Hangen Dala 1

A mutunce suka amshesu,sannan suka gabatar da itawa mmn amir din gamida danqa amanarta a hannunta kamar yadda al’ada ta tanada,cikin matuqar dakiya da nuna juriya mmn amir tace
“Toh,amana abune mai nauyi,amma duk da haka muna fata da addu’ar Allah S W T yabamu ikon riqewa,yashige mana gaba ya kauda fitina” dukka suka amsa da amin cikin yabawa da halayyar mmn amir din.
Ta cikin mayafin rufaida ke tabe baki sanda mmn amir din ke karanto addu’o’i suna amsawa,qaramin tsaki taja qasa qasa cikin ranta sannan ta furta
“Bagidajiya,kawai zata batawa mutane lokaci” sai data kammala suka shafa sannan suka miqe da ita suka fice zuwa dakin mmn ummi,har cikin zuciyarta taji sanyi na sauka sanda take shafa addu’ar,ta saki sassanyar ajiyar zuciya gami da sake maida kanta cikin sabgogi ta hanyar sallama da maqotanta wadanda suka soma haramar komawa gida ganin an kawo amarya.
Idanunta qir a kansu sanda suke shigowa dakin nata,baqiqqirin take ganinsu,kallon da take musu tamkar ganin abokan gaba ne a sansanin yaqi.
Wani irin tafasa zuciyarta take,kaman ta tashi ta koresu,amma dole tazauna tanaci gaba da dubansu,saboda maganar da jamila tayi mata tun kafin su shigo.
Yadda sukayi bayani dakin mmn amir haka sukayi mata,zuciya ta ciyota,taga zallar rainun wayonsu,ita za’a baiwa wani amanar kishiya?,duk yadda taso ta danne tayi shuru saita kasa
“Dacan baku bata tarbiyyar zaman gidan miji ba da bazata iya ba har sai kun bada amanarta?” Da mamaki suke kallonta,idanunta qyar akansu tana jiran wata ta tanka musu,ware idanu rufaida dake cikin mayafi take,inama daga ita sai ita tafadi wannan maganar,lallai wannan matar saita gane kurentq,dama tana sane da ita sarai,bata manta daduk wani cin fuska data mata ba kafin shigowarta gidan ,ta kuma ci alwashi ta lashi takobi saita rama,saita bada mata yaji a rayuwarta mai radadi
“Ikon Allah,to adai dinga haquri” yayar umman tata ta fada,sai duka suka miqe tare da rufaidan don barin dakin
“Da ba’a haquri ai da ba’a kai yawar haka ba,da bata shigo bama” ta fada ranta na mata zafi.
Dubanta jamila tayi bayan sun fice
“Gaskiya baki kyauta ba mmn ummi,abu na ‘yan mintina ki barsu suyi su gama su fita shine kika kasa shuru,nikam gida zan wuce” ta fada tana miqewa ta dauki jakarta ta rataya
“Madalla,Allah ya raka taki gona,tunda na taba qanwar umma uwarmu” bata tanka taba tafice a dakin,ta leqa dakin mmn amir da tuni baqinta suka yoye saura ‘yan qalilan suma daketa hada karonsu zasu wuce,sai qanwarta salima da zata kwana gidan donta tayata hidimar gobe ta gidan.
Zuwa awa daya gidan ya yoye babu kowa,hatta da amarya sai ita kadai,don qawayen nata duka angon yasa an kwashesu an maidasu gida,don yace bazaiyi wani siyan baki ba,saboda yana bala’in jin nauyi da kunyar mmn amir,bazai iya tsayawa yayita wannan yarintar ba da qawayen amarya ana jinsu,duk da hakan bai yiwa rufaida ba,amma haka ta haqura suka tafi suka barta.
Dukka yaran mmn amir ta sanyasu suka canza kayansu,salima ta gyara musu wajen da zasu kwanta tasaka su sukaje suka kwanta,hatta dasu usman basu kalli qofar dakin mamansu ba,don sunsan qarshen zancan wala’alla kafin bacci ya daukesu sai sunci na jaki.
Dai dai lokacin da amarya rufaida take kewaye dakinta tana dubawa,ba laifi komai yayi mata yadda takeso,duk da tasan cewa data yarda bbn amir din ya raba musu gida to dakin nata sai yafi haka,saidai sam ita bata da sha’awar wani raba gida,tafi sha’awar a hadesun yadda zataji dadin nuna musu cewa ruwa na sa’an kwando bane,wannan ma hakan ya mata.
Babban falo ne mai hade da bedroom,sai wajen dining wanda kusa dashi kuma qofar toilet ne,duk da ita kitchen taso a mata a wajen,duka sauran falukan matan nashima haka yake,gini ne mai kyau wanda yasha tiles da fentin mai kala biyu,kalar da kowacce cikinsu ita tazaba da kanta.
Tana zaune tun dazun inda take,ba inda ta motsa,jikinta gaba daya ya mata nauyi,ga wani ciwon dako ina na jikinta ke mata,hakanan zuciyarta sam babu wani sauran karsashi ko qwarin gwiwa tattare da ita.
A haka taji shigowar baban amir din gidan,tanason ta tashi tabar falon amma ta kasa,a haka harya shigo gidan,sai daya tabbatar ya kulle ko ina sannan yashigo tsakar gidan bakinsa dauke da sallama,shuru tsakar gidan yake,saidai a kacame yake,ko baqone kai zaka tabbatar cewa lallai anyi wani sha’anine cikin gidan.
Idanunsa kan qofar dakin rufaida,wanda yake tarwai da haske kamar yadda dakin mmn ummi yake,sabanin dakin mmn amir da nata hasken baikai nasu ba,da alama ta rage qwayayen dakin nata.
Kai tsaye dakin mmn amir din yanufa,ya yaye labulen bakinsa dauke da sallama,amsa masa tayi a sanyaye bayan ta daga kanta da niyyar kallonshi,saidai ta kasa,saboda wani abu daya takore mata wuya,hakanan taji cikinta yasake nauyi
“Sannu da zuwa” ta furta daqyar tana kuda kanta gefe,idanunshi a kanta yana karantarta ya amsa mata
“Kun yini lpy ya yaran duka?”
“Sunyi bacci” ta bashi amsa a taqaice,shuru daiya ratsa tsakaninsu,hakanan yadinga jin nauyinta,yana tuna wancan shekarun da suka shude a rana irib wannan,kusan hakan tayi masa,yaga zallar kishi da bacin rai a fuskarta amma tazabi yin shurun kamar wannan lokacin,duk sai yaji nauyin tashi yafita din,yana ganin kamar ya cutar da ita a rayuwa har sau biyu,cikin son nade tabarnar kunya yace
“Na tsammaci zuwa yanzu kin kwanta,don nasan kunsha kujiba kujiba ko”
“Yanzu nake shirin tashi” ta fada tana yunqurawa da qyar
“Yi a hankali” ya fada sanda tadan koma baya kamar xata zauna sai kuma ta sake miqewa,ledar hannnunshi yamiqa mata ganin tana niyyar shigewa uwar dakinta
“Babu wani abun da kuke da buqata?” Ya tambayeta yana kallon bayanta sanda take dab da shigewa dakin nata
“Babu komai” ta fada bayan ta dakata ba tare data waiwayo ba
“Haka akeso” sai yasake yin shuru na wasu sakanni sannan yace
“Halima…..don Allah ki kwanta kiyi baccinki sosai kodon abinda yake jikinki,karki sakawa ranki damuwa don Allah”kai ta jinjina tana qoqarin hadiye abinda ke taso mata sannan ta sanya kai cikin dakin.
Kusan sakan goma sannan ya taka ya juya yafice yana jin tausayinta sosai cikin ranshi,ta nuna dukkan wata jarumta da haquri,ba shakka haliman baiwa ce da Allah yayi masa na macen da ba kasafai ake samun irinsu ba,maryam kawai ta zame masa ishara.
Daga nan dakin mmn ummin yashiga,itama da sallamar yashiga,tana tsakar falon tana kai kawo goye da ummi a bayanta wanda ta jima dayin bacci,fuskarta kawai zaka kalla kasan bala’i da tashin hankalin da take ciki.
Dauke kanta tayi sanda taga shigowarsa,qirjinta yaci gaba da zafi,ko sallamar ma bata da lokacin amsa mishi
“an yini lpy” ya fada itama yana zama hannun kujera,banza tayi dashi,saima tasoma tattare kayan dake zaune d’ai d’ai tsakar falon kamar batasan Allah yayi ruwanshi ba,qoqarin danne bakinta take ta hana kanta ruga masa ashariyar daketa yawo saman harshenta,data gama saita wuce dakinta tarufe qofar tabarshi nan zaune.
Yasan cewa lallai anzo gabar da duk dauriyarki dole gazawarki ta bayyana,saboda haka baiyi qasa a gwiwa ba yanufi qofar dakin yasoma qwanqwasa mata
“Bude mana maryam”
“In bude inyi uwar meye?,jibril kafice min daga daki wallahil azim idan nafito ba zamu kwasheta da dadi ba,maciyin amana kawai,Allah dai yayimin sakayya” saita rushe da kuka sosai mai fidda sauti,kanshi kawai ya girgixa saiya koma da baya ya aje mata ledar ya juya yafice zuwa sashen rufaida.