Hangen Dala 1

Da kadan kadan baqi ke zuwa wasu suyi Allah yasanya alkhairi su tafi,wasu kuma su zauna zaman wuni,ko sau daya mmn ummi bata sake leqowa ba tana cikin daki abinta,duk meson su gaisa saidai yashiga.
Daga can sashen rufaida kuwa lokacin da angon yashigo gaida surukai bayan an gama daura auren idanunta a kanshi,wani farinciki takeji yana ratsata,yau Allah ya cika mata burinta,kunyar ragaggiya ce ko sanda akazo daukan hotuna tsakanin amarya da ango,style take badawa kala kala,har wata kakarsu ta ankara,daga bisani ma tabar tsakar gidan tashige daki ta zauna.
Kusan duk hotunan da ake musu yaran saida suka shiga,usman da yake qarami yana hannunshi,tun bata lura ba harta lura,sai abun yasoma tsaye mata a wuya,data sake lura sosai saitaga hatta da shaddar jikinsu ma iri daya ce,qwafa taja can qasan ranta,wato bayan iyayensu suma akwai tasu qurar kenan?,zataji da kowa ta raya haka a ranta.
Saida azahar abbansu yasaukesu a gidan,innarshi kawai ya gaida yafice daga gidan,mmn amir na falon sanda yashigo,saita dauke ido kawai taqi kallonshi tana jin wani kishi na taso mata,ta tsiri hira da mmn ja’afar matar abokinsa,shima daya dubeta saiyaga hankalinta bai kanshi don haka ya juya da hanzari yafice.
Bangaren mmn ummi kuwa sanda yaran suka shigo ji tayi kaman ta kamasu ta gada da uban tayita duka,shaddar jikinsu ta dinga ganinta kamar daga wuta aka cirota,don haka ta korasu waje tace su bata waje.
*BAYAN AWA SHIDA*
Tsaye take cikin dakin tana shiryawa cikin atamfa,kayan kwalliyane baje a gabanta tana makeup,zahara dake zaube tana miqo mata abubuwan da take buqata,dakin ya bade da qamshi kai kace barin turare akayi,ba abinda kakeji sai hira da shewarsu,a haka kakar rufaida hajiya kaka tashigo dakin.
Cikin mamaki take duban rufaida daketa zuba baki rai rai batama lura da shigowarta ba
“Ke aku,samu waje ki zauna” sai a sannan ta waiwayo,ta dakata daga saka dan kunnen da takeyi tace
“Kefa tsohuwarnan kin iya takura wlh” tafadi tana samun waje ta zauna kamar yadda hajita kaka ta buqata,saita itama tasamu waje tazauna tana dubanta
“Duk fitsarar da kike da rawar qafar da kike ina lura dake,to bari na gaya miki gaskiya idanma uwarki bata gaya miki ba,wannan mu a wajenmu abun kunyane aga amarya tana haka,don haka ki kama kanki karkice zaki shiga cikin matansa kina musu wannan rawar kan,idan kikai hakan kai tsaye za’ace ba daga gidan tarbiyya kika fito ba” dariya rufaida ta bushe da ita ita da sauran qawayenta na makaranta dake dakin masu irin tunaninta
“To hajiya yanzu so kike naje nayi ta sussunne kai ina abu kamar banje makaranta ba ko kuwa yaya?,nifa auren soyayya mukayi da mijina,kuma babu wadda zanwa biyayya tunda yadda suke matanshi haka nake,haba hajiya nafa fisu da komai,idan ba’a bini ba ai kuwa bi ba’ace nabi mutum ba” ta fada tana juya idanu,sai hajiya ta kama baki ciki mamaki
“Ni tarasulu,ke rufaida akul ki shiga hankalinki,mu idan muka aurarwa mace miji kunyarta mukeji,mukan jima bama iyama hada idanu da ita saboda abune me nauyi da girma,hakanan abokiyar zamana harta rasu ke har yanzu da nake miki maganar nan ban iya fadar sunanta yaya nake ce mata,haka itama bata taba batamin raiba ko sau daya,suna na kuwa nima ban tabaji ta fada ba,saida nayi haihuwar fari take kirana da sunan dana” sake kwashewa tayi da dariya har suna tafawa da zahra
“In gaya miki gaskiya hajiya?,wallahi bazan iya wannan rayuwar ba,banma tanadeta ba ko a mafarki,kishiyar zan shiga ina kwantarwa dakai ina yiwa biyayya?,bayan nasan cewa na fita da komai?,ai tsakanina da ita kawai shine nasaita mata hanya ta bani waje na sarara nida mijina,matan nashi gidadawa kada ma uwar gidan taji labari” da yatsa hajja ta nunata
“Ke wallahi ki kiyayi kanki,mu dukka din nan da kukewa kallon gidadawa da haka muka fiku iya riqe miji,me bokon taku ta tsinana muku banda tabarbarewa lalacewa da rashin iya zaman aure?,iyee ki gayamin?” Shuru dukka sukayi saidai rufaida tasan halin mutuniyarta,saita hau lallabata
“Aikin banza aikin wofi,duk bokon da kuke haryau sunqi karanta muku iya zama da miji da kishiya lafiya lau,kunawa aure kallon abu mai sauqi,bayan bakusan cewa *HANGEN DALA BA SHIGA BIRNI BA* ne”
“Kiyi haquri hajja nima tsokanarki kawai nake,zauna ki gayamin ina saurarenki” ta fada don kada hajjan ta ballo mata ruwa,ita ta haifi babanta tasan kuwa yanzu idan zance yashiga kunnensa sai ya bata mata ranta,fur hajjan taqi zama tace taje tagwada bokon tata.
Dariya sosai ta dingayi suna tayata sanda hajiyan tafita,haka tajuya taci gaba da diban kwalliyarta.
Lullube amarya rufaida take cikin shigar atamfa da yalwataccen mayafi kamar yadda akasan kowacce amarya,tana riqe hannun qanwar mamanta wadda rafito da ita daga dakin mamarta zuwa dakin dakin da dangin ubanta suke don yi mata fada,qasa qasa tace da zahra dake kusa da ita
“Ke nifa na gaji da wannan qabli da ba’adin nasu,wai meye baka sani bane a auren nan da aketa damunka?,kwanciyar aurece kawai fa ta rage,kosu wlh saina koya musu wani abun,amma sun dameka da zantattuka wani sai haquri sai haquri suke cewa kamar ance musu anmin mutuwa” dariya zahra ta kwashe da ita cikin qunshe bakinta kana tace
“Salon bata lokacine kawai da al’adar da suka daukaketa,kedai kawai ki bisu a haka suyi su gama mu qara wuta” da wannan zancan aka qarasa dakin,sun mata nasiha daidai gwargwado,wanda wajen rufaida kallonta take a matsayin ita da babu duk daya,ta kunnen data shiga haka take fita ta dayan,har suka gama aka tattaro aka fito da ita don danganata da gidanta.????️????️????️????️ *HANGEN DALA*????️????️????️????️
_Ba shiga birni ba_
©️®️ *Safiyya Abdullahi Musa Huguma*
*Haske Writers asso*????
*BABI NA BAKWAI*
“Allah ya kawo mu gidan gimbiya rufaida,lokaci yayi,gamu gidan rufaida,mata mai cikakken iko a gidan jibrila” wata zabiya dake cikin tawagar amarya taketa faman fada tana sake nanawatawa,gami da hadawa da guda mai shiga tsakar ka,su kansu wasu daga cikin ‘yan uwan amaryan basusan wace ita ba,suna dai biye ne,har suka wuce farfajiyar gidan zuwa babban tsakar gidan,wanda ke dauke da varender da dakuna manya a jere.
“Allahumma la sahla illa ma ja’altuhu sahla,wa’anta taj’alil hazna iza shi’ita sahla” mmn amir take maimaitawa sanda takejin wata faduwar gaba da fargaba na saukar mata
“Uhummm,sun iso kenan” daya daga cikin matan qannenta ta fada
“Da alama” samira ta fada tana dawowa kusa da mmn amir din,qoqarin kauda duk wani surutun masu shigowa da amaryar take daga kunnuwanra,da kauda duk wani furuci da zaya iya fitowa daga bakinsu.
“Na shiga uku,hafsa sun kawota,wallahi gasunan” mmn ummi ta fada tana dora hannuwanta saman ka,hawaye yana balle mata,da sauri hafsan ta sauke mata hannun tana cewa
“Haba don Allah mana maryam,ki nutsu,a haka kikeso su shigo su taddaki?,haba don Allah” hafsan ta fada tana sauke mata hannun data dora din aka,jamila tamiqo mata mayafinta tace ta yafa,don wala’alla suce zasu shigo da ita nan din.
“Ku fara shiga da ita dakin uwar gidan” yayar maman rufaida ta fada sanda taga suna yunqurin shiga da ita dakinta,wani takaici yacika rufaidan,taji kaman ta dakatar dasu,saidai ba yadda ta iya haka tanaji tana gani aka sauya akalarta zuwa dakin mmn amir.