GWAJIN DAFI COMPLETENOVELS

GWAJIN DAFI COMPLETE

GWAJIN DAFI COMPLETE HAUSA NOVEL

Sudaida…

Yakirata.Sai tamishi kunnan uwar shegu.Ke Sudaida ba kiranki nake yiba? Hajiya tasa baki”yau na ji yarinya ba dake yake yiba?Shiruma amsace. Hajiya tashiga tafa hannaye da sallallami.Yad’aga mata hannu”kyaleta Hajiya na jaki kawai zata sha.Eh gwamma haka tunda abin nata tsiyane d’inkin ludayi.Yace”ke Asma’u d’auko min bulalan can.Tana jin haka tafara”Ihu sai tajawo k’atan bargon Hajiya ta duk’unk’une aciki.Yayi murmushi “k’aramar mara kunya kawai,fito a cikin bargon kika yadda zan miki walmukalifatu “wallahi bazan fito ba.Yama Hajiya sallama sai bayan sallar Isha’i zai dawo.

Suna hirarsu da Inna tasako mishi maganar a’isha.Yasunkwui da kai tad’anyi murmushi dan ta san halinshi indai yayi haka to zaiyi wuya yayi magana.Kaga kwantar da hankalin ka niba dole zan maka ba,munyi magana ta fahimta da Musaddiq nima banga aibun taba shawara kawai nake ba ka, kanemi auran ta Insha-ALLAH ba kome sai alheri amma fa karka takura kanka idan ba ka so,dan aure ba abin wasa bane zamane da ake fatar yinshi har k’arshen numfashi.Yad’an shafa kwantaccen bak’in gashin kanshi sannan yad’ago cikin natsuwa ya kalleta “nagode Inna ALLAH yak’ara girma na kar6i shawararki da hannu biyu.Tayi murmushin jin dad’i “Ubangiji yamaka albarka ya taimaki rayuwarka. Amin Innarmu.

Wannan makon ya so zuwa wajan a’isha to amma bai samu sarari ba saboda sun gama TP(Teaching Practice)sun koma makaranta. Sai bayan makonni biyu sannan yasamu yashirya ranar juma’a cikin shigarshi ta fararan kaya kanshi da farar hula zita.Yana shiga lungun gidan yahango ya’yan gidan maza suna wasan Hockey.

Nasir abokin Abdul yana hangoshi yak’arasa wajanshi yana dariya yace “Kawu” kamar yadda yaji Abdul yana fad’a “yau kaine a k’ofar gidanmu? Ko kazo gaishe da Mamanmu ne?Yagyad’a kai”eh nazo gaisheta ne amma ba shiga zanyi ba ka gaisheta zamuzo da Musaddiq na musamman mu gaisheta.Yayi tsallan murna”to zan fad’a mata.Aisha tana ciki? Julaibib ya tambayeshi.Eh tana ciki inkira maka itane?Yagyad’a kai. Nasir yashige gida da gudunshi yana k’wala kiran sunanta.

Tayi mamaki tare da k’aryata Nasir.Nasir yafara rantse-rantse da gaske ne yana k’ofar gida.Tarik’o hannunshi “To muje ai ba a k’arya kusa da gida,amma na rantse da ALLAH idan ba shi bane?Tayi kwafa wallahi ka san sauran”Eh na yadda.Kanshi a k’asa kamar yana k’irga tsakuwan da suke yashe a wajan.Sai tasaki hannun Nasir da yake mata dariya ai dama na fad’a miki,yajuya wajan wasansu.

Yaya Julaibib…

Tafurta sunan kamar tana cikin shakkar shi d’inne ko wani me kama dashine?Yad’ago yad’an kalleta”na’am a’isha… Wani murmushi ya su6uce mata “ALLAH da gaske kaine a k’ofar gidanmu? Lallai yau farar rana ce me kyakkyawar suna “Juma’a.A mutunce ta gaishe shi,sai tayi shiru dan bata san abinda yakawo shiba.Shima shirun yayi na wucewar wasu dak’ik’u.Yad’an sake kallanta “na zo gaishe kine,inafatar banyi laifi ba?Tagirgiza kai”wani irin laifi? Gaskiya nagode da wannan ziyara ALLAH yabar zumunci. Ina Yaya Musaddiq? Ya tafi Kaduna.Hirar tasu jefi-jefi,bai wani dad’e ba yamata sallama yatafi.

Tabi bayanshi da kallo har yasha kwanar lungunsu ya bace ma ganinta tana tsaye a wajan cikin mamakin ganinshi a k’ofar gidan su,kuma wai wajen ta yazo dan sada zumunci, tasake juya kwalban turaren arabian perfume d’in daya bata,tabud’e tashaki k’amshin me wani irin dad’i,bata zata za suyi magana irin na yau ba,dan sunsha had’uwa ta gaisheshi amma sama-sama yake amsawa.Ashe dai Sudaida gaskiya take fad’a mata,Yaya Julaibib fa yana da matuk’ar kirki,shi kawai baya san a dameshine,kuma baya san magana da yawa. Tajuya zuwa cikin gida ba tare data kawo kome a zuciyarta game da zuwan shiba.

Bayan Musaddiq yadawo suka tattauna. Musaddiq yakad’a kai”gaskiya da ka sani kafad’a mata dalilin zuwanka”ai da zafi-zafi a kan daki k’arfe.Yagyad’a kai na fahimceka nagode yamik’a mishi hannu sukayi musafaha.

Ranar juma’a data zagayo yaso kwarai yaje wajan a’isha d’an yafad’a mata kome,to amma hakan shi bai tadda ruwa ba” dan sun fara jarabawa me zafin gaske,ba wanda yakoma gida dan itace jarabawarsu tak’arshe a College Of Education Gidan-Waya,sai kuma a zauna zaman girbe abinda aka shuka.ALLAH yaba me rabo sa a.

Lidiya tabita da kallo ita da d’akin, dan ta had’a k’aramin hazo ne da hayak’in taban da take ta zuk’a, takalli Ash-tray d’in da take karkad’e tokar guntayen taban data zuk’e,sai tazaro idanu da mad’aukakin mamaki,”Eh ta san Kasham tana shan taba amma sai ran ta yayi mugun 6aci,kuma bai wuce tasha kara uku ba,amma yau bata san ko kara nawa bane,tamatsa jikin taga tad’aga labulan tare da bud’e gilasan,hayak’in da gauraye d’akin yafara raguwa.

Kasham…

Lidiya takirata,tad’ago tana kallan ta manyan idanunta masu maik’o sun kad’a jawaur fuskarta har ta kumbura saboda kukan data sha bana wasa bane.

“Inzayadami Kasham?(Kaham me yafaru)

Shar…shar…wasu hawaye masu d’umi suka fara sintiri a kyakkyawar fuskarta”Kasham…dasauri ta d’aga ma Lidiya hannu “Don’t dusturb me!

Lidiya tagyad’a kai,tarungume hannayenta a k’irji tana kallanta,Tabud’e dirowa tana dube-dubenta “oh no dammed it”ta dunk’ule hannu ta naushi iska,da alama bata ga abinda take nema ba,takoma ta zauna tasake kunna taba, tabi taban da kallo da tunanin yadda karan zai kare a zuk’a d’aya,takai baki tamata wata irin zuk’a data kusa tafiya da numfashin ta,nan take kuma tari ya sark’afeta.

Tari tadinga yi kamar na shika, abin har yaba Lidiya tsoro ta kamo ta suka fito waje dan tasha iska. K’irjinta yana mata wani irin suya,mak’ogwaranta ya bushe k’amas kamar miyau bai ta6a bi ta wajan ba. Tad’ago a galabaice takalli Lidiya” ruuwa.Lidiya tagyad’a kai”o barin siyo miki,tana k’ok’arin jinginar da ita ajikin bango dan ta fara wata irin shakuwa abinda yadad’a rikitar da Lidiya kenan.

Hey…please come and help meee…!!!

Yadda akayi furucin cikin yanayin tashin hankali da tsoro yasashi waiwayawa inda yajiyo sautin. Tasake yafito shi da hannu… Tabbasss ko su wanene wad’ancan taimako suke nema sai yatafi wajen.Bai gane Kasham da Lidiya bane sai da yakusa k’arasawa inda suke yaji Lidiya nafad’in ban san me yashiga kwakwalwarki da zaki karar da karan taba a zuk’a d”aya ba, gashi nan za kije ki kashe kanki abanza…wani irin abu yaji da yabi ilahirin jiki da zuciyarshi”Kasham kwance wanwar a k’asa,farin wandan legging d’inta yayi dabbare-dabbare da k’asa…

Dan ALLAH ka taimake mu karta mutu,har lokacin tana dafe da k’irji tana wani irin numfashi,gefe da gefen fuskarta busassun hawayen wahala ne,idanunta suna rufewa da bud’ewa bak’i ciki yana 6acewa.

K’amshin arabian perfume d’in data shak’a yasa tad’ago dak’yar takalleshi…sai tamik’a mishi hannunta na dama.Tausayinta yakamashi dan tana cikin wani irin mawuyacin hali,wallahi mutum ba a bakin kome yake ba”Ubangiji????kamana kyakkyawan k’arshe.d’azu- d’azun nan yahango su,da yan course d’insu sunci kwalliya mazansu da matansu suna ta hotuna suna hayaniyarsu ta dandazon d’alibai.

Sai da ya durk’usa sannan ya tabbatar lallai tabar tasha dan gaba d’aya warin ta takeyi”me zan baki ne?Dak’yar tayi furucin”ru.rr… Ruwa…yabud’e ragowan ruwan swan d’in daya ke hannunshi.Ya waiwaya inda Lidiya take durk’ushe dan ta taimaka mata ta tashi, amma bai ganta ba.Sai kawai yad’agata ta jingina da bango, yamik’a mata ruwan.Saida tashanye shi duka sannan ta sauke gwauran numfash.”Sannu…Yace mata da yana yinshi na natsuwa”Kwallah suka cika idanunta,inama inama ace sunyi aure ne yake bata wannan kulawar?Bata ta6a zatan d’ansarai zai taimaketa idan ya ganta a mawuyacin yanayi ba,saboda halin-ko-inkulan da yake nuna mata.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button