Hangen Dala 1HAUSA NOVEL

Hangen Dala 1

Cikin nutsuwa ya musu dukkan jawabin daya dace kowanne maigida yayiwa matansa,yaja hankalinsu kansu xauna lafiya,kuma kowa ya girmama na gaba dashi,kaf maganar bata yiwa rufaida ba,ta tsammaci xai bata wani matsayine na daban a gabansu cikin maganarshi,mamaki ita gaba daya take,kaman ma ba jibril dinta ba,duk wani fifiko datake zatan ta dara saura dashi bata ganshi ba cikin bayananshi,yana bayani kaman daya take da matanshi?,ya zama lallai ta nuna musu akwai banbanci,ba zata lamunta yazama tana hangen dala ba tana tunanin birni zata shiga ashe ba birni bane.

“Sai zancan rabon kwanaki zai zama bibbiyu kamar yadda aka saba ko?,mai magana ko qorafi kuma bismillah kafin mu tashi” shuru dukka sukayi,kowa da abinda yake saqawa cikin ranshi,ganin haka sai mmn amir tagyara zamanta
“Nidai ina da magana ko qorafine zance” waiwaya yayi yana dubanta sannan yabata dama
“Yauwa,inajin gsky zan sadaukar da kwanakina da kuma girki zuwa hannun ‘yan uwana,saboda yanayin jikina,da kuma hutun da likita yabuqata na dinga samu” dukkaninsu suka zuba mata idanu,rufaida tayi caraf
“It means mu zamuna miki girki kina kwana da miji?” Ta fada ranta na mata zafi,kallonta mmn amir tayi sosai kana tasaki murmushi
“Wannan ba damuwa bace,nabarmiki bbn amir harsai na haihu,kiyi girki kuma ki riqeshi” can qasan ranta taji wani mugun dadi,a fili tasaki murmushi tana qiyasta bagidajiya a ranta,banda bagidajiya ta yaya za’ayi ki barwa kishiya mijinki?,ai idan itace ko naquda take ranar ba zata taba yarda ta barwa kishiyarta mijinta ba.

“Tabdi,to wallahi ni ban yarda ba,ta yaya zakiyi haka baki nemi jin ta bakina ba,kina nufin tayi kwana hudu nidata samu a gidan nayi kwana biyu,wallahi ko sama da qasa zata hadu ban yarda ba,da sake an baiwa mai kaza kai,saidai muyi uku uku” mmn ummi tafada tana kumfar baki,haushin mmn amir ya cikata taf,tana ganin kamar akwai maqarqashiya ko hadin baki tsakaninta da rufaida ko bbn amir,sun hada baki da kaine kawai don a zalunceta ko a cusa mata baqinciki”
“Kinga jimana maryam,kamar yaya?,kwana dai ba nata bane kuma tace tabarmin har saita haihu,tunda ba’a baki ba aisaiki saka na annabawa,kinata abubuwa na saka miki idanu daga jiya zuwa yau,shine yanzun ma dai dole kin saka nayi magana,ni banson aikin zubda aji gaban miji” ta fada tana kada idanu hadi da kada qafarta data dora daya saman daya.

A zabure mmn ummi tamiqe tana nuna rufaida
“Ke dakata karkimin rashin kunya,wutsiyar raqumi tayi nesa da qasa wallahi niba sa’ar yinki bace” dariya rufaida tabushe dashi
“Ikon Allah,yanzu duk saboda ba’a baki……”
“Dakata ya isheni da Allah malamai haba!” Bbn amir yafada cikin bacin rai
“Wane irin abune wannan?,to ya isa,zata riqe kwanakinta,sannan ku zaku ci gaba da girki har Allah ya sauketa lafiya,ke maryam zaki riqe girki har kwanakin da rufaida zata karba,zakuci gaba dayin kwana uku uku” hakan yayiwa mmn ummi dadi,saboda tasani dama ita ko mmn amir duk wadda cikinta ya tsufa haka ‘yaruwarta ke amsar girki harta haihu,ko banza an soke kwanan da aka qarawa rufaida,saboda haka ita bata da damuwa,saidai girkin da zatayi har tsahon kwana shida tana basu sunaci bataji xata iya gaskiya,ta wannan bangaren ma kamar bbn amir din duka gidan ita yafi rainawa kenan,mata biyu kowacce nakwance zata dinga dafawa tana bata?,gaskiya da sake an baiwa mai zaka kai.
“Nifa gaskiya bazan mata girki har kwana shida ba,don ba baiwar wani bace ni” ta fada tana harare harare,mamaki ya cikashi,wato wanzan baison jarfa kenan,ya tuna sanda mmn amir tadinga mata girki kwana da kwanaki,harda qarin kwana uku tayi mata saidata cike kwana goma cif
“To shikenan,mu zuba nidake naga waye mai gidan”ya fada akusashe cikin bacin rai,fuuu ta amshe ummi daga hannun mmn amir tafice daga dakin,binta da kallo mmn amir tayi harta fice,saita miqe itama a tausashe
“Nikam ina neman alfarmar akarbi kwanan idan zaiyiwu don Allah,saida safe” daga haka tayi gaba,duka ranta babu dadi,taya mmn ummin zata bari daga shigowar matar tsakanin jiya dayau amma su soma irin wannan tataburzar,harta bari taga warginta da zata dinga fadi in fada da ita?.

Itakam batasan ya aka kwashe ba,tunda tashige dakinta tadan zauna cikin yaran kana tawuce tayi kwanciyarta,bata farka ba saida asuba.

Da safe ya leqosu kamar yadda yasaba,ta gaidashi a ladabce sannan tace
“Yau salima zata koma gida”
“Au,ai na zaci zata tayaki zamane harsai kin haihu” kaita kada
“Inna ba zata barta ba”
“Data qyaleta kuwa aida hakan yafi,shikenan,idan zan fita zan baki saqo ki bata”
“Tohm,sai alfarma da nake nema” harya soma takawa ya tsaya
“Wacce irin alfarma halima?”
“Yaran nan nakeso tawucemin dasu,saboda indai suna nan din bazan huta yadda nakeso ba,idan suka danyi koda sati ne sai adawomin dasu don Allah” ta fada atausashe,saboda tasan halinsa sarai,baiso ko yaya yaranshi su matsa daga kusa dashi,shuru yayi na wasu mintuna sannan ya amsa
“Banaso halima,amma yadda kike kyautatamin dole naso abinda kikeso,su bita din,babu damuwa”
“Na gode qwarai”
“Madalla” ya amsa yana ficewa.

Saida saliman tayi mata duk wani gyara sannan suka shirya tsaf ita da yaran,sanda suke hada kayansu ahmad yashigo
“Umma inasu hanifa xasu?”
“Zaku anguwane,amma bazasu dade ba zasu dawo” nan kuwa ya narke kan saiya bisu,da dabara tasamu ta turashi dakin mahaifiyarshi,don tasanma babu batun mmn ummin tabarsu suje.

Sai data rakosu har farfajiyar gidan sunata murna zasu gidan innar, taga tafiyarsu sannan tadawo cikin gidan,sai takejinta sakayau da suka tafi yaran,koba komai kafin su dawo tana saka ran lamuran gidan su daidaita tagama gane kan komai da yadda zata bullowa kowanne matsala da yadda zata fuskanci komai.

Tana komawa ciki ta sakaya qofarta tayi kwanciyarta hankalinta kwance,tasan koma wacce matsala ce zata taso zata zo mata da sauqi,lokaci kadan kuwa bacci ya kwasheta .????️‍????️????️‍????️ *HANGEN DALA*????️‍????️????️‍????️
_Ba shiga birni ba_

©️®️ *Safiyya Abdullahi Musa Huguma*

Haske Writers asso ????

*BABI NA GOMA*

*zaku iya saurarar litattafaina a tasha ta ta SAUTIN HIKIMA dake youtube,litattafan sune kamar haka*

*Alkawarin Allah*

*Daurin Boye*

*Kundin Kaddarata*

*Mutuncin Mace*

*Dangantakar Zuci*

*_karku manta,nan gaba kadan acan zaku dinga samun ci gaban kowanne littafi nawa*????

 

 

Tunda ta kwanta bata farka ba sai bayan sallar azahar,tamiqe tana ambaton sunan Allah ganin lokaci na neman qurace mata bata sallaci azahar ba,bandakin dake falonta tashiga ta daura alwala tazo ta gabatar da sallar azahar din,tana nan saman abun sallar tana tasbihin data saba bayan kowacce sallah me 33 taji yunwa tasoma sakadarta,duk da haka bata katse ba amma saita qara sauri harta gama,tashafa addu’arta tamiqe tana tunanin abinda xataci.

Bata qaunar fita ma tsakar gidan bare tasan meke faruwa,batasan yata qarke ba,saboda haka saita jona heater anan falon nata tazauna tana jiran ruwan ya tafasa,mintina kadan ya tafasa,ta duba cikin dakinta ta laluba cikin kayan abinci da lokaci lokaci wanta yakan bata,dayake gidan basu da matsalar abinci majority bayarwa take,na qarshen ne daya aiko mata dashi bata bayar ba ta aje din,a sannan bikik bbn amir yakusa,batasan me zaije yadawoba shi yasa ta aje din.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button