Hangen Dala 1HAUSA NOVEL

Hangen Dala 1

Sanda almajirinsu yazo tabashi yamata cefane,taja kayan miyan ta aje takoma daki abinta,tana lissafi gami da tunanin me zata dafa da daddare,wanda bazata kunyata ba,sannan bazai wahal da ita ba,don itadin bawai ta wani iya kalolin girki bane ba.

Bata sake fitowa ba saida ana gab da sallar la’asar,tazo taja kayan miyan tahau gyarawa,aka kai mata markade tadora shinkafa da miya,wanda bata kammala ta ba sai da aka kira sallar magariba,akayi sallahr aka gama sannan tasamu gamawa,ta samu fulasai tazuba nata dana bbn amir,sauran tabarshi cikin tukunya,ba tare data yiwa kowa magana kan ta kammala ba ko suxo su diba,tashige wanka abinta,tana jin uwar gajiyar datayi saboda girkin,ko a gida idan ka ganta a kitchen tota baci,ko mamarta ta matsa mata saita shiga,ko babu kowa a gidan sai ita kuma an tafi anbar girkin.

Ranar Allah bai kawo dawowar bbn amir dawuri ba,sunyi baqi a kasuwa sun dan tsaidashi,hakan yasa harta kammala shirinta bai shigo ba,cikin wata doguwar riga streetgown wadda taba daga cikin qananun kayan data dinga siya tana adanawa saboda irin wannan ranar,riga ce mai hannun vest,wadda talafe tafidda duk wani tudu da kwari na jiki ta,hakanan daga bayan rigar an tsagata tun daga wajen agara har zuwa ramin gwiwarta ta baya,ta gyara kanta tafeshe jikinta da turaruka,sannan tadawo falonta tazauna tana kunna tv,cikin sa’a tashar tauraruwa sun saka waqa,saita qure sauti abinta,wanda yakarade gidan,takoma takwanta saman doguwar kujera tajawo wayarta tahau chartinga tana jin gajiyar aikin datake gani tayi yana ratsa qasusuwanta.

A qagauce take duba duka hirarrrakin da akayi bata nan,haushi tadinga ji,saboda ada tana daya daga cikin wadanda akeji dasu cikin duka grps din da take ciki,saboda yadda take particpating,amma sai gashi yanzu tana neman komawa kurar baya,sai ayita hira bata kusa sabida aikin gidan ko wani sanga ta babbn amir,haka tadinga jan tsaki tana maida amsa daya bayan daya tana wucewa,ba tare data lura da macene konamiji ne yayi magana ba,don duka grps dinta babu wanda tafita a ciki koda kuwa akwai maza,bare tayi tunanin sauya layin waya,sabgarta taci gaba dayi kamar yadda takeyi a baya sanda bata da igiyar kowa a kanta.

Kasancewar unguwarsu irin anguwannin da basa rabo da wutar nepa ne,koda sun dauke mintina qalilan suke dawowa da ita,hakan yasanya mmn amir ke matuqar cinikin lemo da ruwa,banda yanzu data sanya qalula saboda yanayin ciki.

 

Yana sanya qafarsa a tsakar gidan yagashi wani iri ba yadda yasaba ganinsa ba,babu kintsi babu shara,mamaki ya kamashi,saboda abune mai wahala yadawo gidan yasameshi haka idan ba wani taro ko sha’ani akayi ba,duka daga mmn ummi har mmn amir suna da tsafta,kada ma mmn amir taji labari,donko ummi bata kama qafarta ba,don wani lokaci itake tashi ta gyare gidan har harabar,tasamu almajirai su gyareta tsaf idan iskancin mmn ummin yamotsa ta biyasu da kudi,batabi ta kanta ko kadan,to amma saiyau yaga sabanin hakan.

Dauke kanshi yayi daga wannan nazarin,sautuka biyu suka karade mishi kunne,na qarar kida dana kukan ummi,mamaki ya kamashi,don bazai iya tuna yaushe aka kunna kida kamar haka na qarshe ba cikin gidan,saidai duk da haka kukan yarinyar yafi jan hankalinsa,saboda haka yanufi dakin mmn ummi kai tsaye.

Goye yasameta da ummi tana fama jijjigata,gefe daya ga usman da mubarak saman kujera xaune a takure,fuskar mmn ummin kadai xaka kalla kasan cike take fal da bacin rai,yayin da yaran suma kana iya karantar akwai abinda ke damunsu.

Bata amsa sallamarshi ba,saiya jeho mata tambaya yana nufarta da zummar amsar yarinyar yana cewa
“Meya sameta haka taketa tsala kuka da daren nan?” Tofa,dama mai kuka ne aka jefeshi da kashin awaki,kamar dama jira take,kasancewarta mace wadda bata iya shanye ko danne bacin ranta ba,hakanan bata iya nuna abu na kara ko alkunya ba,idan batason abu ko bai mata ba kai tsaye take fadi kota nuna gaba gadi
“Eh,ai dole kasameta tana tsala kuka,tunda an hanata abincin gidan ubanta kuma wuni guda sur me yayi saura?,ai kawai abinda yarage kuma inaga shine rufaida tace mu tattara kayanmu mubar gidan shine inaga abu nagaba” ta fada cikin fada,hasala da haqiqancewa,kai kace shiyacewa rufaidan ta aikata,ko kuma yana da masaniya kan abinda ta aikata din.

Dubanta yake cikin mamakin abinda yafaru,dakuma mamakinta ita kanta,kamar tana magana da usman ummi ko mubarak,duk da kusan idan dasabo yariga yasaba,sam mmn ummi bata iya furta lafuzza mai taushi ba,sai lokaci lokaci idan taso hakan,ko kuma tana da wata buqata daga gareshi,bata iya controlling fushinta ko bacin ranta,duk sanda yazo mata saita amayar,har takan manta a gaban waye ma take wasu lokuttan sai bayan ta gama
“Abinci kuma?,wuni guda garin yaya?”
“Shina kiraka na gaya maka dazu,amma dayake nidin bani da muhimmanci,muma baka daukeni a bakin komai ba baka daga wayar tawa ba,kuma nasan billahillazi daga dazun zuwa yanzu dawowarka ko kaffara bazanyi ba kaga kirana,amma ka gaza biyoni saboda bani da muhimmanci,na rantse da girman Allah da halima ce ko rufaida saika bi kiransu,ba zaka iya shanyewa ba” ta qarasa fada kuka yana qwace mata,ranta na mata suya,kishi sosai yake cinta ga baqincikin abinda rufaidan tayi musu wunin yau din,tana tuna yadda ya tilastatata sai data amshi girki a sanda take cewa ba zata karba din ba,gani take kawai cikin duka matansa itace koma baya,hakanan yafi tsanarta fiye da kowa.

Shuru yayi ransa na masa suya shima,sai a sannan yadubi su mubarak da sukayi tsuru tsuru suna rarraba idanu a tsakaninsu
“Kuje dakin ummanku,daga nan kuce mata tazo yanzu ina kiranta” duka suka amsa dato suka sauka suka fice.

Yana jinta tanaci gaba da kukanta da qananun mitoci,saiya ciro wayarsa yakira rufaida
“Honeyy,baka shigo bane har yanzu?”
“Nashigo ina dakin mmn ummi”sosai ta bata rau,ta qanqance idanu kamar yana gabanta
“dakin mmn ummi kuma?”
“Eh,kizo yanzu inason magana dake” daga haka bai jira jin me zatace ba ya katse wayar.

Jin yakira rufaidan zuwa dakinta yasanya ta hanzarin goge fuskarta,kana tahau kalle kallen meye ba dai dai ba cikin dakin,saboda wunin yau sau daya tak tayi shara tun safe,bacin rai ya hanata,haka take,aduk sanda ranta ke a bace,haka yake mata tasiri ya hanata aiwatar da duk wani abun kirki,hakanan sai taji bacin rai yashafi kowa da kowama har yaranta,haka take fama dashi har zuwa sanda zai dusashe da kansa.

Balaifi dakin,saidai duk da haka ba neat yake sosai ba,lokaci yaqure ba abinda zata iya gyarawa,saboda haka tazauna tana ci gaba da kumbura,yayin dashi kuma yayi shuru saboda nazari daya fada,idanunsa sun dan sauya launi saboda bacin rai,ko almajirinsa baya yarda matan gidan su bari da yunwa,bare ace yau cikin gidansa aka wuni da yunwa?,harda yaran cikinsa?.

Mmn amir ce tasoma shigowa,tasamu waje tazauna bayan tayi masa sannu da zuwq,duba daya tayi masa tasan ranshi a bace yake,tasan dama hakan zai iya biyo naya,saitaja bakinta tayi shuru,idanunta kan tvn dake aiki volume can qasa,duk da itama rabin hankalinta yatafi ga tunani.

Tsayin mintina kafin rufaida tashigo dakin,hakanan tafito sanye da rigar,ba tare data nemi dan kwali mayafi ko hijab ta saya jikinta ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button