Hangen Dala 1HAUSA NOVEL

Hangen Dala 1

 

Da sauri xahra ta dawo
“Ke rufaida?,garin yaya,naga kamar bashi daya bane,shida wata mata ne harda yarinya a hannunta”
“Mata kuma?,yarinyar hannun tata macace?”
“Eh ba zata wuce shekara biyu ba” wani mugun ashar rufaidan ta lailayo ta maka
“Amma bansan matar nan jaka bace sai yau,zuwa zatayi wajen kenan?,lallai lallai yau zatasan da rufee take zancan,rabi’ah qyale rigar nan basai kin zugeta ba,shi zai qarasa zugewa da kansa” ta fada tana qwace jikinta,saita ciro wayarta daga jaka ta kirashi,bugu daya ya daga,ta narke masa sosai
“Kaga kasa qawayena sunatamin dariya wai bakaji dani tunda baka iya shigowa ciki mu fito tare” sosai ta rikitashi,saiya hau kallon mmn ummi dake qame a gefe ta gefan idanu
“Haba dai?,bari naxo to” ya fada yana kashe wayar
“Ina zuwa” kawai yace musu ya fito,saiya zagaya gefan murtala ya masa rada a kunne sannan ya wuce.

Tare suka jero shida ita,mmn ummi ta juya don gyarawa ummi xama a jikinta ta hangosu,wani abu taji yariqe mata wuya,ta zuba musu idanu sanda suke tahowar,sarai rufaida taga cewar ta gansun,hakan ya sanya tasaka hannunta cikin na bbn amir gami daci gaba da janye masa hankali har suka kawo bakin motar,idanunta nakan maryam din a fakaice,don babu laifi kwalliyar datayin ta mata kyau sosai,bata tsammaci ta iya ado yakai haka bama.

Shiya soma bude murfin motar yashiga sannan rufaidan
“Thanks my zuma” rufaidan ta fada tana kashe murya,murmushin yaqe yayi saboda mmn ummi dake motar,cikin tabara saikace qaramar yarinya soma tittirjewa
“Shine kayi shuru ba amsa?,wallahi kaci bashi,zaka sani”
“Yi haquri karki tasarmin yarinya” mmn ummi ta fada cikin matuqar tunzura,tanajin zuciyarta kamar zata fito,saita dan dago tana duban mmn ummi fuskatta cike da murmushin cusa takaici
“Au,ayyah antyna,kiyi haquri ai bansan kina ciki ba,ina yini?” Ta gaidata tana jefa mata wani kallon raini.

Lallai rainin hankalinta yakai,ita zata faki idanun bbn amir ta dinga jefawa kallon banza,sannan ta gaidata daga bisani,dauke kanta tayi tayi banza da ita,sai bbn amir din da baisan me ake ba ya waiwaya yana duban mmn ummin
“Ana gaidaki fa maryam” juyawa tayi ta jefawa rufaidan harara da kuma kallon banza sannan tace
“Lafiya” sama sama cikin shan qamshi,hakan ya batawa rufaidan amma saita share saboda tasan cewa lallai zata fanshe.

“Zugemin dear don Allah,tun daxu muke fama amma yaqi” sai kuma ta dubi mmn ummi
“Ki haquri anty zan dan ari mujinmu xai rufemin zip” wannan qaton asharne yazo bakinta,amma wanzuwar murtala a wajen yasa ta kasa furtawa,don tana ganin mutuncinsa kamar yadda shima yake ganin mutuncinta,hakanan tanajinsa yana zuge mata zip din tana wani shagwaba gami da cewa
“Yimin a hankali dear da zafi”.

Maganar murtala yasanya mmn ummin taji kamar ta ciro zuciyarta
“Malama rufaida wannan shagwaba ai a bari mudan kauce ko?”fari tayi da idanu,maganarsa ji tayi kaman an qaramata qaimi ne
“Kai haba malam murtala,normal nefa,wannan aiba wani abu bane,na saba indai ina gaban dear,wani abun aisai an shiga daga ciki wannan kam ba wanda zaiji ba kuma wanda zai gani sai wanda yakai ido ko kunnensa”
“Hakane kam” ya fada yanason rufe maganar don ya fara shanshano wani abu.

Sanda suka fara tafiya qawar rufaida na gaba,hira suke ita da qawar tata suna kwasar dariya abinsu ganin kamar bbn amir din hankalinsa ya kasu kashi biyu,duk da tayi qoqarin janyr hankalin nasa donta cusawa mmn ummin haushi.

Suna gab da shiga wajen taron mmn ummin ta dora masa ummin datayi bacci saman cinyarsa
“Dan riqemin ita bari naje na kama ruwa nadawo” ta fada tana balle murfin motar tafice abinta,abun ya batawa rufaida rai sosai,don su kawai ake jira aga shigowarsu,ga qawayenta daga can qofa suna tsaye sun shirya kansu suna jiran shigowar tasu,sanda tasoma masa qorafin sunbar mutane na jiransu saiya dubeta
“Komu shiga ta tadda mu”
“Kan ubancan kayyasa” ta fada cikin ranta,a ranar auren nata,ranarta rana ta musamman kawai saiya wani sungumi ‘ya su shiga dakin taro da yarinya a kafada,dan hoton da zatayi na amarya a kafadar ango shikenan yasha ruwa yake nufi ko kuwa,sam ba xata lamunta ba.

 

Wayarta ta dauka ta turawa zahra dake zaune gaban mota tex,ba’afi minti biyar ba zahran ta juyo cikin nuna kulawa
“Ita kanta babyn kidan gurin nan zai tasheta,gashi da alama taji dadin baccin,ko zaka kawota na sami zani na goyata ta kwanta sosai?”hakan sai yaga kamar yafi,hakan ya masa,saboda haka zahra ta zagayo ta amshi ummi,yayin da su kuma sukabi ta cikin ayarin masu tarbar amarya da ango suka dunguma dakin taron.

Sai data tabbatar ta bata lokaci me yawa sannan tafito daga inda take boye,dab da zata wuce securityn dake wajen taji ance
“hajiya,ko wannan diyarki ce?” Da sauri ta waiwayo,saiga ummi kan kafadarsa tanata baccinta,wani irin bacin rai take taji ya sauko mata,ranta yabaci sosai,har wani daci daci takeji saman harshenta,qarasawa tayi ta amsheta tana tambayarsa wanda ya bashi ita
“Watace ina tunanin qawar amarya ce”
“Na gode” tace dashi tana amsar ummi,cikin bacin ta durfafi dakin taron tana qiyasta cin mutuncin da zata yiwa bbn amir da rufaidan ma gaba daya,ita zai wulaqanta?,ya bada ‘yarta kuma ‘yarsa ajiya?,yana nufin budurwarsa ta fita tafi ‘yarsa?,ashe haka bbn amir din yake sai yanzu ainihin kalolinsa suke dake bayyanar mata,lallai da gaske,bataga laifin matan da suke cewa duk wadda ta riqi namiji uba ta mutu marainiya,da gaskene namiji hankakane,gabansa fari bayansa baqi,ko a mafarki bata taba tsammatar haka daga baban amir ba,ta zaci ko a fuska kadai ta nuna batason abu ya barshi kenan har abada,ashe ita biqin jegon jaka takeyi.

 

Gab da xata shiga hall din daya daga cikin samarin dake gadin qofar yasa mata hannu
“Hajiya ina zuwa?” Daga kai tayi tana dubanshi cikin mamaki
“Ciki mana,ina zan shiga idan ba nan ba”
“Saidai ki koma gaskiya,an hana shiga”
“Kamar yaya?,kasan me kake fada kuwa?,kasan wace ni?” Dariya taga sun sanya gaba dayansu bayan sun hada idanu
“To hajiya ko wacece ke kuwa saidai ki haqura ki koma”.

Nan ta tsaya musu bayani amma suka watsar da ita a wajen sukaci gaba da hirarsu,abinda yasake bata haushi yakuma daure mata kai shine bayan ita wasu da yawa sun shige,ta musu magana sukace sudin ai an gayyacesune ansan da zuwansu,wani azababben bacin rai yadinga cinta,kunyar yadda suka tozartata ya kamata,saita koma inda suka aje motarsu,abin takaicin a rufe take,murtala kenan shima yana ciki.

Wayarta taciro a gaggauce tasoma kiran bbn amir,lallai ba shakka dukkansu saisun gane kurensu,da saninsa kenan za’a wulaqantata?,ta kirashi a qalla ya kusa sau ashirin saidai bai daga,kasancewar yawa da qarfin hayaniyar dake wajen ba zata barshi yaji ba.

Kamar zata saki kuka haka ta rungume ummi ta soma takawa zuwa titi donta samu abun hawa ta wuce gida,don ba zata iya zama har sai an tashi ba,bacin ran da takeji ita kadai tasan irinsa,inda Allah ya taimaketa da jakarta ta fita,da a cikin motar aka kulle batasan ya zatayi ba.

 

Kai tsaye dakinta tawuce ba tare da kowa yasan tashigo ba,yaran duka suna dakin mmn amir sunma yi bacci abinsu,kayanta tasoma cirewa tana watsarwa,jin zuciyarta take kamar anyi gobara,xani tasamu ta daura ta zauna jiran dawowar baban amir.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button