’e tsaye, sai ya kuma dafe k’irjinsa da sauri hajijiya tafara katantanwa dashi, basu fargaba sai jinsa sukayi kawai a k’asa.
Gaba d’aya suka kuma rikicewa, sukayi kansa.
Muftahu yace, “bamuda isashen lokaci, asuba ma ta gabato, dolene mubar gidannan dan ko yaushe zamu iya gamo da abinda bamu shirya masaba”.
Duk sunyi na’am da wannan maganar tashi, nan fa suka fara kwasar wad’anda suka sumar suna kaiwa mota, sannan suka tasa k’eyar d’ayar baiwar da wancan, suma.
Yayinda Nuren yad’an bincika gidan, ganin babu wani abunda zasu k’aru dashi yazo suka kama Galadima daya Suma suka fita dashi.
Hankalin Sauban ya tashi matuk’ar tuk’ewa, ya fito yana nufarsu da ta6a jikin d’an uwansa, “Yaa Nuren miya farune? miya faru da Yaa Sam?”.
“Sauban bamu hanya, ba lokacin wannan baneba yanzu”.
Sole Sauban ya matsa baya hawaye Na kwarara a idonsa, suka shinfid’ar da Galadima a bayan mota, sai lokacin Sauban yaga yaran a hannun Aunty salamah da Ameer, da hanzari suma ya nufesu, Aunty salamah ta bashi Abdurraheem, jujjuya yaron yayi yaji kamar baya numfashi, “innalillahi….” yashiga maimaitawa zufa Na keto masa, dolene Yaa Sam ya suma, hawaye yafarayi yana rungume yaron a jikinsa, Tausayin dukkan ahalinsa da suka kwallafa rai ga yaran ya kamashi, musamman ma iyayensu, ya ALLAH nasan bazaka jarabcemu da abinda bazamu iyaba, ALLAH kabamu juriya”.
Muftahu yace, “su shiga mota, duk shiga sukayi, Nuren dasu Ameer suka wuce da wad’ancan sauran wani waje daban, Muftahu kuma ya kira police d’in da suka shirya komai dasu, a hanya suka had’u, sai sukai joining d’insu tamkar tare sukayi aikin, suka kira manyansu suna sanar musu gashifa sun kama wani matashi da baiwar masarauta da yaran….
Wannan labari yama su d.p.o dad’i ya kira IG shima ya sanar masa, yaji dad’i shima, koba komai mai martaba zai yaba k’ok’arin dasukayi, akace yanzu suna inane?.
Amsawa sukai da gasu a masarauta, dan harda Galadima sukayi aikin, yana kuma cikin wani yanayi shida yaran yanzu haka.
Basuda za6in daya wuce suce musu to suma gasunan zuwa masarautar.
Tun’a mota su Muftahu sun gargad’i baiwar nan da d’ayan mutumin akan suce su biyune suka sacesu, inhar sukace basu kad’ai bane wlhy saiya kashesu, sannan su tanaji fad’ar wani abun ba ainahin gaskiya ba, (dan Galadima baya buk’atar police su shiga cikin aikinsa yanzu, yafison saiya kama kowa sannan, dan inhar police suka shiga aikin mutane da yawa zasuyi escape ne) shiyyasa Muftahu yayma wad’ancan gargad’in tunma kan su k’arasa cikin masarauta.
Da yawa wasu basu rintsaba a masarauta gagara badau yau.
Munaya dai dole aka sake d’irka mata allurar barci mai k’arfi, dan kusan kuma haukace musu tayi gabannin asuba, dalilin wani barci daya figeta tayi mafarki mai matuk’ar tada hankali.
Su inno Na zaune har yanzu suna kai kukansu ga ALLAH Muftahu da Sauban suka shigo d’auke da Galadima da suka kamo tamkar gawa, sai Saleem da police biyu dake falo d’auke da yaran sukuma.
Zaram duk suka mik’e suna tambayar lafiya? Miya sami Galadiman?.
Basu sami wata amsaba, saida suka kwantar dashi a gadon sannan Sauban ya share hawayen fuskarsa yana fad’in “suma yayi inno”.
Aunty Mimi da mom sukayi kan Galadima suna kuka, inno tace, “kun samo yaranne?”.
“eh gasu can a falo tareda police, saidaifa duk sun mutu, shiyyasa ma Yaa Sam ya suma”. yak’are maganar yana kuka.
Hawaye suka zuboma inno, waya ta d’auka ta kira papi, Wanda shima dai a zaune suka kwana dagashi har Sarki jalaludden.
A time d’in dama har ankai musu bayanin shigowar su Muftahu d’in.
Yau dai kam tilas Manyan Sarakuna biyu suka nufo sashen Galadima da Kansu, abinda waninsu bai ta6a yiba kenan.
Maganar ganin yara yafara baje Masarautar tun’a daren, dan kowa kunenensa a bud’e yake, da masu fatan a gansun da masu fatan kar’a gansun.
Lokacinda papi da mai Martaban suka iso Inno Na rungume da yaran duka tana hawaye, sukuma su Aunty Mimi suna bedroom wajen Galadima.
Kusan a tare Akash da Dr jalal suka iso dasu papi.
Mai Martaban da papi suka kar6i yaran daga hannun inno, Suna zama bisa kujerun.
Akash wajen Galadima ya nufa, dukda ba shine likitansa Na zuciya ba zai iya bashi taimakon gaggawa, shikuma Dr jalal ya fara kar6ar Abdurraheem dake hannun inno, yan d’ube-dube, yayi Na tsawon lokaci kafin ya ajiyeshi ya kar6i Na hannun mai Martaban, shima yagama duk abinda ya dace ya kar6i Amaturrahman a hannun papi, ajiyar zuciya ya sauke yana fad’in “Alhmdllh duk basu mutuba, allurar barci mai k’arfi sosai suka musu, shiyyasa numfashinsu yay nisa sosai, danta musu k’arfi da yawa, amma idan kuka saka kunne nawasu mintuna saitin jikin zuciyoyinsu zakuji suna motsawa kad’an-kad’an, sai dai ta wannan tafi yin k’asa sosai gaskiya”. Ya nuna Abdurraheem dake hannun inno.
Su mai Martaban suka sauke ajiyar zuciya suna hamdala ga ubangiji.
A cikima Akash nata iya bakin k’ok’arinsa ganin Galadima ya farfad’o, Ahaka su mai Martaban suka k’araso cikin d’akin d’auke da yaran a hannun, Munaya Na gefen Galadima an lullu6a mata bargo batasan wainar da ake toyawa ba, dan barcin nata shine mafita fiye da zama ido biyu.
A gadon suma yaran duk aka shimfid’esu, Dr jalal yad’an musu dabarun likitoci sauran kuma aka barma ubangiji ikonsa Na jiran farkawarsu.
Hankali kuma duk saiya koma ga Galadima da aketa fama.
Har aka kirayi sallar Asubahi babu amo babu labari akan farfad’owar tasa. daga k’arshe dai Akash saida ya kira likitan Galadima na zuciya. Shiya dunga fad’ama Akash d’in yanda yadace yayi, lokacin shiga salla ya saka su mai Martaban fita masallaci dole, sukabar Akash da Dr jalal dake taimaka masa suna aikinsu, saisu Aunty Mimi da suka kasa matsawa ko nan da can, Sauban ma da k’yar su papi suka lalla6asa yabisu salla.
Har gari ya waye sashen Galadima ya cika da manyan masarautar irinsu mama Fulani matan Sarki da sauransu Galadima babu wani bayani, zuwa yanzu ma wasu sun fara tunanin kodai yama mutu ana 6oyewane kawai.
Wajen 8:00am Dr Yaseen Ali Modibbo babban likitan zuciya da akeji dashi ya iso, bisa kiran da Dr jalal ya masa yafad’a masa, dan abubuwan da sukaima Galadima bai farfad’oba Akash yakuma sanarma likitansa, shine yace tofa gaskiya Kodai asamo ainahin likitan zuciya ko kuma su taho dashi kafin cikar awanni 12, idan ba haka ba komai zai iya faruwa.
A k’iyasin da sukayi cikin awanni 12 bazasu Isa india ba, tunda duk tsiya sai an samu jirgi mai tafiya, sannan ma kafin komai ya biyo baya. Hakkane yasaka Dr jalal kiran Dr Yaseen Ali Modibbo d’in, cikin amincin ALLAH kuma ya amsa zaizo d’in, saikuwa gashi ya iso.
Canjama Galadima d’aki akayi, dukkan kayan aikin da Dr Yaseen yazo dasu aka shigo dasu, rufe d’akin sukayi suka duk’ufa su uku kansa suna taimakon Dr Yaseen d’in.
Sun jigata kwarai da gaske kafin zuciyar Galadima tafara bugawa k’asa-k’asa, sai numfashinsa yafara fisga yana k’ok’arin fita. Duk ajiyar zuciya suka sauke. Suka cigaba da aikinsu, ana sakama Galadima wani abu a k’irji kamar dutsin guga, saiya girgiza sannan a cire, akuma maidawa. Basu barsa ba saida yasaki wata ajiyar zuciya mai matuk’ar sauti, harsu mai Martaban dake falo saida suka jiyosa kuwa.
Wannan ne yasaka zukatan doctors d’in uku sanyaya, Dr Yaseen da Dr jalal suka had’a baki wajen fad’in “Alhamdulillah!”.
Numfashin Galadima ya dawo dai-dai, amma sun masa allurar barci danya samu nutsuwa.
Yaranma an kawosu ne Dr Yaseen ya kuma bincikawa, shima dai yace suna da ransu, amma Abdurraheem yanada ciwon zuciya shima, shiyyasa yafi sauran y’an uwansa jigata, ALLAH nema dai yay rabon yanada sauran numgashi, amma allurar tamasa k’arfin da zata iya dakatar da bugun zuciyarsa. Suma dai sun kuma samun taimako, musamman ma dai Abdurraheem da tausayinsa ya kama mutane da yawa a wajen.
*_2:00pm_*
Zuwa wannan lokacin Munubiya da mama Rabi’a da Ayusher Feena duk sunzo masarautar, Hakama baba k’arami da daddy, dan an sanar musu samo yaran da halin da galadima yake ciki.
Amma saboda kara irinta Abba da innarsu Munaya sai suka bar su Baba k’arami da maman Fauziyya da mamansu yaa Hameed, maman Safara’u suka taho, sai innaro da gwaggo Safiyya.
Ba’a barin wani bak’on fuska shigowa masarautar a yau, amma su sai mai Martaban yasa aka shigo dasu, basu samu ganin ko d’aya a cikin su Munaya ba, saidai Munubiya da aka shigar d’akin galadima inda Munaya ke kwance, Sauran kuma sun shiga ayarin y’an zaman jigum-jigum da jiran tsammani.
Har zuwa wannan lokacin Galadima da Munaya babu Wanda ya farka, Amaturrahman da Abdurrahman dai sun farfad’o, sai dai suna kuka ko fita bayayi.
Wanka laraba ta musu aka gasa musu jikinsu sosai, yau dai dole aka nemo madarar da Galadima bayason susha d’in, ita aka dama aka basu sukasha, aiko sun shata sosai dan yunwa sukeji, bayin ALLAH, rabonsu da abinci tun jiya da rana kusan I war haka d’in.
Tausayinsu ya kama Munubiya dake basu madarar, tana yi tana sharar hawaye, da da farko nono inno tace ta basu, sai papi yace, “a’a kar ayi wannan gangancin, dan ba’asan abinda ALLAH zaiyiba wataran, ko akwai k’addarar aure a tsakanin yaransu, kar azo ayi Dana sani a watarar da baza’a iya maido wannan ranarba balle a gogo 6arnar da akayi”.
Kowa ya gamsu da wannan magana, dan haka Muftahu yafita suka nemo madara shi da Saleem.
Shine aka basu.
Baiwar da aka kami da mutumin kuma suna hannun police, kuma kowa yaji cewar tana cikin bayin gidan wad’an da aka aminta dasuma sosai, saidai ba’asan ta wane sashe bace.
Wannan Abu ya tsurar da zukatan Sauran bayin, dan dolene ya shafesu.
Hankalin Uwargidan Sarki Sarauniya Zulfah (mahaifiyar su matawalle) a tashe yake, amma dayake ta iya takunta bazaka ta6a fahimtar haka ba, saima nuna tsantsar damuwarta akan lamarin da tayi fiye da sauran matan Sarki. dama kuma tafi nuna kulawarta ga Galadima kowa yasan wannan, shiyyasa babu Wanda yakawo wani Abu game da ita, saima wasu daban ake zargin.
Munaya da Galadima sun farfad’o ne kusan time d’aya, amma Galadima ya riga Munaya, dama allurar awanni 4 kacal aka masa, da Sunan ALLAH a bakinsa ya farka, sannan yafara kiran yaransa d’aya bayan d’aya yana fad’in karsu tafi su barsa..
Rik’eshi Dr Yaseen yayi yana fad’in “ka kwantar da hankalinka ranka ya dad’e, dan zuciyarka tana cikin yanayin jiran k’iris ne, inamaka albishir da cewar yaranka suna raye, yanzu nan zakagansu insha ALLAH”..
Galadima ya sauke nannauyar ajiyar zuciya yana kallon Dr Yaseen, ya lumshe idonsa a hankali sannan ya bud’e, hanunsa ya d’ora akan saitin zuciyarsa saboda wajen yamasa matuk’ar nauyi.
Ana haka Dr jalal ya shigo d’auke da yaran biyu, dan Abdurraheem shi yanan a d’akin kusa dashi bai farfad’o ba.
Tunda Galadima yaga yaran sa suna a raye saiya kuma rungumesu a k’irjinsa da Dr jalal ya d’ora masa, wasu hawaye masu zafi suka gangara gefen kunnensa.
Dr Yaseen yaji dad’in kukan da Galadima d’in yakeyi, dan zai rage masa rad’ad’in da yakeji da nauyin zuciyar, hakan ya nuna aikinsu zaiyi k’yau insha ALLAH.
Galadima ya dad’e rungume da yaran, saidaga baya ya farga babu guda d’aya.
A hankali ya bud’e baki yana fad’in, “ina d’ayan?”.
Murmushi Dr Yaseen yayi, yace, “gashi a gefenka yana barci shima”.
Juyawa Galadima yay ya kallesa, ganin d’an cikin yaron Na motsi alamar fitar numfaahi sai dad’i ya kuma ratsashi, ya lumshe idonsa yana yun k’urawa zai tashi zaune, taimaka masa. Dr Yaseen yayi, yatashi rik’e da yaransa, kwantar dasu yayi sannan ya matsa ga Abdurraheem hannunsa dafe da k’irjinsa har yanzu, rankwafawa yay kan yaron ya sumbaci goshinsa da kumatunsa, sannan ya shafa kansa la66ansa suna motsawa alamun yana masa addu’ar fatan samun lafiya a garesa shima.
A 6angaren Munaya Itama tana farkawa da kuka ta farka, tana kiran yaranta, itadai afad’a mata idan sun mutu kawai saita hak’ura.
Rungumeta Munubaya tayi tana lallashi da mata albishir d’in dawowar yaran garesu, hakan yasaka Munaya d’agowa da sauri tana kallon Munubiya, “Sweetheart da gaske kikeyi?”.
“da gaske nakeyi Sweetheart, yanzu haka suna tare da mahaifinsu”.
Dad’i ya ratsa Munaya, ta kuma k’ank’ame Munubiya suka rungume juna suna kuka da dariya lokaci d’aya.
Hakan kuma saiya sanya su inno kukan tausayinsu da sha’awar wannan k’aunar juna nasu.
Saboda su mai Martaban sun shiga wajen Galadima sai akace ita Munaya tayi wanka kozataji k’arfi kafin su fito.
Bata musaba ta amince, ruwa mai zafi laraba ta had’a mata, tashiga wankan. Tanayi tana kukan farin ciki. bata cuci kantaba tayi wanka sosai ta gasa jikinta.
Kafin ta fito an gyara d’akin tsaf, sai k’amshin daddad’an turaren d’aki yakeyi, babu kowa duk sun fice.
Su mai Martaban suna tare da Galadima, sunyi farin cikin tashinsa, hakama yaran. sunkuma yima Abdurraheem addu’ar tashi shima. Sun d’an jima a d’akin, dan har saida aka shigo dasu Dady da baba k’arami, Yaa marwan, Yaa Hameed suma suka gaidashi da masa jajen ALLAH ya kiyaye gaba sannan suka fita gaba d’aya.
Daga nan manyan irinsu mama Fulani, inno matana Sarki da sauran su duk suka shigo suma, harda su innaro da akaita kuka.
Galadima dai Kansa kawai yake iya d’agawa, idonsa a lumshe. Baya buk’atar kallon kowa a cikinsu.
Su inno duk tausayinsa ya kamasu.
Innaro aka share hawaye tace, “barka da arzik’i kaji, ALLAH ya kiyaye gaba, ya shiga tsakanin nagari da mugu, ya tona asirin duk makirin dake cikin wannan satar yara”.
Duk da amin suka amsa. Galadima ma yace amin akan la66ansa. sai tunani yake ina Munaya take?, dan hankalinsa yafara tashi da rashin gilmawarta, musamman daya tuna a halin daya tafi itama ya barta.
Yadai kasa daurewa ya bud’e baki da k’yar yace, “Mom ina Munaya wai?”.
Saida mom ta matso da kunnenta sannan tajishi, tasan yana lafiya ma ya aka k’are da k’asaitar magana balle yanzun. Murmushi tayi, tace, “tana d’aki, itama sai yanzu ta farka, dan dole aka sake mata allurar barci bayan tafiyarka, waccan bata dad’eba ta saketa”.
Tausayin Munaya ya kuma kamashi, ya jinjina kai yana yunk’urawa zaune sosai. Cikin yamutse fuska yace, “Mom nima yakamata nayi wanka Na rama sallolin dake kaina”.
Mom tace, “to bara a kira su Muftahu su kamaka ”.
Kansa ya girgiza mata da mata alamar, zai iya da kansa.
Mom tace, “Alhmdllh”. Rigarsa ya jawo yasaka, dan da dagashi sai best. d’aukar Abdurrahman da Amaturrahman yayi ya fito, yabar mom tana gadin Abduraheem dabai farko ba. babu kowa a falonsa Dan duk sun fice.
Da k’afa ya turo k’ofar, Munaya Na zaune a bakin gadon rik’e da mansa zata shafa amma dukta kasa, burinta taga halinda Galadima da yaranta suke ciki kawaine damuwarta, gashi har yanzu babu Wanda yazo yakirata akan su papi sun fita. bud’e k’ofar ya sakani d’ago ido. Zummbur na mik’e tsaye ganin Galadima rungume da yaran, ai yau nama manta dawata kunyar towel na d’aura, hawaye suka shiga zarya tsakanin idona da kumatu, Galadima ya tako a hankali zuwa gareni idonsa a kaina. Da sauri namatso garesa nima, nahad’ashi shi da yaran na rungume ina sakin kuka mai k’aramin sauti.
Shiru yay kawai ya zubama gashinta ido yana tausaya mata daga ita har yaran, ansakasu a yak’in dabasu San mafariba, ya godema ALLAH da yarannan sunada sauran numfashi a duniya. Da baisan yanda zaiyi da munaya ba. Ganin kukan nata zaiyi yawa ya bud’e baki da k’yar yace, “ya isa mana”.
d’ago idanu nayi na kallesa, cikin muryarta data dishe saboda kuka nace, “Nagode yalla6ai, dasun mutu nima mutuwa zanyi”.
Murmushin gefen baki yayi, cikin d’age gira d’aya yace, “dama ana sonmu haka?”.
Sai yanzu kunya ta kamani, nai k’asa dakai ina kallon k’afafunmu.
Bai sake cewa komaiba ya ra6a ta gefena yaje ya shimfid’e yaran akan gado.
bathroom ya nufa yana cire rigar jikinsa, nidai Na k’arasa gadon Na rungume yaran ina sumbatarsu, wani dad’i da tsantsar farin ciki Na ratsani, Na d’aukesu Na fara shayar dasu ko zasu rage nauyin da sukamin, aikam kamar jira sukeyi suka kama sha. Hannun rigar namijin Na d’aga saboda tanan muke gane shaidarsu, ganin Abdurrahman ne saina fara tunanin ina Abdurraheem shikuma?, hankalina yaso tashi amma saina daure ina jiran Galadima ya fito naji daga garesa.
Galadima dake kallonta bata saniba ya d’an cije lips, ya tabbatar yanzu tana son yaransa, amma baisan miyasa take ignoring d’insu ba idan yana waje? Kokuwa tsabar jan ajinne oho?.
Har Lokacin daya fito wankan tana shayar dasu, ta shafa kan wannan ta shafa Na wannan, sosai suka birgeshi itada yaran, jin kamar motsi yasakani kallon wajen, da sauri na janye yaran daga bakin nono naja towel d’in na rufe abinna ina turo baki gaba.
Baki ya ta6e yashiga takowa inda muke, ya rankwafo kaina ruwan fuskarsa yana d’iso min a jikina, a kasalance yace, “wane darene jemage bai ganiba malama, tunkan su sha ni……..”.
Da sauri na saka hannu na toshe masa baki.
Zama yayi yana janye hannunna, cikin waro idanu yace, “to mikike tunanin zan fad’a? lallai kinfi k’arfina, niba can Na dosaba to”.
Sosai naji kunya, na sauke yaran a kan gadon na sakko, zuciyata cikeda mamakin sa, ya d’aure fuska yana basarwa yayta sakin magana kuma kamar bashi yayiba.
Ficewata nayi bayan na d’auki bathrobe d’insa na d’ora akan towel d’in jikinna.
Wani kallo ya bita dashi yana ta6e baki, kafin ya maida ga yaransa daketa kalle-kalle, ya shafa kumatunsu sannan ya mik’e zuciyarsa na tunanin su Momma, addu’arsa d’aya kar wani ya sanar musu.
Kasa fitar nayi saboda jin kamar da mutane a falon da zanbi ya sadani da 6angarena.
Badan nasoba tilas Na dawo baya.
Galadima dake gaban mirror yana shafa mai yana kallonta ta ciki, amma sai yayi biris tamkar bai gantan ba.
Komawa nayi na zauna a bakin gado ina tunanin mafitar yanda zan samu kaya, da jin haushin sharenin da yayi.
Ana haka mukaji knocking, saida ya kalli Computer d’in yaga Mom Ce d’auke da Abduraheem sannan ya mik’e yana amsawa..
Zuwa yay ya bud’e mata, bata shigoba ta mik’a masa yaron da har anmasa wanka Ashe, ta mik’a masa kaya a leda tace na Munaya ne.
Galadima yace, “mom ya tashine?”.
“ya tashi, tunma fitowarka babu dad’ewa, harma an masa wanka”.
Sumbatar kumatun yaron yay yanama mom sannu
Idonsa akan yaron yana kuma sumbatar goshinsa cikin lumshe idanu ya k’araso inda nake dana zuba musu idanu cikeda sha’awa.
Kusa dani ya zauna ya d’ora minshi akan cinya. nima rungume kayana nayi na sumbaci goshinsa, inason bashi abinci amma inajin kunyar Galadima, gashi ya zubamin ido yak’i tashi.
Lura da hakan dayay ya sakashi yin miskilin murmushi ya mik’e yabar wajen.
d’an hararan bayansa nayi ina fad’in mugunta dai babu k’yau a kan la66ana………………✍????
“Hummm fans nasan kwace wai ina Harun ne?????, kumuje zuwa dai danjin ina ya shige haka? Ita kuma sarauniya Zulfah (uwar gidan Sarki mike matsalarta)?.????????
*_Ya Rabbi ka gafarta ma iyayenmu_*????????????