Hangen Dala 1HAUSA NOVEL

Hangen Dala 1

Kudi ya irgo masu yawa ya miqa mata,ta amsa tana dubanshi tare da kallon kudin
“Sauran kiyi amfani dasu” ya furta yana kallon idanunta,godiya tayi masa kana ta miqe ta fito,sai data nutsu ta lissafa kudin da zai isa ayi komai,sauran canjin suna da yawa ba laifi,data lissafa taga sun kai mata kudin datake na cikon da zata sauya plasma dinta.

******** ***** ********

 

Zaune take a falon qafafunta na amiqe,gefe wata matace wadda a qalla ba zata wuce shekara talatin ba,kana kallonta zakaga kamar da suke da mmn amir,hira suke jifa jifa har dayar ta jefo magana kan gidansu mmn amir din
“Yaushene tariyar amaryar taku ne?”
“Saura kwana goma inajin ko sati,don cikin satin nan masu jere xasuxo” baki ta tabe sannan tace
“Wannan karon kamar ba kishiya za’a miki ba anty halima,shi kuma mijinku haka Allah gada masa” itama nata bakin ta tabe
“To yaka iya da abinda yafi qarfinka?,idan fada yafi qarfinka ai wasa kake maidashi samira,wancan karon da hankalina yayita tashi me aka fasa?,meye kuma ya sauya?,tunda ya gingimo yakuma dauki aniya aisai ka tayashi da idanu da kuma addu’a ko?” Kai ta girgixa
“Haka yake,amma banga kina wani shiri ba” qaramin murmushi tasaki
“Nice kuwa me shiri,amma yanzu ta abinda yake cikina mu rabu lafiya nake tukunna,bama wannan ba,bari na dauko miki kudin plasma din nan ki tafi dashi,yanzu abinda ya rage kawai kiyi xancan labulayena da mutumin,kudin sun samu shi nake jira,yayimin masu kyau sosai don Allah kalar kujerun,zan dauko miki dinkunana ki tafi dasu duka ki ajemin”
“Amma dai anty halima aiko kala biyu kya dauka ko saboda zuwan amarya”
“Xan dauki uku ma,amma nikam yanzu batasu nake ba,ta lafiyata nake”
“Allah dai ya raba lafiya”
“Amin amin,don Allah idan baban abba zai barki kizo mana jibin ki tayani girkin ‘yan jeren,yaran duka suna makaranta kya tayani zama ma”baki samiran ta kama
” au wannan karonma keya hada da girkin?,bai baiwa waccar ba taji yadda kikaji?”
“To meye a ciki?,ko nayi ko banyi ba zaikai wani guri ayi,kuma a hadamu duka a zaga,sannan kuma babu wani abu da zai fasu,kinga ni mubar wannan xancan don Allah muje na lissafa abinda yarage na baki” daga haka ta yunqura tamiqe samiran ta bita tana sake jinjinawa juriya da qarfin halinta.

********* ***** *********

 

Tunda safiyar ranar bayan mmn ummi ta sallami yan makaranta tafito tasoma hada duka kayan girkin da zatayi amfani dasu,maman ummin nata shige da fice gami da sabgoginta,batace ma maman amir din kanzail ba,sai itama tadan bata iska don ta fuskanci yau a cike take fam,su kansu yaran sun daku kafin Allah ya taimakesu su wuce makaranta.

Duk wasu kan kayanta ta hadesu tsaf,tsinkenta bata bari tsakar gida ba,duka mmn amir din ta ankare da ita amma bata tanka ba,hakan yasake qular da mmn ummin,a yanzun tafi yarda da zanxan hafsa datace ita tabaiwa baban amir goyon baya,kuma tabashi goyon bayanne saboda su quntata mata don tazo ta taras da ita itama a gidan,ta wuce yafi a qirga amma ta rasa dame zata takali mmn amir din da zance,har daga qarshe tace
“Hmmm,sannu da aiki” saita daga kai ta amsa mata kawai taci gaba da aikinta
“Kekam da daurewa qarya qarqashi kike,yanzu masu zuwa yiwa kishiyarki jere kikewa wannan hidimar,wallahi ko ‘yar sarkin santanbul ce bata isa ba” murmushi ya kubcewa mmn amir
“Ba saboda su nake ba,saboda mijina nake albarkacinsa sukaci,kuma wannan din ba komai bane ni a wajena,tunda ba yanzu na saba yiba” sai ta tabe baki
“To madalla,Allah ya taimaka” bata amsata ba taci gaba da aikinta,a haka samira ta cimmata ta kama mata sukaci gaba.

Kafin lokacin isowarsu harsun kammala,tayi wanka ta sauya kayanta masu kyau wanda suka sake fito da ita dukda tsohon cikinta,tuni mmn ummi an dauki kwalliya kamar wadda aka gayyata wani babban taro,ta samu kujera ta dasa bakin qofar dakinta wanda yake fuskantar dakin amaryar,duk da yadda takejin zuciyarta kamar zata faso amma haka ta daure don tanason ganin tunqwal uwar daka,hakanan tanaso taga idanun kowacce shegiya da nasu salon.

Mmn amir kuwa tana daki suna hira abinsu da samira,tana ta taya samiran aikin duwatsu na hannu da akewa kaya beadwork,ba’a wani jima sosai ba sallamar baqin ta ratsa tsakar gidan,gaban mmn amir yafadi,saita kira sunan Allah tana tattara nutsuwarta,mmn ummi dake tsakar gidan kuwa wayarta a hannu tana danne danne,tana jinsu har suka qaraci sallmarsu suka shigo babu wadda ta tankawa,sai sukayi turus ganinta a tsakar gidan suka hau kallon kallo a tsakaninsu,daya daga cikinsu ce tasake maimaita sallamar waiko ji ne batayi ba ganin kota dago ta dubesu,wannan karon dagowa tayi ta musu wani banzan kallo ta watsar,ganin haka daya daga cikinsu taja tsaki tana cewa
“Muyi abinda ya kawomu,don da alama dakunan a bude suke” sanda suka juya zasu shige din mmn amir tafito.

A mutunce suka gaisa,wanda mmn ummi taji kamar ta shaqota,suna gama gaisawa takoma daki abinta,samira ta gabatar musu da abinci da ruwa takoma daki sukaci gaba da sabgarsu ba tare dako sun kao hankalinsu ko sun damu da abinda ke gudana a tsakar gidan ba.

A hankali xaman qaryar datayi a tsakar gidan yasoma gundurarta,duk wani abu da aka shigo dashi idanunta akai yake,a zahirin gaskiya rufaidan ta fita yawan kaya nesa ba kusa ba ko sanda akayi nata auren bare yanzu da yara suka lalata wani itama ta lalata wani,sai taji hankalinta yayi mugun tashi,lallai dole tasan abunyi,dole ta sabunta komai nata,dole ta tattara takoma daki har zuwa sanda yaran suka dawo daga makaranta.

Yadda suka wuni jere haka tawuni yawo tsakanin dakinta da tsakar gida zuwa bandaki,ranar kuwa yaran sunsha duka sosai,gashi dama babu islamiyya bare su tsira,abu kadan yaro zai mata ta kamashi ta kila ta kila,kusan a kansu ranar ta huce,saida suka guji suka gudo dakin mmn amir,wadda tunda tasaki labulenta suna ciki ita da samira bata sake ma fitowa ba bare tasan wainar da ake tonawa,ko abune take da buqatarsa a tsakar gidan takan aika samira ko amir yadauko mata.

********* ****** *********

“Yauwa nawa ne kudin lallen namu nida amaryar?” Zahra’u dake tsaye wadda tacire nata lallen ta fada
“Ku bada dubu da dari biyar harda baqin”
“Baji wannan amaryar ta musamman ce,ko nawa kikace a baki bayarwa za’ayi,angon ya tsaya mata,uwa uba gidan mutum biyu zata shiga itace ta uku,koba haka ba jama’a?” ta qarasa maganar dai dai sanda ta zaro kudin ta miqawa mai qunshi,kusan fiye da rabin dakin ‘yammata ne,amare da qawayen amaren,maganar zahra’un ta ruda dakin kowa da abinda yake fada,wata daga cikinsu dake zaune daga can gefe an gama sanya mata lallen ta tabe baki
“Mata biyu?,tabdi,wallahi saita tashi tsaye tayi da gaske,itakuwa meya kaita?,aini wallahi ban auren mai mata ma sam” wadda ke fuskantarta itama tata qafar da qunshin tace
“Hhhhh,lallai hajiyata baki hadu ba,ni nan da kike ganina wallahi idan bame mace bama bazan auri saurayi ba,kuma yanzu haka burin nawa zan aura,ai bari kiji na gaya miki…..” Ta miqe ta zauna sosai sabanin dazu da take kashingide
“Indai kin hadu kin cika mace,inda zaki nunawa duniya kedin kat ce,kiyi soyayya dame mata,ki guma mata baqinciki,tanaji tana gani halayen mijinta yasauya,ki karbeshi daga hannunta,ki morewa soyayya ya zama naki ke kadai,daga qarshe ki aureshi ki shiga gidan ki kafa sarautarki,ki watso taciki waje,idan kikaga wasa wasa ma ki hadota da yaranta”
“Shine magana!….” Rufaida ta fada cikin wani jin ixxa isa da ganin cewa tashiga layin wadanda suka cika mata
“Wannan dagani tafiyarmu zatayi kyau,badon lallene a hannuna ba damun tafa dake wallahi,amma bari nacire lallen ki sakamin number dinki,yaushe ne naki bikin”
“Cikin satin nan ne”
“Kash,naso ace akwai tazara daya yajewa dayanmu,amma duk da haka bata baci ba,kafin mu gama yaga amarcinmu zamu jone,zaki zomin koni naxo miki” dora bayani tayi
“Ke nifa tun kafin na shiga wallahi ta gama sanin matsayina a wajensa,ita kanta ta gama sallamawa,donko kishi dani bata isa ta nuna masa tanayi ba,ina kiransa duk sanda naga dama,wani lokaci ma ita zata daga,ta gaidani in amsa sama sama inashan qamshi,idan nasoma na datseta ince ta baiwa mamallakin wayar,ke wallahi saboda tasamu fada da soyayya a wajensa,data fuskanci saita kama qafa dani har kirana take tana gaidani,ta kuma bawa yaranta su gaidani,bari na taqaice miki zancan,ba yaranta ba har ita anty sama anty qasa take kirana dashi” dariya rufaida ta kwashe dashi,labarin ya mata dadi,har taji kamar dramer dinma tafi tata
“Dole muje dake wallahi,amma wannan matar tasa anyi jahila” dariya itama matashiyar me suna jamila tayi
“Kamar kuwa kin sani,daga primary aka liqa masa ita daga can qauyensu,tun bashi da komai har yayi arziqi,kinga kuwa yanzu dole yanemo ta gaban jirgi,kada babban abu ya tashi ta kwafsa masa” suka sheqe da dariya suda sauran wadanda kejin dadin hirar a dakin.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button