Hangen Dala 1

Kai tsaye dakin mmn ummi yanufa,baima kula da salima dake kitchen ba tana kunna wutar gas,ranshi ne kawai ke suya,taya za’ace yaranshi sun wuni basuci komai ba bayan za’a iya girki a gidan koda bai bada kudin cefane ba,tunda suna da komai.
Wannan karon tayi wanka ta shafe jikinta damai,tana sanye da dovuwar rigar material me gajeran hannu,kwance take abinta saman doguwar kujera tana kallo hannunta riqe da remote,ummi ma nakwance gefanta tana bacci,da alama ta matseta ne ta sanyata baccin dole.
Tunda ta amsa mishi sallamar bata kuma kallo shi ba taci gaba da abinda take,zama yayi hannun kujerar dake daura da ita sannan yace
“Lafiya kuwa yau kike?” Dubanshi tayi ta amsa mishi a taqaice
“Eh”
“Qalau kuma?”
“Ras” ta sake amsa mishi,kai yake jinjinawa,dama yayi tambayar ne don kada ya yanke hukunci bisa rashin sani
“Amma maryam don tsabar wulaqanci dason tozartani gidana akwai baqi ace an wuni ba’aci komai ba tun abincin safe?” Dama jira take yace wani abu,saboda haka tamiqe tazauna sosai
“Ka fito kafadi maganarka kanka tsaye mana,kace kawai ban girka na baiwa amaryarka da baqinta abinci ba,to bari kaji,wallahi wallahi dana dafa taci ita da baqinta gwara kowa yawuni da yunwa,kuma ni ai bamai aikinta bace dazan dafa mata tana zaune,aiba ita tafi kowa zane a duwawu ba,idan ta matsu maiya hanata shiga kitchen din ta girka?,aiba riqe mata qafafu akayi ba kuma qofar kitchen din a bude tawuni bare kace wani abu” daga haka takoma ta kwanta abinta,harya bude baki zai magana sai kuma ya fasa,yanajin akwai lokacin maganar,saiya miqe yafice daga falon ba tare daya sake ce mata komai ba.
Bakin layinsu yafita yaje ya qaro cefane,sanda yadawo salima harta gama dafa indomie din tana juyewa,sannu ya mata ya aje kayan yajuya zuwa dakin rufaida.
Itama kallon yataddata tanayi,ta sauya kwalliyar jikinta da wasu doguwar riga data matseta sosai,murmushi tasakar masa ya maida mata ya zauna yana cewa
“Ga kayan cefane can,kozaki taya yarinyar can salima ku gyara ta dora wani abun,don mmn amir ta gaji gsky,nasan tuni ta kama”
“Tashin balagar tsintsaye” ta fadi cikin ranta,amma a fili saita aje lemon hannunta
“Ina mmn ummin idan mmn amir ba zata iya ba?”
“Ajima zan ganku gaba daya,zaki ji koma meye” narke masa tayi sosai
“Yanzu dear jiya akawoni yau a ganni a kitchen?,idan nayi baqi suka gani aisai sucema bakasona” daga haka tasaki kukan qarya,lallashinta yasoma yi har aka bagarar da zancan,inda daga qarshe indomie yaje yasiyo musu da qwai.
“Anty bbn amir naga ya aje kayan cefane tun daxun,kuma naga ba wanda tafito bare ya taba” salima ta fada bayan ta aje musu indomie din sun soma ci,dubanta mmn amir tayi na wasu sakanni,ta gama gane abinda ke faruwa,ta kuma gama yanke hukunci na matakin da zata dauka
“Mu gama kuje keda rabi’a ta tayaki ku gyara ki kawo amir yakai markade,saiki dora koda shinkafa ce,ki dafa qwai ki hada salad”
“Tohm” salima ta fada tana ci gaba dacin abincinta.
Tanacin abincin tunani na zuwar mata,ta soma gane inda kowa yadosa,zakuma tadauki mataki cikin kwanciyar rai.
Suna gamawar kuwa saliman tayi yadda tace din,ita kuwa sallar la’asar kawai tayi wadda lokacinta yadan gota ma sannan tasha magungunata tashige dakinta takwanta donta huta,bata jima ba kuwa bacci yayi awon gaba da ita.
Sanda tafarka anata kirayen sallar magariba,nepa sun dauke wuta amma har bbn amir din ya tayar da inji,wanka takesonyi,saita miqe a hankali tafito falon,babu kowa falon amma tana dan jiyosu daga tsakar gida,fes falon yake yana qamshin turaren wuta kai bakace da yara a dakin ba,kamar dai yadda saliman taga tanayi,tazauna saman daya daga cikin kujerun tana qwalawa saliman kira.
Shigowa tayi da alama tayi alwala ne
“Gani anty”
“Kin gama ne?”
“Eh na gama,suna cikin coolers,na zubawa bbn amir nashi”
“Yauwa sannunki da aiki,yanzu ruwan wanka zaki doramin,idan kin dora din ki leqa dakunansu ki gaya musu abinci yana kitchen,kadan ruwan zai danyi zafi ki kowomin zanyi wanka”ta amsa mata da to ta juya tafita.
Wankanta tayi sosai ta shirya cikin wata doguwar rigar material,wadda tayi mata kyau sannan ta fidda cikinta sosai,ta kuma haska choculet colur fatarta,ta feshe jikinta da turare kamar yadda tasaba,sannan ta dan goga hoda daman lebe tadawo falon.
Suna falon amma zaune shuru sakamakon bitar karatun islamiyya da kowannensu yakeyi,saita samu gu tazauna ta jona dasu itama har aka sallaci isha’i,lokacin bbn amir yashigo,yaran suka tarbesu yariqesu kana ya qaraso,bai zauna ba ya shaidama mmn amir din yanason ganinsu a falonshi,ta amsa masa dato sannan yafice.
Gyara daurin dankwalinta tayi ta sake feshe jikinta da turare sannan tasake fitowa,hanifa tayi sauri tace
“Zan biki umma”
“A’ah ki zauna da salima,yanzu zanje nadawo” daga haka tayi gaba.
Shi dayane da alama sauran basu fito ba,tayi sallama tashiga falon,ya amsa mata yana murmushi kana ya dora da fadin sanda take shirin zama
“Sannu uwar biyu” murmushin itama tasaki,sai data zauna sannan tace
“Ni dayane a cikina,scanning ya nuna” baki ya kama yana murmushi
“Idan kuma Allah boye dayan yayi fa?” Dariya yabata sosai,wai duka yaran gabanshi basu isheshiba,kalen ‘yan biyu yakeyi
“Dayanma an godewa Allah,banda abinka bbn amir duk yaran dake gabanka?,ga wanda idan Allah ya nufa amarya zata haifa maka?”
“Dozen biyu fa nakeso” sosai dariya ta qwace mata ganin bilhaqqi da gaske yake
“Ina zakakai dozen biyu”
“Da gaske nake miki,yara ai rahamane” tana dairiyar take gyada kai,daidai sanda rufaida amarya tashigo.
Sanye take da wasu matsatstsun baqaqen riga da skert da suka fidda dukkanin jikinta sosai,taku take d’ai d’ai tana taunar chewing gum tashigo da sallama.
Kai tsaye kusa da bbn amir tazauna kamar zata shige jikinsa,dauke kai mmn amir tayi kamar bata gani ba
“Kin sha magungunan dai ko?” Bbn amir yakuma fada yana dan janye jikinsa ganin yadda ta matseshi sosai,fuskarta a sake tana murmushi kamar dai daxun tace
“Bamu jima da dawowa ba dukka nasha,shinema nadan samu barci”
“To ma sha Allah,Allah ya qara lpy”
“Amin amin,na gode” ta fadi tana maida hankalinta ga wasu jaridu dake kusa da ita ba tare data dubi sashen da rufaidan ko bbn amir din yake ba.
Tanajin yadda rufaida ke janshi da hira irinta soyayya,amma sai tayi kamar batasan sunayi ba,ta maida hankalinta sosai tana duba jaridar,rufaidan rabin hankalinta nakan mmn amir din,so take taga sauyawar fuska ko yaya tattare da ita,saidai taqi bata dama,hakan yadan sosa mata rai,tasake bada qaimi,amma azahiri saikace ko a jikin mmn amir wai an mintsini kakkausa,duk da zuciyarta cike take da kishi fal.
Ganin abun na neman wuce gona da iri saita rufe jaridar tana duban bbn amir
“Ko za’a yiwa mmn ummi magana ne?,inason in sha magani na kwanta dawuri”
“Eh to,to ayi matan” yana rufe bakinsa mmn ummi tashigo dakin dauke da ummi,mmn amir tasoma mata tafi tun kan su qaraso yarinyar tasoma daga mata hannu,suna qarasowa ta karbeta,tahau qyaqyata dariya kuwa,don yau duka basuga juna ba.
“A ina zan zauna kenan?” Mmn ummi tafada fuskarta tsaf a dinke,duka suka dubeta shida rufaidan don basu gane me take nufi ba,shi yasoma magana
“Ko inama,ai akwai wajen zama”
“Amma ka kiramune don muzo mu ganta nanuqe da ita,toni indai irin wannan zaman za’ayi wallahi bazan zauna ba” sai sannan rufaida tagane me take nufi,saboda haka tasake shige masa tana duban idanunta
“Ayyah mmn ummi,aiga daya side din can saiki zauna na wani abu bane ko?” Ta fada tana fakar idanun baban amir ta watsa mata harara,sarai ta ganta,kuma itama batayi qasa a gwiwa ba ta maida mata,kafin tace wani abu bbn amir yadubi rufaida
“Koma can kema ki xauna” ya nuna mata kusa da mmn amir,ranta yabaci sosai,saidai duk da haka taci riba tunda ta bata ran koda iya mmn ummin ne.