GWAJIN DAFI COMPLETENOVELS

GWAJIN DAFI COMPLETE

GWAJIN DAFI COMPLETE HAUSA NOVEL

Tarakashi da adawo lafiya sannan ta rufo k’ofar ta zauna a bakin gadon,tasa hannu tashare mata jinin da yake gefen bakin ta,tabud’e idanunta suka kalli juna.Lidiya tad’an d’age gira”wallahi kashin kare baya taki” Baranzan shine yadace dake ba wancan tsinannan bahaushen ba,danni bazan fasa fad’a miki gaskiya ba,kome naku d’aya da Baranzan”Hun wai saboda wani bare da bai san ALLAH yayi ruwan tsiran kiba kike ga ba dani,indai bani namiki magana ba ke bazaki minba. Tamaida idanunta tarufesu”ita abinda yadami zuciyarta shi d’in ne yadameta”daga ita har Baranzan basu d’ad’ata da k’asaba”kowa da kiwon daya kar6e shi mak’ocin me akuya ya sai kura”.

A’isha tabiyo Sudaida dad’an gudunta da aka buga tara”Ke malama jirani”Tatsaya tana kalllanta har ta k’araso”Kefa kika ce ba inda zaki”.Aisha tagyad’a kai”Eh nafa sane naga gaba d’aya ajin an watse an barni kamar mayya,me zaki siyane?Ta tambayi Sudaida”Ba abinda zan siya dan bana jin cin kome na makarantar nan yau.Wajan Nasmat zani.Tarik’o hannunta”Dalla shareta zo muje wajan Yayanku tad’an turo baki me zanje in mishi?Ke shifa Yaya d’ansarai ba yaso a dameshi.Ke dai zo muje mana ni wallahi ina sanshi.Sudaida tamata wani kallo sannan ta ta6e baki”Lallai kinji jiki, Yaya Julaibib d’in kike so?.Eh wallahi”Yanayin shi me sanyi ne,baya san hayaniya.

Wa alaikumussalam.Ya amsa sallamar su. A’isha tamata nuni wai su zauna,ita kuma tana nok’e kafad’a.Yad’an d’ago yakalle su,sai yacigaba da nazarin d’aya daga cikin tarin littafan dake gefan shi,hannunshi rik’e da jan biro da alama hannu yake sawa akan aikin daya basu.Yasake d’agowa yakallesu ganin sun zauna sunata kallanshi”yaya wani Abu ne?Aisha tayi tsagal “Yaya Julaibib dama… Da… Sauran kalaman suka mak’ale saboda wani rikitaccen kallo da yake mata,sai ta mik’e “bakome Sudaida taso mutafi.Har sun jiya Sudaida taji kiranshi.Ta tsaya sannan tajuyo tana kallanshi ya yafitota da hannu.Tak’arasa wajan”Yaya Julaibib gani “Yad’anyi murmushi”hala kud’in taran na ku ba yawane yau?A ah wallahi muna da kud’inmu. Yamik’a mata wasu kud’in”duk da haka sai Ku k’ara,tasa hannu biyu takar6a”Mungode ALLAH yak’ara bud’i.Yad’an bita da kallo yana murmushi.

A’isha taja tsaki kawai anzo wajanka amma saika wulakanta mutane. Sudaida tad’aga mata hannu”a ah wallahi Yaya d’an Sarai bashi da wulakanci, kuma baki ga abinda yakeyi bane?Ai dama nafad’a miki shi fa baya so adameshi…Nasmat tak’araso wajan tatarar da Aisha tana k’unk’uni “Ke da wa kuma?Da Yayanku d’an wulak’ancin can mana tanu mata Julaibib d’in da d’an yatsa.Nasmat ta kyalkyale da dariya miskili kafi mahaukaci ban haushi”to amma shi da baya shiga shirgin mutane to me yahad’o ki dashi? Tawatsa hannu”shareshi kawai suka cigaba da tafiyarsu suna hira.

A sanda hantsi yadubi ludayi na safiyar lahadi suna hirarsu da Inna Khalifa d’an mak’otansu yashigo da gudunshi”Yaya Julaibib ana sallama dakai”To kace ina zuwa. Suka cigaba da hirarsu,ganin bashi da niyyar tashi Inna tace”Tashi katafi mana.Yamik’e To Inna yad’auki rigarshi daya cire yana sawa,a zaure yak’arasa sawa,yana fitowa caraf idanunsu yahad’u,yamata wani irin kallo data kasa fassarawa.Tayi yar dariya”Malam d’ansarai kenan wato ganina yasa ka canjawa kamar kaga me tagayyara rayuwarka har abadan duniya ko?To ni dai nazo gaisheka ne,wancan makon ko sau d’aya ban samu nazo makarantaba dan bani da lafiya kuma a dalilin sanka nashiga halin dana shiga amma ko katambaya”Lafiya kuwa Kasham bata zuwa makaranta?To koma dai yayane Thank God naji sauk’i,ina kuma so kamin jagora zan shiga gaishe da Mama.”Bata nan”Yabata amsa a takaice. Takama ha6a????d’ansarai wallahi bakayi kama da masu zabga k’arya a kalaman suba,nafa tambayi yaran yacemin tananan,inaso muyi kome cikin mutunci da girmama junane shi yasa ban shigo kai tsaye ba,amma kai naga kamar ba hakama kake so ba,idan natsaya rarrashinka kuma raina ne kawai zai 6aci a banza,tunda har yanzu baka d’aukeni wata tsiya ba,ko albarkacin k’aunar da nake maka ban ta6a ciba.

Koma inda kika fito,tunda ba gayyatoki nayi ba.Tagirgiza kai idan kamin haka tsakani da Allah baka min adalci ba,tanuna mishi Bible d’in hannunta daga majami’a (Church) nake,ana tashi nashigo cikin gari ko gida ban koma na ajiye Bible d’in ba,duk dan d’okin ganinka.Yau d’aya dai kamin adalci a matsayina na yar Adam bama masoyiyar kaba.

Inna tafara jiyo hayaniya.”Na rantse da girman ALLAH idan kika tako inda nake sai na 6allaki.Inna tajuyo furucinshi cikin fad’a.Kai dawaye Julaibib?Inna ta tambayeshi bayan tashigo zauren.Cikin tafasar zuciya yajuya yakalli Inna idanunshi jawur”ni da wancan mara kamun kance.Zuciyar ta tabuga Dammm…Kasham wato kwana biyu da bataji d’uriyar taba ta zaci ta hak’urane kamar yadda taita zuwar mata kwanakin baya. Inna dai hakuri take bata tunda maigayyar yace baya so, zuwan ta nak’arshe da Inna tafad’i haka yar dariya kawai tayi tamata sallama tatafi .To yau kuma kwatsam ba zato sai gashi tadawo.

Kasham daga waje tace”Mama kice yabarni in shigo dan ba wajanshi shi kad’ai nazo ba har dake,idan kuma ba haka ba zan mishi abinda har abadan duniya bazai manta dani ba.Wata jijiya tafito rad’am agoshin shi kamar shatin bulala”ni kuma sai dai baki k’araso wajan nan ba amma wallahi sai na 6allaki”ke! Yafad’a a tsawace idan kin fasamin abinda bazan mantaba har abadan duniya ke ba…Inna tatareshi”Kai Julaibib dakata! Inna wallahi…tad’aga mishi hannu na dai ce ya isako?Yasunkwui da kai..”haba Julaibib idan rai ya6aci bai kamata hankali ya gushe ba,wai kamanta da sharrin mace har yafi na shaid’an kaifi?.Bai sake magana yasa kai yafita.

Kasham tashigo zauran suna gaisawa,Inna tabita da kallan tausayi”Iska na wahalar da me kayan kara.Takai gwiwoyinta k’asa tahad’a tafukan hannayenta alamar magiya idanunta sun ciko da k’wallah “Mama ki taimakeni mana”.

Inna tajijjiga kai”Zanso k’warai Julaibib ya aureki ko dan matsananciyar k’aunar dakike mishi,kuma ya tsamoki daga duhu zuwa haske amma hak’ata bata tadda ruwaba,to kema me zai sa bazaki hak’uraba? Sharrr…hawayen masu d’umi suka zubo a kyakkyawar fuskarta “saboda ina san shi Mama,Julaibib d’an kine na san zaiji maganarki,idan kikace dole ya aureni ai bazai k’i miki biyayya ba.Inna tadafa kafad’arta “Kasham kenan, kasancewar Julaibib d’a na ne ba yana nufin in tilas tashi yin abinda baya so bane,Julaibib yana da hakki akaina, kamar yadda nake da hakki akanshi,shi aure ba abin wasa bane,zaman aure kuma ana yin shine bana wucin gadi ba,a ah zaman din din din ne da ba a san rabuwa sai dai idan k’addarar hakan ta kasance ba yadda za ayi,kinga shi yasa ma ake so mutum yaza6i abokin rayuwar daya kwanta mishi arai, kowa yanajin k’auna da soyayyar d’an uwanshi da gasken-gaske,tayadda idan an samu sa6ani za ayi fad’a, idan an huce za ana juna uzuri,za a yafema juna, amma idan d’aya a dole yake zaune da d’aya to abu kad’an d’in da bai ta ka kara ya karya ba sai rigima ta 6alle wanda daga nan auran zai lalace an rabu, to ina amfanin 6ata goma biyar bata gyaruba?

Suna cikin haka saiga Alhaji Abdullahi yashigo shima da nasiha yabita me ratsa jiki.Tagyad’a kai”Eh tabbas duk abinda suka fad’a gaskiyace wacce daga k’inta sai 6ata. To amma fa ita har kwannan gobe tana san d’an Sarai bata kuma cire rai da auran shiba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button