Hangen Dala 1HAUSA NOVEL

Hangen Dala 1

Kitchen din takoma sharp sharp tayi jallop din taliya da tattasan leda,da yake gwanar girkice tayi dadi qwarai kuwa,ta diba tazubawa usman da ahmad tawuce da saura daki,donko gyaran dataso yiwa kitchen dinma saita fasa,hakaza tsakar gidan,takoma daki abinta ta sakaya qofarta.

Dai dai sanda kowacce cikinsu ta taqarqare tana zabga mishi kira,sam bai sani ba,wayar tana a silent kuma cikin aljihunsa yana fama da custumers,sai daya sallamesu sannan yasamu waje yazauna yaga kiran,hankalinsa yatashi ganin kira wajen sha biyar na rufaida da mmn ummin,saiya rasa ma wazai soma kira,hankalinsa ya tashi yana fatab Allah yasa ba wani mummunan abu bane yasamu iyalin nashi.

Yana cikin wannan taraddadin kiran rufaida yakuma shigowa,babu jinkiri yadaga
“Lafiya meya faru?” Shine abinda yasoma fada
“Mmn ummi tayi kiranka ne?”
“Me yafaru?,naga miscal dinta”
“Yauwa,kome zata gaya maka karka yarda da zancanta,idan kadawo gida zakaji komai” shuru yayi yana nazari,tunaninsa nason hasaso masa abinda ke faruwa,jin yayi shuru ya tabbatar mata bata fada masa komai ba,saboda haka cikin jin dadi tace
“Saika dawo,i lov you” ta katse wayar takoma ta kwanta abinta saman gado tana juyi hadi daci gaba da charting dinta.

Jin maganar da rufaidab ta fada yasashi jan mugun tsaki,ya gama hasashen komai,haushi yacikashi,wanne irin kira ne wannan haka na rashin tunani?,yana shirin maida wayar kiran mmn ummin yashigo itama,saiyaqi dagawa yamaida wayar yaci gaba da sabgoginsa,amma sai hankalinsa yagaza kwanciya,ya fiddo wayar yanemi mmn amir
“Lafiya lau,ba wani abu daya faru,kowa lafiyarsa qalau” tace dashi sanda ya tambayeta,don tunda taga kiran tasan bai rasa nasaba da daya daga cikinsu ta sameshi,jin amsarta ya kwantar masa da hankali,saiya sauke ajiyar zuciya yayu hamdala kana yace saiya dawo sukayi sallama,ta aje wayar tana lulawa cikin duniyar tunani da mamaki,daga bisani ta ture duk wasu guntattakin tunani taci gaba da lamuranta.

Hakanan taci gaba da kwanciyarta saman gadonta,batako motsa ba ballantana tafito,don ta riga data saba ko a gidan idan tahau online tasoma charting bata tashi saita kai intaha,kota cikinta batayi bare sauran lamura,tana baiwa wayarta da charting muhimmanci matuqa,koda qannenta suja dameta da hayaniya idan tana charting din takan iya makesu,shi yasa ba kasafai suke zama kusa da ita ba idan suka ganta ta sanya waya a gaba.

Har sha biyu da rabi na rana bata gyara dakinta ba bare gidan bare ayi batun girki,saida kamfanin wayar da take amfani dashi suka tura mata saqon data dinta yaqare sannan ta haqura tasauka,data duba balance dinta kuma na waya taga bazai isa ya siya mata data ba,anan taci karo da lambar wayar mardiyya(wadda suka hadu gidan lallen biki sukayi musayar number),rabonta da ita tun ranar dinner din mardiyyan dataje mata,sukaci dariyarsu ita da qawayen mardiyya na matar shamsudden din angon mardiyyan,kan taqi zuwa dinner din,suna ganin kawai tsorata tayi,tasan ba zata iya hada kanta da mardiyyan ba.

Yankewa tayi kafin tatashi bari takirata taji yaya ake ciki,don ita gata tana nan tana nata yaqin dasu mmn ummin,kuma tanajin a jikinta akwai nasara cikin abinda tasoma din,ba zata dauki wata wahala ko wani tsari ba,dole yadda takejin tafisu karatu,takuma fisu matsayi a gun miji to a harkar gidan ma tafita daban.

Bugu hudu ta mardiyyan ta daga wayar,cikin farinciki da walwala takama sunan rufaidan.

“Amarya,amarya” mardiyya ke fada cikin fara’a,dariya itama rufaidan tayi
“Amare dai,ya kike qawa,ya gida ya al’amura” cikin walwala tace
“Komai normal,al’amura suna tafiya yadda ya kamata,kefa?”
“To alhmdlhi” ta bata amsa a taqaice,duk da har yau ita abun bai mata ba,bata samu yadda take hasashe tasamu ba,kota samu sama da hakan ba.

Gyara zamanta mardiyya tayi sosai tana cewa
“Ai qawata duk matar da bata auri mai mace ba bata bata cika mace ba,ai ki shiga kawai inda za’a dinga takara,a goga dake kisam cewa eh yes kema macace kin isa,ke kinga yadda abubuwa ke tafiya kuwa?,fiye da yadda nake xato da tsammani?” Ta fada muryarta na cike da farinciki da kuma zumudi,gyara xama rufaida tayi cike dason jin lbarin
“Allah qawata?”
“Wallahi kuwa,ashe dai hasahenmu qawata haka yake,uwayen gidan nan idan banda gidadanci basu aje komai ba,sai uban haihuwa da tara yara,matar nan ban sake raina ajawalinta ba saida nashigo,kinsan wata biyu tabani?”
“Ke don Allah?” Rufaida ta fada cikin sigar tambaya da kuma mamaki,
“Wallahi nake gaya miki,tunda nazo gidan nan take bauta har nayi wata guda,bana komai kuma miji na wajena,yana hannuna sai yadda nayi dashi,ke ko bita kanshi ko kulashi ma bata fiya yi ba,kullum tana can tana dubgar aikin gida dana yaranta,idan zai kwana biyu bai leqa su ba bazata koda kira wayarshi ba bare ta nemeshi,idan yafito ma iyaka gaisuwa,ko zaman hira na minti goma batayi dashi,ni kuwa hakan yayimin na kame abuna tsaf,kullum muna qule a daka muna diban soyayya madararta” ta qarasa fada tana qyalqyalcewa da dariya,tayata rufaida tayi,tanajin lallai ashe ita tayi sake da yawa
“Waikinsan wani abu kuwa?”rufaida tasake fada
“Matar nan kamar babu zuciyar kishi a jikinta,kinga yadda take nan nan dani,saboda tasan saita hanyata zata samu fadar wajenshi,bari kiji wani rashin zuciya,randa nacika wata daya da sati biyu saura sati biyu ta amshi miji ko?” Kao rufaida ta gyada cikin zaquwa kamar mardiyya na kallonta
“Kawai shashashar saita tsiri tafiya garinsu,yanxu haka tana can,har kwanakinta sun shigo bata dawo ba,kota gajima tatafine gaba daya oho” ta sake sakin dariya,abun yaburge rufaida sosai,saita gyara zama itama ta bata nata labarin
“Tabdi,wallahi ki zage damtse,yaci ace matsayinki yafi haka,ki bude wuta kawai qawata” daga nan ta qara dora rufaida kan wasu shawarwarin irin nasu sannan sukayi sallama.

Aje wayar tayi tahau nazari,lallai saita sake bude wuta fiye da wadda tabude a baya,amma bari zata sake bude duk wani shafi nata,da wannan tunanin tasauko daga gadonta tasoma gyaran dakin tana duba agogo dake nuna mata qarfe daya harda rabi na rana.

_ina miqa fatan alkhairu a gareku,da kuma shuru da kukaji na tsahon wani lokaci,Allah ya zame mana jagora a duk lamuranmu amin_????️‍????️????️‍????️ *HANGEN DALA*????️‍????️????️‍????️
_Ba shiga birni ba_

©️®️ *Safiyya Abdullahi Musa Huguma*

Haske Writers asso ????

*BABI NA SHA BIYU*

 

*ZAKU IYA SAURAREN LITATTAFAINA A TASHATA TA (SAUTIN HIKIMA) DAKE A YOUTUBE,SAUQI GA MUTANEN DA BASU SON KARATU DA KANSU SAIDAI SAURARE,LITATTAFAN NAWA SUNE KAMAR HAKA*

*ALKAWARIN ALLAH*

*DAURIN BOYE*

*KUNDIN KADDARATA*

*MUTUNCIN MACE*

*DANGANTAKAR ZUCI*

_DA WASU SABBIN DA ZASU ZO MUKU NAN GABA KADAN DA YARDAR ALLAH_

 

Sai data kammala gyaran dakin nata sannan tafito tsakar gidan,batako damu da yanayin data samu tsakar gidan ba na rashin shara ba,saima harara data gallawa tsakar gidanbda qofofin dakinsu mmn amir taja tsaki,cikin quna quni tace
“Lallaima,rainin wayi,sunafa nufin girkina ne,nizan gwaggwafe nayi musu shara,toko tsakar gidan tsohona baxan iya tuna lokaci na qarshe dana share musu shi ba,idan sunaso suga gidansu dakyau saidai momiyo ko hasana su share(qannenta kenan)” daga haka tayi gaba tahau sabgarta.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button