Hangen Dala 1

Suna zaune yaran a nutse duka suna kallo cikin tsafta,ya tambayesu ina mmrsu,usman ne ya amsa mishi data tafi asibiti,saiya juya yana neman qarin bayani wajen salima,ta gaya masa cewa takira wayarshine taqi shiga,shuru yayi kana yasoma qoqarin fito da wayarshi daga aljihu yasoma kiranta,saidai wayar taqi shiga,maidata aljihu yayi yana rayawa cikin ranshi,kishinne yamotsa itama shi yasa taketa shakulaton bangaro da shi,saidai koma meye baiga laifinta ba sam,tayi namijin qoqarin da sai an tara mata dari ba’a samu wadda zatayi abinda tayi ba
“Kuzo muje ku gaida antynku” bbn amir ya fada sanda salima ta gaya masa kayan abincin yana kitchen.
Kowa yasan yaro da zumudi dason amarya,sai suka miqe kuwa dukkansu suka bishi,sai salima kawai tarage,ya soma biyawa ta kitchen ya diba abincin ya baiwa amir yadauka suka nufi dakin rufaidan.
Tana zaune sosai tana shaqar iska dai dai,jiran dawowarshi kawai take tana tsara yadda yau zata haramta kowa ganinsa da kuma walwala cikin gidan,sai taji sallamar yara,ta daga kai da sauri tana dubansu,take duk wata fara’ar dake fuskarta ta bace bat
“Meye hakan?” Take tambayar kanta cikin zuciyarta,zuciyarta na wani iri zafi ganinshi tare da tarkacen yaranshi duka.????️????️????️????️ *HANGEN DALA*????️????️????️????️
_Ba shiga birni ba_
©️®️ *Safiyya Abdullahi Musa Huguma*
Haske Writers asso ????
*BABI NA TAKWAS*
Amir ne ya qaraso ya dire tire din dake dauke da kayan abincin,ya duqa har qasa ya gaidata,ta bishi da wani kallo tana amsawa da qyar kamar wadda aka cusawa tsumma a baki,tana jin zuciyarta na mata daci,takaici ya cikata.
Duka yaran suka qaraso cikin falon suma,da daya da daya suka soma gaidata,daqyar take iya amsa gaisuwa daya tak,duka tana qare musu kallo a kaikaice,sai taga kowannensu yasamu waje ta zauna.
Dubanta ta maida kan bbn amir,tayi tsammanin zai musu magana su tafi,sai taga sabanin hakama shima wajen zama yake nema dauke da ummi a hannunshi,hakanan dukka hankalinsa yana kansu yana musu tambayoyi kan abinda ya faffaru jiya a gidan.
Dif tayi yana shaqar wani baqinciki da takaici,ummi tasoma daga mata hannu taba bangala mata dariya,amma saita dauke kai kamar bataga yarinyar ba,saida babanta ya kula ne yace
“Antynsu,so take ki dauketa fa,kinsan ummi dason yawo kuwa dason a dauketa” yaqi tayi tana qoqarin sakin fuskarta amma sam ta kasa,don bata saba da hakan ba tun asali,bata fiya iya biye abinda kecin zuciyarta ba
“Ki sauko muci abincin,usman ku matso maza aci abinci” ya fada yana saukowa qasan carfet gami da janyo farantin abincin gabanshi yasoma bubbudewa,amir ne kawai yace yaqoshi
“Abba suma bamu dade da gama karyawa ba,tun kafin umma tafita ma” ya fadi kasancewar dukka yafisu hankali da wayo
“Qyalesu suci,kasan hali ai ko sunci abinci idan sukaga zanci sai sunci ko abikaina?” Suka saka dariya duka harda yara matan.
Waiwayawa yayi da zummar sake cewa rufaida tasauko suci abincin sai yaga wayam ba ita a wajen,abinda bai sani ba tun sanda yasoma tattaro kansu suci abincin tamiqe tabar falon
“Ikon Allah,ina antyn taku?” Ya fada yana duba falon
“Tashiga daki abba” hanifa ta fada,saiya dire ummi yace yana zuwa.
Zaune ya sameta gefan gado qafarta daya kan daya tana cika tana batsewa,cikin kwantar dakai da kwantar da murya yace
“Haba amarya wadda bata laifi,ya zaki taso ga yaranki sun shigo gaidaki,ga kuma abinci can bakici ba?” Taso boye fushinta amma saita kasa,taga idan taboye abinda ke ranta kamar ta cuci kanta ne
“Ai gwara nabaku waje kuci sosai ko?” Dan jim yayi cikin mamakin me kalamanta ke nufi,bai gama wannan tunanin ba tadora
“Ta yaya ina amarya ranar farko a gidana zanci abinci da mijina kawai saikaje ka debomin tarkacen yara suxo su cikamin daki,fusabilillahi haka ake?,niwa nayiwa gaka duk cikinsu?” Mamaki sosai ya kamashi,don bai tsammaci jin wannan furucin daga bakinta,sakamakon a baya yadda take haba haba da yaran,har gidansu take sawa yaba kai mata su,sannan idan baizo dasubama zatasa yakira gida da wayarshi a bata yaran su gaisa,saisu kusa cinye masa kudin waya ma suna hira.
“Yanxu rufaida yaran nawa na cikina kika gayawa haka?,ko kunyar idanuna bakyaji?”dubanshi tayi,taga alamun maganar batayi masa dadi ba,amma sai ba zata iya bashi haquri ba,don a ganinta ita akaiwa laifi,maimakon haka ma saita soma qanqanun gunguni,ta maida kanta saman filo ta kwantar
“Nidai bawani mummunan abu nake nufi ba,saidai idan kaine ka fahimci haka”.
Ganin da gaske ba zataci abincin ba yaga bai kamata tun ranar farko haka ta faru tsakaninsu ba,saboda haka ya juya ya fice daga dakin,ya debo mata abincin ya aje mata
“Gashinan saikici anan” miqewa caraf tayi daga kwanciyar ta kamo hannunshi,cikin narkewa kamar maishirin kuka tace
“Wato baka ma damu dani bako?,to wallahi ba inda zaka fita anan zaka zauna kaima muci tare” hakanan yazauna din kodon abinda yafaru daren jiya yana ganin dole ya haqura ya lallabata.
“Ya kamata kije ku gaisa da mmn ummi,mmn amir bata nan tafita asibiti,in yaso zuwa anjima saina ganku kuma gaba daya ko?” Kamar ya soka mata wuqa a qirji haka taji,wanne irin taje ta gaidata don tsabar son ya siya mata raini?,ina laifi ma ita ta leqo?,amma batason wani dogon jayayya muma da abinda zai bata mata amarcinta yadda ta tsarashi,sabida haka tana hadiye bacin ranta haka tamiqe ta isa gaban mudubi tana sake goga hoda,zaya fita tace ya tsayata su fita tare,yace ta taddashi a falo.
Sai data sake kwalliye fuskarta sannan ta feshe jikinta da turare,ta ciri chewing gum cikin wanda tazo gidan dashi ta jefa a bakinta ta turo daurinta gaba sosai sannan tafito.
Tsaki taja qasa qasa tanajin takaicin ganin har yanzu yaran suna nan,haka suka dunguma gaba daya suka fice.
Tana nata falon tana tsintsince kaya zata soma shara,ranta cike fal da qunci da daci,musamman lokacin data fuskanci yaran sun shiga dakin amarya ne,ta qudira a ranta yau saitayi musu dukan tsiya,ta kuma zauna ta karanta musu kada tasake ganinsu dakinta,idan maman amir tasake to ita tabbas ba zata sakeba bare ta rainata,idanma basuyi wasa ba ko dakin mmn amir din sunbar zuwa bare su shiga dakin wata amarya.
Shine a gaba dauke da ummi,sai rufaida a bayanshi da sauran yaran daga bayanta,tsayawa tayi da ninke zanin goyon ummi wanda ta kwantar da ita dashi dazu saman kujerar tana dubansu.
Rufaida ta hango daga bayanshi,tana qarewa mmn ummin kallo,wadda ke sanye da t.shirt nai kwala harda aljuhu a gaban rigar,a tsaye t.shirt din take babu shape da alamu ta maza ce,sai zanin atamfa sungul wanda daya daga cikin zunnuwan goyon ummi ne.
Murmushi rufaida ta saki tana danne dariyar dake cinta,wani raini na musamman game da mmn ummin ya taso mata,ba shakka dukkan yadda tayi hasashensu haka suke,ta bangaren mmn ummi kuwa kunya da takaici suka cikata,ko a mafarki bata taba tsammatar rufaidan xata shigo dakin nata ba,dako da wasa ba zata taba yarda tazauna ta ganta a haka ba,hannu tasa ta amshe ummin tana cika tana batsewa,yayin da rufaida tazauna hannun kujerar mmn ummin tana qarewa falon kallo,babu wata qazanta tattare dashi,saidai da alamu bata damu da gyaran dakinta da sassafe ba a matsayinta name yara
“Mun tashi lpy mmn ummi” rufaidan ta fada tana murmushi wanda ita kadai tasan manufarsa
“Lafiya”
“Ya kwanan yara kuma?” Takuma fada da wani salo na daban
“Qalau” ta amsa mata tana cirewa ummi wandonta daya jiqe da fitsari.