Hangen Dala 1

Da wannan tunanin yakashe wayar yakira mmn ummi,ya kira wajen sau uku bata daga ba,tana gani kuma tana sane tayi dagawar saboda abu biyu,na farko tana jin haushi yafita bai leqo ba,gashi tana son amsar wasu kudade data shirya qaryar amsa daga hannunsa,nabiyu kuma batason ya mata magana ko fada kan dariyar data yiwa rufaida dazu,haka yagaji ya haqura da kiran tunda yafita haqqinta.
Har zai aje saiya tuna bai ajewa rufaida kudin cefane ba,amma sanin akwai kudi daya aje dakin yasa ya lalubi lambarta.
Dai dai lokacin tana kwance saman doguwar kujerar falonta,tasha tea da bread cup din yana aje gefenta,tunda yafita ko dakin bata samu ta gyara ba,tana miqe tana latse latsen waya abinta,charting take a grp dinsu wanda yake cike da qawayenta,tana ta basu labarin yanayin rayuwarta a gidanta,da kuma abinda yafaru dazu tsakaninta da bbn amir din,ashariya wasu ke qundumowa suna sake dorata bisa layin matakij da zata dauka,hirar tayi mata dadi,hakan yasanya zuciyarta yadan rage fushin da takeji.
Kiran bbn amir din yashigo,takalli lambar taja tsaki,tayi minimizing kiran takoma kan watsapp dinta harta katse,wani kiran yasake shigowa sannan ta daga,murya a dake tayi masa sallama ya amsa
“Afwa na sha’afa ban aje kudin cefane ba,ki duba qasan kayana akwai kudi ki dauki dubu daya”
“Dubu daya?” Ta fada cikin izgili izgili a muryarta,ya tsammaci jine batayi sosai ba,don haka yasake maimaita mata
“Eh dubu daya” tsaki taja yadda bazaiji ba ta kashe kiran,takoma grp dinsu tana gaya musu nawa ne kudin cefanen nasu,kasancewar kowa yasan yadda take cika baki da kurari kan bbn amir din sai sabuwar hayaniya ta barke,wasu na rainawa wasu suna babu laifi,kowa yashiga bata irin tashi shawarar,saita koma ta kwanta sosai tana sake duba saqonnin a tsanake daha bayan daya.
Dai dai lokacin da mmn amir tasoma jin yunwa,saboda haka ta katse carbin da takeja din ta yunqura tamiqe tafito daga dakin bayan ta aje hijabinta,kamar hadin baki mmn ummi tafito itama dauke da ummin tana magana ciki ciki a hade,da alamu mita take,usman na biye da ita yana kuka kuka
“A’ah,lafiya dan fodiyo?”mmn amir ta fada tana shafa kan usman din,ita kadai ke kiranshi da sunan wani lokaci cikin gidan,saiya maqe kafada cikin kuka sanda mmn ummi ta tura kitchen tashige
“yunwa nakeji”
“Bakaci abinci bane?,gashi har sha daya saura?”
“Inafa zaici abinci?,bayan babu abinda aka girka cikin gidan,zokiga kitchen din qwalam babu komai sai qonanniyar taliya” ta fada cikin daga murya ta yadda tasan rufaidan zataji.
“Toh,garin yaya?” Mmn amir tafada bayan taduba kitchen din ta tabbatar ba’a dafa komai din ba
“Oho,tsabar iskancine da iya shege,da kuma daurin qarqashi data samu wajen mai gidan,nina tabbata da nice yau a gidan na na kade idan na aikata haka,gwara ke da yake anayi dake tunda kin daure masa baya yayi yadda yakeso”
“Dakata,duk wannan bata taso ba,ko wani uzuri ne dai ya hanata fitowa,karki gaggawar hukunci” mmn amir ta dakatar da uta,don batason tasoma sakin zancan nan nata wanda idan kishin ya tsikareta kamar wadda aka dorawa wuta saman ka saita saukeshi
“Koma uban meye bari naje nagani” mmn ummin ta fada tanayin gaba xuwa dakin rufaida,da ido mmn amir tabita kawai tana addu’ar Allah ya kade fitina.
Sai data shige dakin sannan ta maido dubanta kitchen din,gaba daya yakoma wani irin tunda tasaki harkar girkin gidan,kamar yanzu da yake cike da kwanukan girki,saita duqa a hankali tana tattaresu waje daya.
Da qarfi ta bankada labulen dakin tayi tsaye tana duban rufaida wadda ke kwance dafa’an tana faman charting,ganin haske daya dadu a dakin yasanyata daga kai ta kalli bakin qofar,suka hada idanu kowacce ta tsuke fuska
“Ina abincin safiyarmu?” Ta jeho mata tambayar kanta tsaye,wani kallo ta watsa mata sannan tamaida kanta a charting dinta kafin ta bata amsa
“Ban dafa ba,don babu wanda ya ajiyeni”qarasa shigowa dakin mmn ummi tayi,wanda ada batayi niyya ba
“kamar yaya?,me kike nufi?,mu mugama dafawa mu baki kina lafe a daki keda miji kuci sannan yanzu kice mu bazaki dafa ki bamu muda namu yaran ba?”, sosai tatashi tazauna tana duban mmn ummin
“Kinga tsaya,karki cikamin kunne da hayaniya,abincine banga damar dafawa ba saboda haka ki samamin salama malama” sosai mmn ummi ta tunzura,ai kuwa cece kuce ya barke tsakaninsu,wanda hakan yaja hankalin mmn amir dake kitchen din
“Ya salam” ta fada tana miqewa daga durquson da tayi,bayanta ya amsa mata,tayi tsai donta huta tanajin kuma yadda harshe ke tashi daga dakin rufaidan.
A daddafe ta qarasa qofar dakin ta daga labulen tashiga
“Haba don Allah,meye haka?,saikace wasu qananun yara?,harshenku yacika gida?wannan aiba mutunci bane wallahi”
“Kinsan me wannan ‘yar rainin hankalin tace?” Mmn ummi tafada tana nunata cikin zafi,kafin mmn amir ma ta amsa ta gaya mata duka yadda sukayi,sannan ta dora da cewa
“To wallahi bata isa ba,yadda muka dafa muka bata itama saita dafa ta bamu”dariya rufaida ta sheqe da ita
“xakiga isar tawa kuwa,naga wanda ya isa yakaini kitchen”
“Zaki gamu da wanda kike ganin ya daure miki gindi kuwa” daga haka mmn ummi ta juya fuu tafice daga dakin tafada dakinta tasoma lalubar wayarta,yayin da rufaida tadauki wayarta tawuce bedroom dinta tana ci gaba da zagin mmn ummi gamida lalubar number bbn amir,tana ganin gwara tatareshi da zancan tun kafin yazo a rigata lauya maganar.
A falonta ta cimmata tazauna tanata huci gamida maimaita kiran lambar bbn amir
“Wa kike kira?”mmn amir ta tambayeta sabida sanda tafito ta fuskanci itama rufaidan bbn amir din take kira
“Shi wanda ya daure mata gindin nake nema yakwana da sanin abinda yafaru” kai ta girgiza tana duban mmn ummi,batasan sai yaushe zata soma gane dukkan lamura ba,idan rufaida farin shiga wadda batasan ciwon zamantakewar aure da ciwon jibril din gaba daya da qimarsa ba ita ta aikata,ita mmn ummi da yake uban yaranta kuma wadda tadan dauki wasu shekaru cikin mu’amalar aure,tasan ciwonsa yaci ace tayi?
“Yanzu abinda zaki aikata din kina ganin kinyi dai dai kenan?” Dubanta tayi cikin jin haushi tace
“Kamar ya?”
“Yanzu kinwa uban yaranki adalci kenan?,ya fita neman abinda zaici gaba da tufa miki asiri keda yaranki,amma ki rasa dame zaki saka masa saida kiransa ki daga masa hankali?,ke kina kira ita tana kira?”
“Auto,me kike nufi?,na qyaleta kenan tatakamu tabarmu da yunwa taci karenta babu babbaka?”
“Idan tabarku da yunwa baki da hannun da zaki sarrafa abinda zakici koda dai dai cikinkine?,ki jirayi dawowarsa idan yaso kya kai masa qorafin?”
“Au….to ko bakinku daya?” Da mamaki take duban mmn ummin harta gane hakan saman fuskarta,duk da tadanji nauyin abinda tafada din saboda ita kanta tasan ba hakan bane,amma da yake idanunta a rufe suke saita dora
“Idan ba haka bane toki qyaleni,don wallahi saina gaya masa yasan sa saninsa,ai dama duk qanda yasayi rariya yasan zata zubda ruwa,niba irinki bace dazan zauna inaji ina gani a cuceni na qyale,duk wanda ya cuceni saina qwaci haqqina koda tsiya koda tsiya tsiya ne ehe,tunda ya jajibo wata toya shirya tarbar duk wani qalubale”
“Allah ya bada sa’a” mmn amir din tafada tana miqewa tabar mata dakin.