Hangen Dala 1

“Allah ya rufa asiri,amma dai kubi a hankali,bigiren da uwargida tahau wataran shi zaki hau kema,wala’alla tasu ma tafi taku kyau” wata mata dake tsaye tana zarowa me qunshi kudinta bayan ta cire nata ta fada,duk sai idanunsu suka koma kanta,
“Malama waya saka dake,nifa dama tunda na fuskanci kedin uwar gida ce ko zama kusa dake naqi,saboda haka ba ruwanki da sabgarmu,jeki ji da damuwarki”
“Sannu sannu dai bata hana zuwa,kuma *HANGEN DALA BA SHIGA BIRNI BANE* daga haka ko waiwayowa ta dubesu batayi ba ta dauki diyarta dake bacci tafice,nan suka dasa yi da ita,wanda daga bisani suka watsar kuma sukaci gaba da sauraren labarin da jamila take basu,wanda baqaramin dadi yakewa rufaida ba da sauran masu ra’ayi irin nata.
_muje zuwa masu karatu_. ????️????️????️????️ *HANGEN DALA*????️????️????️????️
_Ba shiga birni ba_
©️®️ *Safiyya Abdullahi Musa Huguma*
*BABI NA BIYAR*
Aqalla ya kusa minti ashirin tsaye gaban mudubin yana dudduba kanshi yaga inda baiyi ba a jikinsa,shaddace ‘yar ubansu ya saka sky blue,ba abinda take sai sheqi da walqiya,hakan hular kansa itama babu abinda take sai daukar ido,komai na jikinsa daya sanya mai tsadane,kasancewar jin kansa da yake yaudin rana ce ta musamman,kuma yanason ya fitar da rufaida kunya ita da qawayenta ranar dinner din kamar yadda tace.
Wayarsa dake gefe ce tadauki burari,da hanxari ya dauka yaduba,rufaidan ce cikin hanzari ya daga ya kara a kunnensa,yayin da fuskarsa ta yalwata ta kuma wadatu da fara’a kamar wanda aka yiwa albishir an ‘yantashi daga wuta
“Dear…inata jira fa”
“Karki damu baby ina kan hanya,ganinan zuwa karki fushi don Allah,yanzu ba lokacin fushinki bane kinsan ya….” Maganarshi ta maqale sanda yaga shigowar mmn amir dakin.
Kanta tadauke kamar bataji abinda yake fada ba din na,shi yasa sam bataso ma shigowa dakin ba a irin wannan lokacin donta kaucewa ganinsa da kuma kaucewa ganin abinda zai motsa mata kishinta,saidai ba yadda zatayi Allah ya qaddara saitaji din.
Hakanan ya diririce,yar kunya ta saukar masa,saiya hau kame kame
“A’ah,mmn amir ba zaku bane?” Murmushin qarfin hali tasaki tana zama gefan sabon gadonshi sakamakon nauyin da takeji cikinta yayi,wanda ta tabbatar an sauya gadonne saboda amarya,saidai bata taba nuna masa ta gane hakan na,mmn ummi ce tayi qaura da kwana a dakin,tace dacan bai sauya saboda su ba saidon wata,to tabar kwanan dakin,tanajinsu amma bata saka musu baki ba
“A wannan yanayin da nake ciki hutu nafi buqata aiko?” Ta fada don ta baiwa kanta kariya,don tanajin koda ace lafiya lau take bataga abinda zaya kaita wajen bikin ba,kai yashiga kadawa
“Hakane kam,haka ne,Allah ya raba lpy”
“Amin,dama hajiyace tace kafin ka fita ka bada sauran kudin cefanen abincin wuni,saboda ba lallai ka kwana gida gobe ba ko saboda baqi,da sassafe kuma za’a je ‘yan kaba a siyo kayan miyan”
“Toh…ba damuwa” ya saka hannunshi cikin aljihu ya fito da sabbabin kudi wanda ya tanada saboda liqi wa amaryarsa ya irgo ya bata,hannu biyu tasa ta amsa kana tamiqe ranta na mata suya,zuciyarta na zafi amma tana qoqarin ganin ta danneta ta hana mata tasiri,a hankali ta juya tafice,saiya bita da kallo kunya da tausayinta na ratsashi.
Dakin mmn ummi tawuce donkai mata kudin saboda ita hajiyar tace ta baiwa saboda ranar tafado ranar girkinta.
Zaune ta can uwar dakanta,saman gefan gado tama fuskantar mudubi,saman gadon baje yake da kaya kala kala,daga na kwalliya zuwa na sakawa,da alama ta bajesu ne tana zaben wadanda zata sanya ne,ta kuma gama zaba din,don lace ne ta wareshi gefe hadi da mayafin da takalmi masu tsini,awarwaraye xuwa sarqa da dan kunne.
Cikin mamaki mmn amir ya qarasa shiga dakin gamida sallama idanunta a kanta,daga kai tayi daga shafa jambakin da take tana amsa mata sallamar sannan ta sake maida kanta,ta mudubin mmn amir take kallonta,tasha makeup sosai wanda tajima rabonta dataga tayi kwalliya irin haka
“Da alama fita zakiyi ko?” Mmn amir ta tambayeta cikin shakku,da mamaki ta waiwayo tana dubanta
“Ya kike tambayata kamar bakisan meke faruwa ba,wai tsayama,ba zakije bane banga alamun kin shirya ba?” Kai mmn amir ta girgiza cike da mamaki,saboda abinda yafarun kafin yau bata tsammaci mmn ummi xatace zataje partyn ba.
Rufaida ce ta rarrabawa qawayenta number wayar mmn ummin suke kiranta suna zaginta tun randa sukayi hatsaniya da rufaidan ta wayar bbn amir din,a rana sai a kirata sama dasau talatin,data gane sune tayita mita har kunnen bbn amir din,toya danyiwa rufaidan magana,tace yace tana bata haquri,a hado da katin dinner guda biyu tace abasu tana gayyatarsu ai duka mijinsu ne.
Sam hakan baiwa mmn amir ba a nata tsarin,amma ga mamakinta saitaga mmn ummin yanzun na shirin zuwa
“Yanzu keda gaske kike zuwan xaki?” Sake waiwayowa tayi ta dubeta
“Qwarai kuwa,aiso nake naje naga shegiya da qawayenta,kuma na tabbatar zuwana zai quntata musu,ya hana bbn amir rawar gaban hantsi,sai naga tunqwal uwar daka”
“Kiga tunqwal uwar daka ko ko gano abinda zai tashi hankalinki ya hanaki barci?” Mmn amir ta fada cikin ranta,don tasan wanda yayi nisa bayajin kira,koda ta gaya mata baji zatayi ba,saboda haka ta aje ajiyar zuciya tana miqa mata kudin hannunta
“Allah ya kyauta,gashi inji hajiya tace zata kiraki” kudin ta harara kafin daga bisani ta amsa
“Nifa ku daina sakani cikin wannan sabgar taku,wadan nan sabbin kudinma da alama amaryar xai baiwa ya tsakuro a ciki ko?”
“Bansani ba wallahi,saidai idan kun hadu ki tambayeshi” baki ta tabewa mmn amir din sannan tace
“Yanzu ba zakije din ba?”
“Saikun dawo Allah yasa ayi lafiya a gama lafiya,amma ki dauki ummi kawai basai kinje da yaran ba bare su bata miki kwalliya”
“Kin kawo shawara kuwa” ta fada har cikin zuciyarta,ita kuwa mmn amir tayi hakanne saboda kada aje a tafka wani abun kunyar gaban yaran,batason duk wani abu da zai sakawa yaran negative tunani kan iyayensu ya dinga giftawa ta idanuwansu.
A tsakar gida akayi clashing da bbn amir da mmn ummi,sai aka hau kallon kallo,kowa da abinda yake saqawa a ranshi,ran mmn ummi fal kishi take dubanshi,ko ran aurenta gani take baiyi kwalliya irin haka ba,yayin da gabanshi ya fadi,yayi tsammanin ba zataje na kamar yadda mmn amir tace,yanzu ya zaiyi kenan?,ga rufaida nacan tana jiranshi,duk saiya daburce,duka basirarsa tadauke
“Na shirya” ta fada tana tsareshi da idanu
“Toh….toh,ina zuwa” ya fada yana juyawa da sassarfa yafita daga gidan.
Daya daga cikin abokansa yakira ya gaya mishi abinda ke faruwa
“Kaga kasan ya za’ayi?,bari nazo na tuqaku,idan yaso sai aje a dauko rufaidan ka zauna dasu duka a baya nina kaiku wajen” dan jim yayi saboda yana tunanin yadda zata kaya,yasan yadda rufaida taci burin lokacin nan
“Yanzu hakan xa’ayi?”
“Kana da wata mafiyar ne bayan wannan?,idan akace za’akai wata sannan axo a dauki wata za’a bata lokacine kawai”
“Shikenan,sai kazo”
Cikin minti ashirin murtala abokinsa ya iso ya daukesu a motar,suka zarce gidan kwalliya inda tacan za’a dauki rufaidan.
Yana zaune a cikin motar yakirata yace gashinan ya iso ta shaida masa gata nan fitowa,a sannan anata kiciniyar rufe mata zip din gown dinta,saita aika qawarta ta sanya mata jakarta da kayan data cire cikin motar kafin tafito.