Hangen Dala 1HAUSA NOVEL

Hangen Dala 1

 

Sannu sannu sai Allah ya canzashi,wanda yasan ba komai bane yakawo hakan face addu’a data saka a gaba babu dare babu rana.

Yasha raba dare suna waya da mmn ummi suna kwance gado daya da mmn amir,baya shayi ko shakkarta,takan tashi ko kallonshi ba zatayi ba,tun a sannan bata da bandaki cikin falo sai tsakar gida,nan zata fito ta daura alwalarta ta koma falo tayi shinfida tahau sallarta,tabarshi shi kuma cikin dakin ya qaraci wayarshi har yayi bacci,wani lokacin bai sake ganinta sai zashi sallar asubahi.

Yakanyi mamaki idan washegari tatashi wasai tashiga sabgarta da yaranta,fuskarta cike da annuri,wanda duka hakan bai rasa nasaba da wannan sallar dare data kusa kwana yi.

“To tashiga hankalinta,idanma tanayine saboda muji n bata a gabana,saidai idan ita bata da tarbiyya mu muna da ita ehe” bai saurareta ba sai yunqurin danne zuciyarsa da yake,yasa kanshi yafice daga dakin.

Ya tabbatar da cewa kura ce tayi lafiya,ko kuma yakoma kan tarbiyyar mmn amir ne,inda ta sameshi a lokacin da yake a bbn amir dinsa bata isa ta gaya mishi wadan nan kalaman ba yana kallonta,koda bada shi take ba,saidai mmn amir ta zame masa mudubi,hakanan yakanji a karan kanshi bai kamata yayi wani abu naba dai dai ba,kobanza a yanzun iyali yake tarawa.

***** ***** ***** ******

Cikin kwanaki amarci sosai rufaida takeci yadda takeso,tasamu kusan duk abinda takeso daga wajen bbn amir din,don idan yadawo daga kasuwa babubinda yake sake fita yana tare da ita,hakan yakan mata dadi yana faranta ranta,takanyi kowacce shiga da take tunanin zata ja ra’ayinsa da hankalinsa,ta kuma samu yadda takeso,zub da habaici jirwaye da kamar wanka,dariya da darrarku na cusa haushi da takaici dukka ta baje abinta.

Babu wanda ke qunsar takaici irin mmn ummi,nafarko bata da wata sana’a da takeyi face zaman dabaro,zaman hira,zaman charting ko xaman kallo,uwa uba gaba duk wani motsi na rufaidan idanunta yana kai,kome take tana sane dashi tana biye dashi,hakan ya sanya tunda rufaidan ta fuskanci hakan saita qara qaimi,kullum burinta ta bullo da wani sabon abun dazai basu takaici.

Saidai ta bangaren mmn amir ko a jikinta wai an tsikari kakkausa,wasu abubuwan tana sane dasu itama,amma data fuskanci zuciya na neman janta saita dawo da sana’arta,nan da nan taci gaba da saida ruwa da lemonta,kasancewar ta iya sosai,ga uwa uba tsafta,hakanan idan bata komai takan zauna tayi tilawar qur’ani,idan ta gaji ta kunna kallo ta taba,dama ita ba charting take ba,idan tagaji da kallon kuma takan kunna karatun qur’ani yadda zai cika dakinta ya hanata jin motsin kowa da komai,yara kam har yanzu bata daukosu ba,don haka wuni takeyi daki abinta,idan dare yayine takan nemi izini wajen abban amir tadan fita tayi tattaki kadan tadawo gida,takan leqa wani sa’in gidan mmn laila maqociyarsu,kuma qawarta qwaya daya da take da ita,bata fiya shiga gidan tayi fitowar banza ba,takan qaru da ita ta fanni da dama,kusan halinsu yaxo daya,hakan yasanya suke abota sosai.

Abu biyu zuwa uku ke damun rufaidan,yadda ta fuskanci jibril din mutum ne mai son yara,uwa uba baya yarda da wulaqanta kowa cikin matansa,amma ta fuskanci kamar mmn amir din yafi kaffa kaffa da lamarinta akan mmn ummi,hakan yasanya tasake daura damara gamida cin alwashi.

Cikin haka kwanakin amarcin amarya rufaida sukaci gaba da turawa,har mmn ummi tagama girkin yazamana a yanzun rufaidan ce zata karba.

******* ******** *******

Karfe bakwai na safiya ya farka daga baccin daya daukeshi bayan dawowarsa daga sallar asuba,yazauna saman gadon sosai yana kallon rufaida daketa sheqar baccinta,donko sallar asuba batayiba kasancewar tana hutun sallah.

Hannunsa ya saka saman filon da take kai ya bubbuga yana tashinta,daqyar ta iya bude idanunta da sukayi jaa saboda bacci,mugun dadin baccin takeji sosai
“Tashi ki doramin ruwan wanka,saiki dafamin wani abu,zan fita daurin aure qarfe tara da rabi nakeso nafita” lumshe idanunta tayi tanajin wani yaji yaji na bacci,ta yaya tana baccinta me dadi zaice tawani tashi tadora masa ruwa da abinci?,ruwanne bai iya dorawa ba ko abincin ne dole sai yaci,itafa ba abinda tatsana tun a gida irin ka hanata baccin safe,daka hanata bacci da safe gwara kayi mata koma meye
“To” kawai tace dashi ta maida idanunta ta rufe,ya zaci taji,saboda haka yamiqe yafita falo yashiga bandaki don ya rage cikinsa kafin ruwan yayi zafi.

Saidai abun mamaki koda yafito wajen minti ashirin saiya sake samunta kwance abinta,babu alamun tatashi ma,sake tashinta tayi,ta dago kao cikin fusata,wanda har taja tsaki ba tare data tuna a inda yanzun take ba
“Wai meye?,nifa gaskiya bacci nakeji,kabari idan natashi saina dora maka mana” tana kaiwa nan tasake maida kanta
“Ya zakici haka,tashi da Allah,ina gayamiki zan fita ne qarfe tara da rabi fa” cikin qunar rai kamar ta kutuntuma ashar tatashi tazauna,fuskarta a dinke tsaf,bacin rai kamar tayi me?,ta kalli agogo taga takwas saura
“Haka kawai saboda rashin sanin muhimmanci mutum a akama a tasheshi,toko a gida ni iyanzu ina kwance,babu kuma wanda yake tashi na,sai kawai yanzu azo a hau tashin mutum” ta sake jan tsako bayan ta gama qunquninta.

A falo ta wuceshi fuuu ko kallonshi batayi ba,ya bita da kallo kawai harta fice,mamaki yadan kamashi,na meye quncin tashin?,wani lokaci kafin suyi aure iwar haka yana shirin fita waya na maqale a kunnenshi suna shan hira,kullun dawuri take tashi saboda shi,yanzun kuma na meye nauyin?.

A kitchen kuwa bayan ta dora ruwan wankan saita samu waje tazauna,bacci nacin idanunta kamar takifa,ba zata iya tuna yaushene tatashi iwar haka daga bacci ba a gida,idan ba rashin lpy take ba zata asibiti,ko wata lalura ta daban.

A daddafe tagama dafa ruwan tajuye masa tashiga dakin ta dire masa
“Yauwa,shayi xaki fara dafamin,saiki soyamin doya daqwai,ta isheni,idan ita zakuci kiyi duka gidan,idan kuma wani abun zaki dafa muku to” idanu ta fiddo,kusun uwa,bayan shayin ma sai an dafa wani abun na daban?,na daban dinma sai ta dafa da kowa cikin gidan?wallahi ba zata iya wannan tsiyar ba,ganin yashige bandaki sai kawai tajuya takoma kitchen din tadora shayin shima tana Allah Allah ya dahu,cikin zuciyarta kuwa haushi cike fal na hanata baccinta.

Tana gama juyewa ta dora ruwa,ta farke indomie ta tsumbulata cikin ruwan,ta farke maginta ta zazzage mata ta rufe
“Babu wani doya da qwai da zan iya da sassafen nan kamar wata ‘yar daudu,yaci indomie kawai,gwara dana hade mata kayan hadin bari naje na kwanta nadan sake matsewa kafin ta dahu,aikin banza,banson tashin safiyar nan” tasake yin tsaki tana ficewa daga dakin.

Gadonta tawuce tafada kai,ta sake jan bargo ta lulluba abinta,batayi minti daya cikakke ba baccin yasake awon gaba da ita.

Daure da towel yashigo dakin yana goge jikinsa,ga mamakinsa saiya sake ganinta kwance tana bacci
“A’ah” ya furta ranshi nadan sosuwa,bubbuga qafafunta yasoma yi
“Rufee,tashi mana ina abincin?” A zabure ta farka tana mutstsika idanu,yasake maimaita mata tambayar
“Au,tana wuta bari nazuba maka”
“Doyar?” Ya fada cikin mamaki,bata amsashi ba tayi gaba da sauri,saidai ina ta makara,sanda taisa kitchen din har mmn ummi da qauri ya isheta tafito tasauke tukunyar,wadda tuni taliyar ciki ta qone qurmus.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button