Hangen Dala 1

Bbn amir ne yajuya zai fita rufaidan ta miqe
“Tsayani mana dear,bacci fa nakeji” daga haka tabi bayanshi,wani abu yatsaya mmn ummi a ranta,tabusu da kallom harara da ashariya cikin zuciyarta,sai usman yamiqe yana cewa
“Abba tsayani zani” finciko usman din tayi da hannu daya,ya saki qara kuwa saboda yaji zafi sosai
“Dakin uwarka ne kona ubanka?” Ta fada tana zarewa yaron ido,yaji ihunsa hakan yasa yadawo,hannu yamiqa masa
“Taho” da hanzarinsa yatashi,hanifa matace zata koma,haka suka sake binsa su ukun.
Tana shirin miqewa kan kujerarta tana tsara tadda zasu wuni tare saigashi tare da yaran,qugu ta riqe kawai tana kallonsu,ranta yasoma suya,ya aje usman yana shigewa daki saita bishi.
Sanda ta isa taras dashi tayi yana kira a waya,don haka ta tsaya tana kallonshi har computer ta shaida masa is not reachable,yasauke wayar tana sakin tsaki
“Taqi shiga” ya qarashe maganar yana duban rufaidan
“Dear,gaskiya bacci nakeji,kuma yarsn nan kasan bazasu barni nayi ba,niban saba da bari bari ba,infact ma bacci ni nakeji,tunda farfajiyar gidan nada yalwa ai zata ishesu wasa ko?” Bai samu sararin bata amsa ba kira yashigo wayar tashi,saiyaga mmn amir ce,da hanzari ya daga har hakan yaja hankalin rufaida tasoma son sanin waye yakirashi haka har yake zumudin dagawa cikin kulawa.
“Test test ne yanzu likita yarubutamin,kuma kudin hannuna danazo dasu duka sun qare,idan ba damuwa ko zakamin transfer ta accnt dina saina tsallaka nan titin asibitin akwai atm na cire?” Ta fada bayan ta gaidashi,hakanan yaji duka babu dadi
“Ke zakije ma ki cire kudi da kanki?,wayace ki tafima baki gayamin ba bayan nace ki shaidamin idan kin gama shiryawa?,kuma inata kiran wayarki a kashe?”
“Babu network ne inda nake din,sai yanzu dana fito” dan shuru yayi shima sannan yace
“Jirani ina zuwa” daga haka ya sauke wayar,saiya dauki agogonsa daje gefan gado yasoma daurawa.
Tsuke fuska rufaidan tayi,donta fuskanci dawa yake wayar
“Ina kuma zakaje?”
“Zan duba mmn amir ne a asibiti,tana buqatar wasu kudi zan miqa mata” idanu ta qanqance ranta nasake baci
“Amma inaji tace ai kayi mata transfer taje tacire da kanta ko?” Tsaiwa yayi da daura agogon dayakeyi yayi yana dubanta,ya tsammaci zata qarfafashi ne akan yaje dinma
“Matata da tsohon ciki a jikinta nabarta taje layin atm cire kudi?,yau qarshen wata anyi salary,kuma kema kinsan yadda wajen yake cika da masu cirar albashi duk qarshen wata ko?”
“Nidai gaskiya dear ban yarda ba,wannan wanne irin abune,duka yadda naso zama dakai hakan yaqi samuwa haba” ta fada cikin fushi tana juya bayanta.
Murmushi yasaki yana mamakin kamar batasan yana da iyali ba,amma dayake ance amaryace bata laifi saiya rungumota ta baya yace
“Haba sarauniyar mata,yanxu zanje na dawofa,abani aron lokacin baxan jima ba,afwa zamu samu lokaci har saikin gaji,kwana shidane dake fa nan gaba?” Wannan maganar ta sakata tadan sassauto,amma duk da haka fuskarta a hade take,zafin kishi takeji sosai idan tatuna wajen wadda zaije,musamman ma dataga ya dauki muqullin mota,mai yiwuwa ma yasakota agaban motar kuma duka da sunan matarshi,haka tana gani ya debi sauran kudinsa ya saka a aljihu yafice.
Sai dataji tashin motarsa ta tabbatar yafita sannan tadawo falon,yaran suna zaune suna kallo,ya sauya musu tasha zuwa mbc,cikin tsuke fuska ta dubesu
“Kai….ku tashi maza ku tafi dakin babarku ku kalla” ba musu suka miqe daya nabin daya suka fice,ta sauke labulenta sannan ta maida qofarta tarufe,tadawo tayi kwanciyarta bayan tasauya tasha tana kada qafa,haushin yaran yana cikata,haka kawai su zasu soma zame mata qarfen qafa babu gaira babu dalili?.
Zaune ya sameta cikin reception na asibitin,akwai fresh yo a hannunta me sanyi tana sha kadan kadan saboda wata sabuwar yunwa data taso mata kamar bataci komai ba kafin tafito.
Daura da ita yazauna yana mata sannu,sannan ya mashi dukka takardun gwaje gwajen
“Nan cikin asibiti za’ayi ko a wajene?” Ya fada yana dubanta,duk da fafur taqi dubanshi kai tsaye
“Sunce duk wanda yafi”
“Zauna anan naje lab din na tambaya wanne ne yafi saurin amsar result” daga haka yawuce xuwa lab na asibitin.
Bai jima ba yadawo
“Muje suyi mikin,sunce duka daya ne” daga haka suka wuce,tana gaba yana biye da ita a baya,da alama cikin yasoma mata nauyi sosai fiye da baya,don d’ai d’ai take daga qafarta har suka isa.
Ko lokacin gwajin ma yana tsaye bisa kanta,yana janta da hira lokaci lokaci,saidai duka bata fiya bashi wata cikakkiyar amsa ba,hakanan takejin haushi haushinsa,bakinta kuma takeji ya mata nauyi kamar me ciwon baki.
Basu bar asibitin ba saidaya tsaya aka kammala komai suka miqawa likitan,ya duba duka sakamakon sannan yadaga kai ya dubesu.
“Ba wata matsala bace mai yawa yadda na zata alhmdlh,saidai duk da haka tana buqatar hutu da kuma ci gaba dacin abubuwa masu gina jiki,jininta yahau kadan amma wannan ba matsala bace in sha Allahu,taci gaba dashan magungunanta”
“Toh likita,in sha Allahu” ya miqa masa hannu sukayi musabaha yana mishi godiya suka fito.
Da kansa yabude mata motar gidan gaba tashiga sannan ya zagaya shima yashiga nashi bangaren,ya tada motar suka fice daga asibitin.
Har suka hau kan kwalta sosai batace dashi uffan ba,sai daga bisani yadan dubeta kadan sannan yace
“Meye damuwarki?,me kike da buqata?” Itama duban nashi tayi kadan sannan ta dauke kai tana mamakin ma’anar tambayarsa da maqasudinta
“Babu komai” kawai tace dashi,numfashi ya aje
“Duka cikin amir da yake na fari,hanifa ahmad da rabi’a duka ba wanda jininki yahau sai wannan?” Sake dubanshi tayi kana tadauke kai
“Kowanne ciki da irinsa,hakanan ba lallai mace tayita samun yanayin cikkunanta yazana iri daya ba” sai yayi shuru duk da bai gasgata maganarta ba,zuciyarshi tana bashi kawai shine sila,hakanan yakejin duka ranshi babu dadi.
Bai sake magana ba har suka hau titin zooroad,wanda nata gane ina zai kaita ba saida suka kai bakin gate din gidan zoo,yayi horn masu gadi suka bude yabiya kudin shiga suka bashi ticket yashige.
Maimakon ya dakata a inda aka saba parking sai taga yayi ciki,tafiya kadan sai gasu a wani garden na daban,ya tsaida motar ya dubeta
“Fito muje” da mamaki ta dubeshi
“Me zamuyi anan?,bafa yara muka kawo ba?” Kai ya kada
“Na sani,ke na kawo kisha iska ki huta kadan”dan shuru tayi kana tace
“Amma kasani na baro yara a gida,sannan ana iyayin baqi yaudin”
“Yara ai basu kadai bane,akwai mutane a gidan,baqi kuwa duk wanda yazo akace masa kina asibiti ai yasan lalurarki” bata sake cewa komai ba ya dafe mata murfin motar tafito,nan ma yasake wani pyment din suka shiga.
Sosai wajen taji ya sanya mata nutsuwa,saboda yanayinsa dake luf luf da shuke shuke masu bayar da sanyi da iska mai dadi,hakanan babu hayaniya kai kace ma ba’a gidan zoo din kake ba.
Sai da sukayi awa guda cikakkiya ya tabbatar data sake samun nutsuwa da hutu sannan yazauna yana fuskantarta,dukka hannayenta yakama yana duban qwayar idanunta bayan yakira sunanta,kasa amsa mishi tayi,sai zuciyarta tayi rauni,duk wani nauyi data rinqa daukewa a qirjinta taji yau yana neman ya rinjayeta,cikin murya mai taushi yace
“Nasani cewa kinyi qaqari matuqa,kinyi jajircewa da tsaiwar daka,hakanan kin nuna sadaukarwa da kuma kara da karamci irin naki,tunda lamarin nan yataso bama yanzu ba tun zamanin maryam zuwa yanzu,ina mai matuqar miqa godiyata a gareki da kika zamemin abun dogaro cikin gidana,kika amsa kuma wannan sunan da hausawa ke baku na UWAR GIDA RAN GIDA,babu shakka kedin ran gidana ce halima bawai ganin idanunki ba,Allah shine shaidata,na gode qwarai halima,ubangiji yaci gaba da baki juriya da qarfin hali,ya kuma saka miki da aljanna madaukakiya” idanunta yarausayar taba son qarfafawa kanta gwiwa ta amsa addu’arshi,sannan ya dora
“don Allah inason wata alfarma awajenki halima game da gidana”
“Allah yasa bazata gagareni ba” ta furta a sanyaye”
“In sha Allahu,na yarda da nagartarki halima,inason aduk sanda nayi kuskure a tsakanin kuku ukun kiyimin uzuri,sannan karki qyaleni ki sameni ki nusashe dani,ki dorani kan hanya” idanunta tawaro waje har hakan yaso bashi dariya
“Baban amir,gaskiya ka doramin aiki mai girma da nauyi,dukkaninmu matanka ne,hakanan kana qaunarmu ka auremu,ta yaya zan dinga bin diddigi kan lamuran kowaccenmu ina gyara ko kwaskwarima akai?”
“Ashe bakison kada nashiga wuta kenan ko halima?”da sauri ta girgixa kai
“a’ah,’a’ah,ko kadan,zanyi iya abinda naga zan iya dai,kuma shine daidai wanda zan fita haqqin addinina” kai ya kada shima
“Ko hakanma na gode,Allah ya saka da khairan” amin ta amsa mishi tana kallon yatsunta da suka dan tashi kadan fiye da dada kafin tasamu ciki.