Hangen Dala 1HAUSA NOVEL

Hangen Dala 1

Mmn ummi dake bakin window din tana kallonsu ta saki labulen cikin tafasar zuciya,wato ta fuskanci wani dama dama yake da mmn amir,itace banza kenan?,fushinta banza farincikinta banza?,anya ko matar nan haka ta zauna?,sai wani sashe na zuciyarta ya gargadera,don tunda suke da mmn amir din nata taba ganin wani abu guda daya tattare da ita daya sata shakka ba,abu dayane tasan cewa tana da yawan azumi kamar ma bata damu da abinci ba,hakanan tana da yawan tashin dare harta dinga zargin ada wani abu take cikin daren,saita gane sallar dare ce.

Sai data zauna saman kujerar sannan ta qwalawa yaran nata kira da sunayensu daya bayan daya,usman ne ya soma shigowa
” gani umma”cikin dakinta ta nuna mas”shiga ka cire wadan nan kayan ka samu wasu cikin kayanka ka saka”dum yayi yana dubanta sannan kuma yace
“Amma umma,wajen daurin aure zamuje”
“Iyee,ni kake gayawa wajen daurin auren kishiyar uwarka zakaje?,to shiga kayi yadda nace maka tun ban tashi na zazzabga maka mari ba” hakanan yaron yashige ciki sum sum,ya sauya kayan yafito,zai fita ta tsaidashi ta nuna masa saman kujera
“Zauna nan” ta fada tana dubanshi,haka yakoma yazauna,yayi lakur saman kujerar har zuwa sanda usman yashigo.

Cikin murna yana nuna mata shaddar jikinsa
“Umma,kalli sababbin kayana zamuje unguwa mu dasu abba dasu ya amir”jawoshi tayi da sauri sannan tahau tube mishi kayan,saiya riqe rigar da hannunsa yana kallonta
“Nidai umma karki ciremin,karki batamin kwalliyata,mama ce ta sakamin unguwa zamuje”
“Unguwar ubanka ko?,maza ni kama min bakinka a nan” yaro da baisan hawa ba baisan sauka ba,ganin tacire kayan da gaske kuma tana niyyar sanya masa tsofaffi saiyahau kuka da ihu harda tsalle,haushi ya cikata,ta janyoshi tahau duka,tanajin mmn amir dake tsakar gida tana tambayarta lafiya amma tayi banza da ita tashiga takoma saman kujera tayi zamanta tana baiwa ummi da kukan usman ya tasheta nono.

Bai gaji ba yazauna dirshan yaci gaba da kukanshi,har bban amir yagama shiryawa,ya gaji dajin kukan saboda haka ya daga lebulen yashigo yana kallonta
“Me aka yiwa yaron nan ne wai?” Sai idanunsa ya fada kan ahmad dake zaune kan kujera yana rarraba idanu
“A’ah,kai kume me kake a zaune duka ‘yan uwanka sun shirya?,ina kayan naka?” Sai daya saci kallon uwar yaga ta maka masa harara sannan ya maida kallonshi ga uban,usman daya dakatar da kukan ganin shigowar uban shiya bashi amsa
“Abba umma taciremin sabbabin kayana” daga kai yayi ya dubeta,bai tanka mata ba yasanya kai cikin dakin ya debo kayan kayan yaran yadawo yasanya musu
“Karka fitarmin da yarana,babu inda zasu gayyar arna a idi” dai daya kada kansu tana rsaye a bayanshi tana yada magana sannan ya juyo yace
“Idan ‘ya’yankine saiki hanani zuwa dasu ai”
“Ai wallahi kaima kanka kasan na fika iko dasu ehe,kuma ba’a canzawa tuwo suna duk juyin da zamani zaiyi sunanshi tuwo” taci gaba da daga murya tana zazzaga ruwan masifa harya yaran zuwan ‘yar farfajiyar dake gidan wanda anan yake aje motarshi.

Surutun duka suka damu mmn amir,wanda itama kanta a quntace take,ga hayaniyar baqi tasoma jiyowa maza ‘yan daurin aure,wanda ta tabbatar ba za’a rasa mata masu shigowa ba,saita saki abinda take tabar tsakar gidan ta hada ruwa tayi shigarta wanka.

Tana bakin madubi tana kwalliya taji shigowar maqotansu su biyu,a gurguje ta gama shiryawar tafito ta samesu,suka gaisa sannan sukace sun shigone koda wani aiki
“Ai kuwa akwai,samira naketa jira ta iso,gasu innarma har yanzu basu qaraso ba” abinda za’a rarrage ta nuna musu,sannan tashiga taci gaba da shiryawa.

Duk da cikin jikinta amma tayi kyau,kwalliyar ta dace da ita,ba jimawa samira ta iso,ita da qanwar ummanta da qannenta biyu da yaransu,nan suka shiga cikin maqotan akaci gaba da aiki.

Ba’a jima ba innar jibril ta iso itama da qannenshi duka mata,da kanta mmn amir ta tarbesu,tayi musu duk wani abu daya dace sannan sukaci gaba da sabgarsu,kafin wani lokaci gidan yadan soma cika da tashin hayaniya,awa daya da wasu mintuna da zuwan innar hafsa ta iso ita da qannen maman ummi,saida suka soma tsayawa ga jama’ar tsakar gidan aka gaisa sannan suka nufi dakin mmn ummi,wanda tun dazun datashiga dakin ko leqe bata sake ba,kai kace babu dan adam cikin dakin.

Jiddace ta waiwayo ta dubi mmn amir
“Tabdi,wai dama mmn ummi na gidan nan?”
“Abinda zan tambaya kenan nima” innar jibril ta fada fuskarta cike da tsantsar mamaki,sai mmn amir ta rasa amsar da zata basu
“Eh…me yiwuwa ko bataji zuwanku bane”
“Wanne irin bataji zuwanmu ba?,awata nawa zaune a nan,sannan duka yaran ai suna tsakar gida,idanma bataji zuwana ba ai bazata rasa jin muryar daya daga cikinsu ba,ashe duk abinda ake fada kan yarinyar nan na rashin arziqin da take tunda jibril yatashi aure da gaskene,ban gasgata ba sai yau” sababi sosai innar take,mmn amir na tausarta
“Kiyi haquri inna ki mata uzuri,ba lallai taji ba” shine abinda taketa fada tana fatan zata sassauto,bata da abin cewar daya wuce haka,saboda shekarun baya iwar haka ita ake tsinewa ake zaga sanda maryam din ke gab da shigowa gidan,bata da wani katabus bata da abin cewa,babu abinda zatayi tayi fari a idanunsu,sai gashi yau da yake ance duniya juyi juyi wai kwado ya fada a ruwan zafi maryam dince abar zagi
“Jeki kiramin ita” innar tace da jidda,saurin dakatar da ita mmn amir tayi tace
“Bari nayo mata mata magana dakaina inna” saboda tana tsoron kada jiddan tashiga ta tunzurata su raba abun fada,abu yazo ya kwabe,don ita kanta yau ta kanta take,ba zata iya daukar kowanne tashin hankali ba.

Daga can dakin mmn ummi kuwa hafsa da jamila qanwarta ne suka sanyata tsakiya suna faman lallashi,yayin da taketa faman sharbar kuka duk sanda ta daga kai ta kalli agogo taga lokacin da aka sanya na daura auren harya gota,yanzu kenan abban amir din ya zama nasu su uku?
“Wallahi wannan abun da kikeyi bayi bane yaya,tun yanzu kin karaya gaba daya tun kafin anjima azo kawota?,baki ganin mmn amir ita saikace abun bai dameta ba?” Tabe baki hafsa tayi
“Uhmmm,kinga maryam,ki tashi ki shirya tun kafinma a gane a haka kike zaune”.

Sallamar mmn amirce ta sanyasu yin shuru,tashigo fuskarta sake tana duban mmn ummi
“hala bakiji zuwan inna ba?”
“Naji,me zanyi mata?,nafito taga na damu ko ban damu ba?,to ta Allah ba tata ba munafuka” sosai maganar ta baiwa mmn amir mamaki,a nata tunanin furfura ko bata tsohonka bace ka girmamata,jamila ma kama baki tayi,daurewa mmn amir tayi
“Amma dakin leqo kun gaisa,kin san idan ba leqowa kikayi ba zata yita qorafine”
“Tayita yi,uwata ce?” Kai mmn amir ta girgiza,sai taga tafiyarta yafi alkhairi akan ci gaba da tsaiwarta,don kada tsautsayi ya debi mmn ummintace zata aikata wani lafazi naba dai daiba a kanta.

Tabe baki hafsa tayi
“Kekam haryau baki da siyasa,tashi ki shirya din kije ku gaisa ki dawo,saime idan kinje?,gutsurarki zasuyi” da qyar suka lallabata tashirya din kana tafito,saidai duk wanda yakalli fuskarta yasan cewa babu walwala ko fara’a a fuskarta kona gamin gafara,haka ta dinga gaisawa da mutane daqyar harta isa dakin mmn amir.

A daddake tagaida innar ta amsa itama tana mata wani kallo
“Wato ke isassa ba’a isa kizo ki gaida mutane ba kenan sai an kiraki ko?”
“Banji shigowarku bane,inacan ina lallaba ummi tana rigima”
“To ai yayi kyau” daga haka shuru ya ratsa tsakani,minti biyar taqara ta miqe abinta tafice.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button