
Dak’yar Kantiok ya ceceni bayan ya samu nashi rabon,suka haushi da zagi ai ba haka suka shirya ba dan me zai 6ata musu shiri?Yana hawaye yake basu hak’uri,dak’yar suka hak’ura suna cigaba da zagina idan ban daina zuwa inda suke ba sai sun kasheni tunda sun riga sun yafeni,sun barma musulmai to inje in k’arata can dai gasu gada zomo ya ji kid’an farauta.
Kantiok shi yakaini asibiti kwanana uku nad’anji sauk’i nace mishi ni zan tafi yadinga bani hak’uri wai ba laifinshi bane,ba yadda zaiyi ne “Naka na kane ko ya cinyeka bazai tauna k’ashin ba,nace mishi ba kome,nabashi complementary card d’ina,dama na zo in fad’a musu na yi sabon gida,wanda muka tashi a ciki na ba wani malami halak-malak acigaba da koyar da karatun alqur’ani da sauran littafan addini ina fatar ya zamar min sadakatul-jariya bayan numfashina ya k’are a doran duniya.
Yakar6a yana tayani murna da kuma bani tabbacin duk lokacin daya samu dama zai kawo min ziyara bazai bari Dinatu tasan sabon gidan na ba,namishi ihsani kamar yadda nasaba mishi mukayi bankwana.Sai dai har yau d’in nan bai zoba,amma lokaci zuwa lokaci muna magana dashi tawaya daga baya kuma na daina jinshi ko na kira lambar ta shi ba ta shiga,amma yanzu Insha-ALLAH za muje gaba d’ayanmu.
“Uncle to ya akayi ka musulunta? Yayi yar dariya”shekarun dayawa Sumayya,ina secondary aka kawo mana yan bautar k’asa (corpers) anan na had’u da Corper Muhammad Aminu,shi yake koya mana lissafi (Mathematics) kin san ko wani malami yana san d’alibin daya ke gane darasin shi,to haka abin yakasance tsakani na da shi,har mukayi sabo na ban mamaki har aikena yakeyi wasu lokutan in siyo mishi kayayyakin buk’ata na yau da kullum idan baya jin zuwa cikin gari,sai washe gari in taho mishi dasu.
Har Staff-Quarter ina binshi idan yana da abun bani naci ko nasha yaba ni,idan babu muyi hira,wasu lokutan kuma yak’ara min haske akan lissafi.Yakan dafa kafad’ata yayi murmushi “Shedrak kwakwalwarka tana ja sosai akan lissafi,kaje ka karanci Accounting nan gaba kazama Accountant General Of The Federation. “Malam bani dame tsaya min inyi karatu iyayena sun mutu.Yayi murmushi dan Iyayenka sun mutu ba shine zai dakatar dakai daga san abinda kake san zama a rayuwa ba,kai namiji ne gwagwarmaya da rayuwar za kayi”babu maraya sai rago”zan taimake ka kayi karatu idan ka gama secondary ka kawo min takaddun ka zan samo maka addimision a jami’ar Ahmadu Bello(ABU)ga tallafin karatu da za a dinga ba ka,kuma ai sana’a zaka fara yi sai kaga kome yana tafiya.
Corper Muhammad Aminu me sauk’in kaine da bai d’auki rayuwar duniya kayan gabas me k’amshin turaren d’an goma ba, a hankali dabi’un shi suka fara burgeni banyi aune ba sai kawai najini rannan ina karanta”Innas safa wal marwata min sha’a’irillah.Ni ban san kome ye ba amma nasan a irin karatun dayake yawan sawa ne,dama su bismillahi na iya saboda indai zaici abinci ko abinsha sai yafad’a dan wasu lokutan ma yana zubawa a faranti d’aya yace muci,tun ina jin nauyi da kunya har nasaba.
Gab da zasu tafi sun gama hidimar k’asa nasame shi a d’aki yana karatun Qur’an sai da yakai aya,sannan nazauna ina gaisheshi dan ranar bai shigo makaranta ba”Malam yau baka shigo ba.Yagyad’a kai “Bana jin dad’i,ban dad’e da dawowa daga asibiti ba”Yadai? Yatambaye ni. Nad’anyi murmushi”ni dai malam ina sha’awar addininka sai dai baza a barni a gida ba.Yamik’e zaune daga kwanciyar da yayi yana fad’in Shedrak kai namiji ne,ka kuma fara mallakar hankalin kanka dan haka kanada damar yin musulunci tunda shi kake so.Da wannan nasamu k’warin gwiwa.
Ranar da zasu yatafi nasha kuka shi ya rarrasheni”haba Accountant General Of The Federation wannan ba girman ka bane,share hawayenka maza basa kukan hawaye,wannan ai d’abi’ar yarane.Da haka mukayi bankwana. Direbansu yaja motar ni da sauran dalibai dawasu daga cikin Malamanmu muka d’aga hannu muna musu adabo????har motar tayi nisa ta 6acema ganinmu.”We may or may not see each other again.
Gaba d’aya sai makarantar ta gundireni kamar akan k’aya nake,a dadddafe nak’arasa.Muna gamawa nafara zuwa kasuwa, dako nake yi dan bani da kud’in da zan yi sana’a, nasha wahala amma na tara kud’i masu yawan danake ganin intayi ruwa rijiya idan bata yiba Masai,sannan natara yan uwanmu nafad’a musu k’udiri na nasan zama musulmi.Sai sukayi tsalle suka dire ALLAH yakashe su ban isaba, bazan yiba meye yata6i kwakwalwata haka?Nima naja tunga nakafe sai nayi sallah.Da suka rasa yadda za za suyi dani sai suka dinga zagina suna fad’in sun yafeni acikin zuri’a da jinsinsu na Bajju,har abadan duniya basu ba ni,ban bi takan suba na d’auki jakata sai cikin gari.
Agidan Liman tsoho anan na zama cikakken musulmi na za6i sunan Hafiz nacigaba da harkokina da musulmai,ina kuma zuwa kasuwa ina yin dako dan incigaba da rufa ma kaina asiri duk da kome ana bani amma ban yadda na zama cima zaune ba.
Rannan kamar wasa ina gwada lambar Corper Muhammad daya bani sai kawai naji ta shiga dan ban ta6a samun shiba sai ranar.Yad’aga da sallama nima ina murmushin jin dad’i dan nasan ma’anar sallamar dakuma muhimman cinta a musulunci”Malam ina wuni. Yad’anyi Jimmm…nawuce war wasu dak’ik’u cikin tunanin a ina yasan wannan muryar? Zuwa can naji ya amsa tare da fad’in “I’m I talking with the Accountant General of the Federation?Na kyalkyale da dariya ina gyada kai dan sunan fa yana sa ina jin kaina a duniyar wata”Yes Malam you’re…mukayi dariya.Bayan mun gaisa nake fad’a mishi na gwada layin shi sau shurin masak’i ba ta shiga.Yace matsalar network d’in k’auyen kune,kuma ai laifin kane kadaure kawai Accountant kasamar muku na’urar sadarwa me k’arfin zango…nayi dariya kawai dan na san zolayata yake yi.
Nafad’a mishi kome.Yaji dad’i sosai yadinga ambaton ALLAH cikin shauk’in murna,tundaga ranar sai muke yawan yin waya danma wasu lokutan ni ina samun tangard’an sadarwa sai dai shi yakirani,muna haka ALLAH yama Liman tsoho rasuwa.Iyalinshi basu kore niba amma sai naji gidan ba dad’i, rannan muna waya sai na fad’a mishi damuwa ta yace ba kome inzo Kaduna insa meshi,aiko washegari dasassafe nayi sallama da mutan gidan Liman tsoho nad’auki hanyar KD.
Malam Muhammad yana aiki da ma’aikatar Ilimi ta jahar Kaduna(Ministry of Education)Ina zuwa yad’orani akan kasuwanci dan ya tambayeni zan tafi jami’a karatun ne? Nace mishi a ah nafi san kasuwanci d’an tunda nafara dako a Zonkwa naji dad’in kudi,yasani a makarantar addini,da daddare ma ba barni na zauna ba,ina makarantar Islamiyya ta maza,ina karatu ina sana’a, k’ank’anin lokaci kuma ALLAH yasama kasuwan cin nawa albarka,wallahi duk abinda nata6a sai yazama bud’i daga Indallahi.
Shekaru na biyu a Kaduna muka had’u da wata Atika muna soyayya har an kai kud’in aure da sadaki amma Iyayanta suka dawo da shi wai su baza su ba tubabbe auran yar su da a ka haifeta musulma iyaye da kakannin kakanniba,Ina ai wannan ganganci ne zagin uba ranar sallah.
Ran Malam Muhammad in yayi dubu ya 6aci yadinga fad’a wannan ma ai jahilcine to ko musuluncima ai da tubabbun yafara yacigaba da bunk’asa har zagaye ko ina lungu da sak’o nafad’in duniya gaba d’ayanta.
A ranar bayan munyi sallar la’asar a masallacin unguwarmu yatsaida mutane dan su shaida.Yad’aura min aure da yarshi mace guda d’aya da ALLAH yabashi daga cikin Ya’ya maza guda bakwai Ummulkhair me kimanin shekara goma sha uku dan lokacin ajinta hud’u a secondary.Yakalli Sumayya yana murmushi kin san abinda yace min? Tagirgiza kai.Bayan an kaita gidana yadafa kafad’ata “Hafiz ga Ummulkhairi nan kaji tsoron ALLAH karik’e ta da amana,Idan tayi ba dai-dai ba ka nuna mata kuskurenta nan take,ka kuma muna mata yadda za tayi dai-dai,shi icce tun yana d’anye ake tank’warashi…Kome daza ka d’orata akai to a yau d’innan za ka fara k’ok’arin gina matashi a cikin zuciyarta,ko ba ta so to kai kajajirce karka karaya Insha-ALLAH sai kayi nasara.Ubangiji ya albarkaci auranku…abinda yafad’a min kenan yajuya yayi tafiyarshi. Sumayya tajijjiga kai”Malam Muhammad Aminu yacika jarumin maza Ubangijinmu kasa ka mishi da mafificin sakamakon ka.Amin,Amin Sumayya.