Hangen Dala 1HAUSA NOVEL

Hangen Dala 1

Turus tayi tana kallon tukunyar tana kuma kallon mmn ummi da tukunyar taliyar ke gabanta………????️‍????️????️‍????️ *HANGEN DALA*????️‍????️????️‍????️
_Ba shiga birni ba_

©️®️ *Safiyya Abdullahi Musa Huguma*

Haske Writers asso ????

*BABI NA SHA DAYA*

 

*ZAKU IYA SAURAREN LITATTAFAINA A TASHATA TA (SAUTIN HIKIMA) DAKE A YOUTUBE,SAUQI GA MUTANEN DA BASU SON KARATU DA KANSU SAIDAI SAURARE,LITATTAFAN NAWA SUNE KAMAR HAKA*

*ALKAWARIN ALLAH*

*DAURIN BOYE*

*KUNDIN KADDARATA*

*MUTUNCIN MACE*

*DANGANTAKAR ZUCI*

_DA WASU SABBIN DA ZASU ZO MUKU NAN GABA KADAN DA YARDAR ALLAH_

 

 

Idanu suka hada da mmn ummi,sai kawai ta waske tana bata rai ta isa bakin tukunyar tasa hannu tabude murfin,ganin yadda tayi baqiqqirin saita saki tsaki,dai dai sanda bbn amir yashigo kitchen din saboda ya zaqu ya fita,yana neman makara ne
“Ina abincin?” Ya tambaya yana duban rufaida da tukunyar taliyar dake gabanta
Sautin dariyar mmn ummi ya karade kitchen din,wanda hakan yasanyasu dukka suka waiwaya suna dubanta,sai kuma ta gimtse kamar ba itace tayi dariyar ba,ta soma ‘yan waqe waqenta tana ciro wasu fulasanta tana sauya musu waje.

Sosai rufaida ta qulu,ta sani sarai da ita take,amma sata a gidan barawo rance ne,kuma duk wanda yaci tuwo da ita miya yasha,ba zata lamunya ba,kuma saita fanshe dariyar data yi mata din
“Ka ganta qonewa tayi wallahi” ta fada cikin salon shagwaba tana wani yarfe hannu,wanda hakan ya qular da mmn ummi wadda kunnuwanta suke kansu
“Qonewa kuma?,garin yaya zaki dora taliyar da bata wuce minti takwas ko goma ta gama dahuwa harta qone?”
“Na dora ne bacci yadan rinjayeni naje na kwanta kanta qarasa”.

Dariya mmn ummin tasake kwashewa da ita cikin salon waqa tace
“Kayan kitchen mama tasiya min,abinci dahuwar ‘yan gayu,wani kalarma sai an dandana,ayye sama mata,mata” daga haka ta sanya kai tafice abinta tana sheqa dariya.

Sosai rufaida ta qarasa qulewa,a zafafe ta waiwayo tana duban bbn amir
“Kanajin matar nan ko?,nifa take tsokana,wallahi kaja mata kunne niba sa’arta bace,idan ba haka ba nixan dauki mataki a kanta dakaina” nan take yaji ranshi yabaci,ita sam bata abinda zaici da barna da kuma bata mishi lokaci take ba,sam bashi ya dameta ba?,bacin rai ya hanashi magana,sai kawai ya rabeta ya isa gaban gas din.

Qwai uku ya dauka ya fasa ya kada,yana neman frying pan ta qaraso wajen
“Ina maka magana amma kayimin banxa kamar bada kai nake ba?” Ta fada itama ranta yana baci sosai,tana ganin kamar ya wulaqanta ko kuma yana bayan cin fuskan da mmn ummi tayi mata kenan.

Kai ya daga ya dubeta kawai,sau tari a kwanakin nan idan tana wanu abu sai yaga kamar ba rufaidanshi daya sani ba,kamar wata rufaidan ce ta daban,sai yaga kulata ma bata bakine,tunda ita batasan ya kamata ko bai kamata ba.

Har yagama soyawa yajuye yadauka yawuce tana tsaye,shurunsa saiya sake bata mata rai gamida kuma tunzurata qwarai,fuuu tabi bayanshi dakin,ta sameshi zaune harya soma karyawa da ruwan tea din data dafa mishi,da kuma qwan data soya.

Kanshi ta tsaya cikin bacin rai,don tana jin ya kamata tanuna mishi bacin ranta sosai
“Ni zaka wulaqanta jibril a gaban matarka?,ni rufaida ni zaka yiwa haka,na kawo.maka qararta amma kayi kunnen uwar shegu da qorafina,wannan shine kulawa ta musamman da kayi alqawarin bani,shine darajar tawa da kace zaka daukaka fiye data kowacce diya mace?,jibril tunda nashigo gidanka nake ganin abubuwa na cin fuska da wulaqanci,dama haka kake?,ina duka alqawuran daka daukarmin?”.

Kai ya tada ya dubeta
” ke bakisan kinyi ba dai dai ba?,bakisan abinda kikayi shi yafi cancanta ki maida hankali akansa ba ba wani shirmen banxa ba?,ga abinda yafi muhimmanci sam ke bashine a gabanki ba,kawai ta abinda aka miki kike na daukar miki fansa?,hakan shine dai dai a wajenki kenan?”ranta yasake baci,wato shi baima ga abinda akayi mata ba kenan,abinda aka mata din shine shirmen banza
“Amma dai aiko yaya kayi magana ko kodan saboda ta rainani,idan yaso mayi solving wannan issue din daga baya” shuru yayi yaba kallonta,wato bata fahimceshi ba kenan har yanzu?,sai kawai yamiqe daga cin abincin yana qoqarin danne bacin ranshi da mamakinsa,yadauki jakarsa da muqullin motarsa ya gewayeta yana fadin
“Saina dawo”
“Jibril” ta kirashi cikin bacin rai daya riqe mata wuya,amma saiya wuce baiko waiwayo ba.

Ganin ya makara da yawa ya sanya bai shiga dakin kowa ba yawuce,yayanke aranshi idan ya isa kasuwa yakira yaji lafiyar kowa,duk da yariga daya ga mmn ummi,mmn amir ce baiji motsinta ba,kuma ya kyautu ya leqata din kafin yafita kodon yanayin da take ciki.

Nan ta zube a kujerar falon nata ranta na mata suya,bata tsammaci zai bari mmn ummin tayi mata haka a gabanshi ba,kuma har tayi magana ya nuna ba wannan ne damuwarshi ba,damuwarshi wato cikinsa kadai?.

Ta jima zaune anan cikin bacin rai,tana saqa yadda zata rama abinda mmn ummin tayi mata,hakan yasanya har rana tasoma dagawa,lokqcin cin abincin yara da matan gidan yayi amma babu amarya babu dalilinta,kitchen wayam ba abinda aka dora,haka tsakar gidansu yana nan tun yadda yake daren jiya,baisamu arxiqin shara ba,wanda aikin amarya ne,kuma bata fito ba bare ta share din.

Dai dai lokacin mmn amir na daki kwance bayan ta idar da sallar walaha,bata wani jin yunwa sosai saboda tunda sassafe data tashi taji tana jin yunwar ta debi cake ta hada shayi mai kauri tasha abinta,tunda cikinta yasoma tsufa cin abincin nata ba wani mai yawa bane,shi yasa wanda tacin bai gama narke mata ba har yanzu.

Qarar wayarta yadauki hankalinta,tamiqa hannunta tadauko tana duba mai kiran,saita saki murmushi,din yanzun haka tunaninsa take taga bai shigo ba kamar yadda yasaba,har kishi yaso taso mata ko rufaida ce ta riqeshi?,sai tayi ta’awizi ta kori shaidan tayi istigfari,ta kuma gargadi kanta kan zato zunubi.

Sallama tasoma yi masa ya amsa mata
“Yanxun nake tunaninka,naji shuru yau babu motsinka nake cewa Allah yasa ya lafiya” ajiyar zuciya yasaki a boye,har kullum naya rasa samun wani abu dazai sanyashi farinciki daga bakin halimatunshi,kome yayi mata,kowanne yanayi suke ciki bata fasa nuna kulawa da damuwa dashi,daya daga cikin abubuwan daya sanya shima ko yaushe yakan qara qaimi wajen ganin yanuna mata kulawa kamar yadda take mishi,koda nashin baikai nata ba
“Nima kina raina,naso leqowa naga ya kika kwana keda baby,to na makara,ayimin afuwa” murmushi takuma saki
“Tunda naji shuru nasan babban lalurane ya tareka,babu komai yau da gobe sai Allah,ina kwana?”
“Lafiya lau,da fatan kin tashi lpy ke da babyn?”
“Lafiyarmu lau alhmdlh”
“To ma sha Allah,su amir basa nan bare na tambayesu,qiri qiri kin koremin yarana” murmushi tasaki kawai,don ita ason ranta ma yaran suyita zamansu a can,koda zasu dawo din gaskiya bata buqatar dawowarsu gida nan kusa,cikin nutsuwa da taushin harshe tace
“Ni na isa na raba yara da gidan mahaifinsu?,kawai dai nafi samun hutu da nutsuwa yadda ya kamata ne abban amir shi yasa,kuma nasan can din babu matsala,koda makaranta aka koma koda qafa suna iya takawa suje,tunda tamafi kusa dasu akan nan din” ajiyar zuciya yasauke
“Aishikenan,tunda anmin qarfa qarfa yana iya” murmushi tasaki mai sauti kadan
“A’ah wallahi,bankai wajen ba”
“Babu komai Allah ya raba lafiya dai”
“Amin ya Allah”
“Shikenan?,saina dawo?”
“To Allah ya tsare,ya bada sa’a,yayi jagora yakuma bada abinda aka fita nema”
“Amin ua hayyu ya qayyumu” ya amsa yana jin dadin addu’ar har cikin zuciyarsa,duk da wannan ba sabon abu bane wajen mmn amir din,abu daya dahar yau mmn ummi takasa koya daga wajenta,abu kadan xai hadasu tana kallo xai fita ma amma ba zata iya bude baki tace masa a dawo lafiya ba,ita a lallai saita nuna masa sai kuma yasan cewa taji haushi,abinda bai taba gani daga wajen mmn amir din ba,kome ya hadasu kome sukayi bata fasa ce masa a dawo lpy,ko Allah ya tsare.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button