GURBIN IDO 26

“I mean bani dako sisin da zan batar don komawata gida,bcoz ban shirya ba” dole dariya ta subucewa jabir,cikin ransa yace
“Kayi ka gama,komawa gida dole,mu lafiyarka da hankalinka mukeso,tafi mana kuma komai”
“Okay,…..duk naji,but bani zan maka komai ba,you know,dole kaje da kanka,tunda kai mai laifi ne a wajensu yanzu” kamar bazai amsa ba kafin yace
“Naji” ciki ciki,kada kai jabir din kawai yayi yana nufar kitchen,cikin ransa yana fadin
“Allah ya shirya ja’afar,mai zama dashi sai ya shirya,zuma ga zaqi ga harbi ga kuma ba tsoro” .
Abinci ya shiryo musu,ya kuma kawo har nan inda ja’afar din yake,yanata wani ciccijewa da basarwa amma jabir yayi kamar bai gane me yake nufi ba,ya gama daagiyar duka ya sauko suka fara cin abincin.
Yadda jabir din yaga yana ci ya tabbatar masa a kwanakin da ya qauracewa gidan bai cin wani abincin kirki,dama can shi din irin mutanen nan ne da ba abincin kowa suke iya ci ba,sau tari sun gwammace su haqura da abincin,sai yaji tausayinsa ya darsar masa a rai,yaji har cikin zuciyarsa yana fatan wannan auren ya zame ma rayuwar ja’afar din wani babban sauyi da kuma ci gaba,suna gamawa kiran amaryarsa ya shigo,don haka ya miqe yabar wajen,jaafar ya bishi da tsaki da kuma harara,ganin yadda yaketa zumudin amsa kiran nata.
[