Hangen Dala 1HAUSA NOVEL

Hangen Dala 1

******* **** *******

“Wai maman amir mu mmn ummi zata wulaqanta?,har ta ganmu ta dauke kai tawuce daki?haka ta koma?,to do n yaya zai qara aure shine me?,me za’a fasa?”
“Mtseweeew,kice fa kika damu wallahi,ni tayita kumburinta idan taso ma ta fashe,qarin aurene babu fashi sai yayishi ehe” murmushi kawai halima tasaki tana zama bayan ta aje musu kwanon abincin da ita da kanta tashiga kitchen tazubo musu,ganin mmn ummi dake da girkin bata da niyyar basu din,shuru tayi na sauraron qorafinsu da yadda kowacce ke zuba baqar magana kan mmn ummin,dubansu kawai take don bata data cewa,zuciyar musulunci da ilimin addini kadai daya ratsata yasanya taci gaba da mu’amala dasu,a shekarun baya babu tamkar ya maryam a wajensu,a sanda ya niyyaci qara auren babu abinda bata gani ba daga gunsu,basa boyewa har a gaban idanunta
“Na qagu wallahi maryam tashigo”
“Wai kinga matar yaya kuwa?,tabdi,wallahi yaya yayi zabe”
“Ke ai wannan kankat ce,tayi a rayuwa,ga ruwan mutunci zallarsa,bakiga yadda takesonmu muda umma ba”
“Kinga kyautar data aikowa umma da ita kuwa?,ke yaya kanshi fa yamato,donta iya soyayya”
“Nce gareta mafa,wallahi da yaya zai barta tsaf zata dinga fita aiki,amma tace masa ma ita tafison tazauna gida takula dashi” ire iren wadan nan maganganun dama wadansu wanda ba zata iya tunasu ba ba wanda basu fadi ba a gabanta,babu kara alkunya ko kawaici,sunsa qafa sun shure duk wani alkhairi nata kyautatawa da haba haba da take dasu,a lokacin ambaton Allah datake yawaita yi shi kadai yazame mata haske,uwa tagari kuma da take da ita tayi mata jagora,matakin farko data soma mata dannar qirji,ta kuma kwabeta,a yanzun taga alfanun hakan
“Wallahi maman amir ni yadda kike yafi komai burgeni” cewar jidda qanwar baban amir,sai a sannan tadago ta dubeta
“Kishi na hankali da nutsuwa ba irin nata ba na jakan mata,ai rannan rufaida ta gayamin komai,wallahi ta burgeni data rama abinda tayi mata” cewar jidda tana ci gaba dacin abincinta
“Indai rufaida ce dai dai da ita take,yarinyar da takejin quruciya da karatu akanta” dariya haula tayi
“Nifa harso nake naga ya zatayi idan rufaidan tashigo,gaskiya tana ruwa,maman amir kedai wallahi kinyi a rayuwa da kika iya kama girmanki,kaman baki da kishi” kai ta girgiza kawai tana fidda dan qaramin murmushi,sa’annan cikin nutsuwa ta dubesu
“Babu wata mace da bata da kishi,duk matar datace bata kishin mijinta toba shakka an samu matsala,kuma idan aka zurfafa bincike akwai wata a qasa,zan muku maganar daban taba muku makamanciyarta ba,abinda kawai zanja hankalinku akai shine,ku gane cewa dukkan mace macace,kuma ba’a cewa jifa idan yawuce kaina yafada kan uban kowa,koda baku da aure ke jidda kina dashi,kuma kuma wataran matan wasune,gidan wasu zaku je,cikin dangin wasu,Allah yasa kun fahimceni”
“Eh hakane,amma wallahi kawai dai duk wanda yadebo da zafine bakinsa,ni banga abun wannan kishi hakaba ina dalili?” Cewar jidda tana watsa hannu,sai kawai mmn amir din ta watsar da maganar tadauko musu wadda ta kawosun,wunin da za’ayi cikin gidan.

*BAYANA AWANNI*

Tunda ta kawo masa abincin ta tattarashi ta watsar,banda ma ‘yan nasihun da maman amir tayi mata da babu abinda zai sanya ta saurareshi,shima cike yake da ita,hakan ya sanya baibi ta kanta ba yaci gaba dacin abincinsa,yana wasa da ummi daketa sabgarta saman carfet,lokaci lokaci yana diban abincin yana bata da cokali harya kammala,yasha ruwa yadauke ummin ya karkade mata jikinta yadorata saman cinyarsa sannan ya dubeta
“Me dame kike da buqata keda yara,inajin saura baifi sati uku ko biyu ba tariya” wani kallo ta watsa mata,kishi na tokare mata a qirji,ta rasa ma me zatace masa
“Kaje ka qarawa amaryar inaga hakan yafi armashi”
“Ohkey” kawai yace ya saba ummi a kafada yafice,binsa tayi da kallo,watoma bashi da lokacin lallashinta kenan barema ya biye mata suyita ba ko zata samu sassauci cikin ranta.

Kai tsaye dakin mmn amir yanufa,tana kwance saman doguwar kujera sanye da doguwar riga mara hannu,yaran duka na zaune qasa suna kallon tv,sallamarsa yasa kowanne maida hankalinsa bakin qofar yana fadin abba,abba,miqewa tayi daga kwanciyar datayi tana gyara zamanta,bayan ya gama da yaran ya dubeta
“Sannu” yace da ita yana dubanta,murmushi tadanyi sannan tace
“Yauwa”
“Ammm….nace dame dame kuke buqata kedasu ahmad gaba daya dasu ummi” ganin ya bata dama yasa lissafa masa iya abinda take ganin tana da buqata din,aljihunsa ya lalubo ya qirga kudi ya miqa mata,hannu biyu tasa ta karba sannan tayi masa godiya,ya sake qirgo wasu ya miqa mata
“Wannan nasu ummi ne,a musu siyayyar duka abinda ya dace” hannu tajanye tana kada kai
“A’ah,ka bawa ummansu ina ganin ta fisu sanin me dame suke buqata”
“Karbi nan,nasan da itadin ai nabaki ko?,banason jan zance” haka tasa hannu ta amsa badon son ranta ba,ta sake masa godiya,ya dubi amir
“Dauki ummi ka maidata wajen mamarta ta soma bacci” ya miqe yadauki yarinyar,shima yarufa masa baya.

Kudin ta irga,ya wucema yadda ta tambayeshin,tasan zai isheta tagama duk wata siyayyarta harda ma qari a sama,saita hada da kudinsu ummin ta adana da zummar gobe tasamu mmn ummin,da alama tamasa halin nata ne shi yasa ya watsar da ita shima.

*mrs muhammad ce*????????️‍????️????️‍????️ *HANGEN DALA* ????️‍????️????️‍????️
_Ba shiga birni ba_

©️®️ *safiyya Abdullahi Musa Huguma*

*BABI NA HUDU*

 

Gidan babu kowa yayi shiru kasancewar yaran dukka sun wuce makaranta maman ummi tana dakinta wanda tun sape bata gilmawarta ba itam tana nata dakin saidatagama kintsa duk abunda xatai na ayyukanta sannna ta dauko kudin da baban amir yabata sannan tanupi dakin maman ummi akwance ta tarar da ita tana kallo ummi najin sallamarta tararrafo gunta tadauketa tana cewa xoki naushi dan uwanki na ciki yadda kikasaba sannann tai sallama takarasa parlourn tashi tai maman ummi tai tazauna fuskarta babu walwala maman amir takarasa tasamu daya daga cikin kujerun parloun tazauna tanacewa muntashi maman ummi murya acushe ta amsa tanacewa lafiya lau to madallah tafada tana mika mata kudin dake dake hannunta amsa tai sannan tace wannan kuma namaye maman amir tadubeta tace kayan siyayyar yarane jiya baban amir yabasu”
“Jiya da yaushe?”
“Sanda kike can kina sake kashe kanki wajen mijinki,mmn ummi bakyajin magana,amma Allah yagani nayi iya abinda zan miki,shine shaida” daga haka bata jira taji me zata fada din ba ta miqe tafice a dakin.

Da kallo mmn ummin ta bita takaici na cikata,wato kudin siyayyar ‘ya’yan nata ma yafi qarfinta?,yafi qarfin yabata da hannunta saiya kaiwa kishiyarta?,qwafa taja ta dauki kudin ta irga,saita rabasu biyu tana ayyana abinda zatayi dasu,rabi kawai zatayi musu siyayyar dasu,saura kuwa zubin adashinta zatayi dasu,ribar qafa kenan ta fada cikin ranta.

******** ****** *********

“Wallahi wallahi babu shegiyar da zanwa girki,girki?,ni nace ka qaro auren kenan,idan sunsoma su rube saboda basuci abinci ba” ta qarasa maganar tana kashe famfo gami da daukar botikin wankanta tashige bandaki ta banko qofar.

 

Shuru ne ya ratsa tsakanin baban amir da mmn amir dake tsaye cirko cirko,bacin ran mmn ummi yana kamashi qwarai da gaske,cikin halayen datake masa bai taba ganin daya daga ciki mmn amir ta gwada masa ba,koda a sanda take neman auren maryam din,kunya duka ta dabaibayeshi,musamman daya tuna sanda babu kunya ba komai ya baiwa mmn amir kudin cefanen abincin ‘yan jeran mmn ummin a wancan lokacin,yace lallai ta girka,a sannan batajin dadi ta gaya masa amma yarufe idanu ya caccaba mata magana,yana ganin kamar tsabar kishi yasanyata tace bata da lafiya qalau take,baiso akai girkin gidansu ne,azo aga kamar bai isa da gidanshi ba,ko kan gidansa ba a hade yake ba,kasa magana ya motsa zaibar wajen
“Ka kawo kawai sai ayi kamar na wancan karon” yajuyo yana dubanta,farinciki ne qasan zuciyarsa,saidai yana ga bai mata adalci ba ayadda tayi nauyi haihuwarta nan da satittika ya bata abincin masu jere,ga wadda takw ziqau ma tace ba zatayi ba inaga ita
“Ki barshi kawao,zankai can wajen gwaggwo sai ayi a kawo musun” ko daya batason yakai wajen mahaifiyarsa kafa wata sabuwar maganar kuma ta bullo,tasan halin surukar tasu qwarai da zafin rai da fada,,wani sabon bacin ranne kawai
“Babu damuwa,tunda anyi wancan wannan ma bazai gagara ba” kai yake jinjinawa,qimarta da nauyinta na kamashi,a sanyaye yace tabiyoshi daki ta karba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button