HALIN GIRMA COMPLETE HAUSA NOVEL

HALIN GIRMA 14

 Halin Girma    14

_*Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK????????*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK????????*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK????????_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK????????_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

_________________________

*_MACE SAI DA GYARA_*????????????????

_GYARAN MA NA KAMFANIN TURAREN:_

    *YERWA INCENSE AND MORE*

*Ƴar uwa ta hanyar gyara ne kawai zaki cigaba da amsa sunanki mace hamshaƙiya a wajen miji ba tare da ya ga kin tsufa masa ba.*

_Maza garzayo ki gyara jikinki da kayan ƙawatattu kuma nagartattu irin namu na gida da suka sami haɗi na musamman da babu cutarwa a ciki. hadin bornu/chadian na kamfanin turaren YERWA INCENSE AND MORE_

*_Muna da haɗin_*

_Turaren wuta kala kala na gidah_

_khumrahs_

_Kullaccham_

_Turaren wanka_

_Turaren Kaya_

_Turaren wanki_

_turaren mopping_

_Dukkanil al’ajab (Turaren tsugunno na Matan aure kad’ai)_

_khumratul al’ajab (khumrah ta jiki ta matan aure_

_Muna Gyaran jiki_ 

_Na amare_ 

_Da masu jego_

_Da sabulai masu gyara fata_

_Turaren tsugunno_

_zumar goran tula_

_Scented hair cream and spray (man kamshin gashi da gyara gashi_

_Akwaisu kujeran tsugunno

_Dilke and halwa set_

_Burners da igniters da tong_

_turaren fesawa dana ruwa._

_wardrobe balls_

_scented pebbles_

_cotton wooly oudi incense_

_kabbasas_

_Da sauran kayayyaki da yawa da bamu ambata ba_

_Akwai ragi na musanman ga yan zafafa fans❤️_

_Muna bada sari, Ko sayi ‘dai ‘dai akan farashi mai sauƙi da rahusa. Ga mai buƙata sai ya nememu tanan ????????_*

_EMAIL:yerwaincenseandmore@gmail.com ko INSTAGRAM PAGE d’inmu:yerwaincense_and_more dama nambR mu:08095215215_

_MUNA TURAWA KAYAN MU KO’INA A FADIN NIJERIYA DAMA KASASHEN KETARE.

100% TESTED AND TRUSTED_

••••••••••

*****

Azahar sosai ya tashi, ya mike yana salati, daga curtains din dakin yayi yana mamakin tsawon lokacin da ya dauka yana baccin, wayar sa dake saman gadon ya dawo ya dauka ya bud’e ta, misscalls ya gani ya duba sannan ya ajiye ya fito zuwa falo in da yatar da abincin sa a jere cikin manyan warmers sai kuma wani dan basket da aka rufe shi da jan kyalle me kyau dake dauke da hoton heart, matsawa yayi gabansa yana kallo,

“Menene wannan?” Yayi maganar yana rik’e kugun sa da sauri wani bafade ya shigo, ya rissina yace

“Sako ne daga shashen Kilishi, inji gimbiya Laila.”

“Laila?” Ya furta cike da mamaki

“Yaushe ta zo?”

“Tun da safe, lokacin baka nan.”

“Dauke shi a kai sashen Ammi, ace ta ajiye.”

Sake dukawa yayi cikin girmamawa yace

“An gama ranka ya dade.”

Juyawa yayi ya koma ciki, yayi wanka sannan ya shirya yana tunanin dawowar Laila a irin wannan lokacin da yasan suna tsakiyar karatu ne. Fitowa yayi ya tsattsakuri abincin ya fita wajen ammi dan be samu ganin ta da safe ba.

A gabanta ya tarar da sakon nasa, ta bishi da kallo sannan ta kalli kwandon da yake na Kaba. Sai da ya zauna ya gaishe ta sannan ya saka aka miko masa basket din

“Ammi kinga ko? Menene ma’anar haka?”

“Ni kaina nayi mamaki, amma kuma kasan dama hakan zata faru idan har ta samu labarin auren ka.”

” Bana son wata matsala gaskiya, zan aika da sako wajen Kilishin dan ba zan dauki rainin hankali ba.”

” Ka rabu dasu, karka yarda su bata maka rai har kayi tunanin biye musu, ka cigaba da addu’a nima kuma ina tayaka mahaifin ka ma,.ba zasu taba samun nasarar abinda suke so ba.”

” Shikenan Ammi, dan Allah aje a kona basket din nan dan bana son ko ganin sa.”

” Shikenan, ka cigaba da walwalar ka karka yarda makiyinka ya gane weakness dinka.”

” In Sha Allah Ammi.”

” Allah yayi maka albarka.”

” Amin.” Ya amsa yana jin tamkar dawowar Laila akwai wani babban dalili

” Yawwa na kira Fatima akan lefen ka, zata hada komai in sha Allah, idan yaso sai su tafi ita da kai da wata dai cikin su, Takawa ma yace shi zaiyi komai, amma duk da haka Fulani tace yayi nasa itama zatayi nata mu ma nan sai muyi namu.”

“Wayyo ni dan gata.” Yace yana murmushi

“Ammi gatan kar yayi min yawa ai.”

“Ba zai ba, Allah yasa ayi damu kawai, amma dole sirikata taga gata.”

“Uhm.. Allah sa idan tazo karta kwace min wajena.”

” Dole ne ai, kasan dai yadda nake son ya mace ko?”

” Shikenan sunana sorry wallahi.”

Dariya Ammi ta saka

” Aikam ka shirya tun yanzu.”

” Shikenan, Muhammad kana ji? Kayi hakuri da duk abinda zaka gani.” 

Ya fad’a cikin yanayin kalar tausayi, dariya sosai ya bawa Ammi tayi sosai, kallon ta ya dinga yi cikin tsantsar son ta, yana son Ammi da duk wasu halayenta, babu abinda yake so irin yaga tana farin ciki sosai, hakan yake sashi jin zai iya komai dan ganin ya faranta mata, ya dawwamar da farin ciki a kan fsukar ta, hakan kuma ba zai yiwu ba sai dole yaki karbar muradin Bubu, dole ya hakura da mulkin ko da yana so, saboda farin cikin Ammin Sa!

***Satin Mama daya cif a Katsina, ranar da zasu dawo ranar Bashir ya iske su a chan da dalleliyar mota da sha tara ta arziki, murna wajen Mama da Zeenat ba’a magana aka dinga turashi gida gida na dangi dan aga irin mijin da zeenatun ta samo, aikuwa nan da nan magana ta karade ko ina cikin family din Maman, anan wasu da yawa suka samu labarin bikin Zeenat din wanda aka saka wata daya kachal bayan Bashir din ya tabbatar musu da zaiyi komai basa bukatar komai hatta da kayan gida duk shi zai zuba, hakan ya sake fasawa Mama kai ta dinga hura hanci a lallai zeenatun ta ta dallo miji na kere sa’a, tausayi da farin cikin halin da ta tabbata Iman zata shiga idan har ta auri fakirin nan take, gashi dai su kam Allah yayi musu gam da katar dan yadda aka dinga maganar Bashir din a dangi kadai ya ishi Mama tutiya da alfahari.

   A motar ya kwaso su Zeenat na gaba gida na tashi cikin taken soyayya Mama da Marwan na baya har Kano, Zeenat ji take kamar tafi kowa sa’a a duniya dan da gaske take jin wani irin son Bashir din na ratsa ta.

   Sanda suka isa gida magriba tayi saboda basu taho da wuri ba yana faman zaga dangi, alwala aka kawo masa ruwa yayi, ya zauna Zeenat din ta shiga ta fito suka dasa sabuwar hira irin ta yaushe rabo. Cikin hirar ne yake fad’a mata lefe in sha Allah za’a kawo cikin upper week, zai sanar mata da ranar sai ta fadawa Mama, hakan yayi mata dadi har tana hasashen uban kayan da za’a kawo mata dan taga Bashir din me bajin ta ne sosai.

  Ranta fes ta koma ciki bayan ya tafi, ta labartawa Maman lokacin Matar Abba Musa ta shigo wajen Maman yi mata sannu da zuwa. 

“Haba ni nayi mamakin da aka ce manyan mutane ne suka zo neman aure gidan nan na tabbata dama wajen Zeenat ne, yarinya kakarki ta yanke saka wallahi.”

Tace tana dariya, murmushi mama tayi

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button