Hangen Dala 1

Awa guda harda rabi wayarra tasoma ruri,data duba saitaga baban amir ne ke kira,wani mugun tsaki taja,tanajin wayar harta gama rurinta ta katse,ya sake kira har sau biyu amma wayar bata isheta kallo ba bare ta daga.
Qarfe sha biyu da rabi na dare yashigo gidan,sanda yarufe qofar tana jinsa,miqewa tsaye tayi tana sauraren qarasowarsa.
A qofar dakinta yaga takalmanta,hakan ya alamta masa ta dawo kenan
Dakin mmn amir yashiga ya taddata sunyi bacci duka ita da yaran,yau duka yaranma na dakin,mazan na falo ita da matan suna uwar dakinta saman gadonta,saiya koma da baya ya rufe musu qofar yadda ya ganta ya durfafi dakinsa.
Yana tsaka da cire shaddar jikinsa ta bankado labulen tashigo,saiya daga kanshi yana dubanta tare da karantar yanayinta,har saman fuskarta takejin zafi saboda bacin rai,ta tsaya gabanshi tana dubanshi.
“Basai kayi haka ba zaka tabbatarmin da cewa kai namiji ne,lallai ka nuna halinku da ainihin kalarku,jibril kai munafiki ne maciyin amana da zakaci mutuncina,ku hada baki da budurwar da zaka aura ku wulaqantani,nayi nadama da danasanin aurenka,ba abinda zance tsakanina dakai sai Allah ya isa!” Ta qarashe fada cikin daga murya da zafin rai,daidai lokacin da wayarshi ta dauki ruri,hannu yakai zai dauka tayi hanzarin rigashi kana ta daga tasa handsfree ganin sunan rufaida
“Dear,na manta kayana dana cire a motarka”
“Allah wadaranki kwarkwasa fidda me giji,baqar daga qarshenki ya kusa zuwa” ta fada tana katse kiran,sannan ta daga wayar zata kwadata d qasa,duk kuwa da cewa tasan tsadarta sarai,da hanzari ya tsaidata
“Karki soma,bani wayata!” Ko kadan bata saurareshi ba ta daga wayar ta makata a qasa,take ta tawarwatse saman tiles din.
Cikin bacin rai ua durfafota,zaginsa da fasa wayar suka hadu suka masa zafi sosai
“Idan ka iso karka barni da raina” ta fada tana tsaye qyam tana jiran qarasowarsa,yana isowar kuwa ya dauketa da wani lafiyayyen mari daya sanyata sakin qara saboda yadda ya ratsata,take rigimar ta sake zama sabuwa,ta soma masa jaye jaye cikin dakin naduk abinda hannunta yakai tahau bannatarwa.
Wannan qarar ita tatashi mmn amir,cikin tashin hankali ta fito daga dakin ta nufi dakin bbn amir din inda tajiyo hayaniyar tana tashi.
Daidai lokacin daya sake daga hannu xaikai mata mari mmn amir tashiga tsakani cikin hanzari,wanda kadan yarage yasameta
“Bban amir,meye haka?,meya sameka?”
“Ki qyaleshi ya aikata abinda yayi niyya,zai auro wata dama babu abinda bazai aikata ba!” Mmn ummi ta fada da madaukakin harshe,fuska jazur,saita waiwaya tana dubanta sanda bbn amir yace
“Idan bata ficemin a daki ba zan aikata duk abinda yazo raina” qin fita tayi sukaci gaba da sa’insa,harsai daya kusa sake kai hannu jikinta sannan mmn amir din tayi nasarar fitar da ita.
Cikin fushi yake furzar da iska me zafi,yasamu gefan gadonshi ya zauna yanajin yadda kanshi ke sake daukar caji.
Gefan gadonta ta zaunar da ita sai kuma mmn ummin ta fashe da kuka tana rufe fuskarta,ji take gaba daya duniya ta mata zafi,kamar duk wata qofar walwalarta da farinciki an tosheta,tsayawa kawai mmn amir tayi tana dubanta,tome xata gayawa maryam?,kome zata gaya mata ta jima da gaya mata shi,ita kanta tagaji da ganin wannan bala’in,tayi a qalla minti ashirin tsaye a kanta kafin tace
“Allah ya kyauta,ya sawwaqe” ta juya tafita daga dakin.????️????️????️????️ *HANGEN DALA*????️????️????️????️
_Ba shiga birni ba_
©️®️ *Safiyya Abdullahi Musa Huguma*
*BABI NA SHIDA*
Tunda safiyar garin asabar ta waye tasake shiga fita hayyacinta,tunda ta idara sallar asuba ta kasa komawa bacci,sai zirga zirga da take tsakanin tsakar gidan soro zuwa nata dakin,idanunta kacokam yana kan dakin baban amir,wani mahaukacin kishi takeji,yanxu nan da wasu awanni kenan yaxama nasu su uku?,tashin hankali,saita dora hannunta aka tana neman inda zata sanya zuciyarta da ranta taji dadi,wani irin radadi da zugi gamida qunci takeji cikin zuciyarta,saita dauki wayarta ta kirayi hafsat.
Bugu hudu ta daga
“Ya akayi mmn ummi,mun tashi lpy”
“Babu batun tambyar lafiya game dani,tunda kin san babu ita,yaushe zaki shigo,wallahi hafsat jin gidan nan nake kamar wata qiyamata ko lahira”
“Karki damu ina sallamar babansu minal zan shirya na taho”
“Don Allah karki dade”
“In sha Allahu” aje wayar tayi tana furxar da iska daga bakinta.
Wayar tatace tasake ruri,data duba sai taga lambar qanwarta ce,ba jinkiri ta daga sai taji muryar mahaifiyarta,kuka ta sanya
“Meye haka maryam?”
“Umma yaune daurin auren fa?”
“Sai kuyi haquri ai,haka Allah ya dora muku”
“Don Allah umma kixo,don Allah”
“A’ah,nikam bazanzo wannan gidan naku ba,zandai turo miki ruqayya da zakiyya,sai yayarku duka zasu taho tare”
“Toh umma”
“Zasu taho miki da saqo,saiki sawa ranki haquri,tunda haka Allah ya dora masa” daga haka sukayi sallama,saita danji sanyi da maganar da sukayi da ummantata.
Qarfe takwas tasoma jin motsin yaran a tsakar gidan,tun cikin satin suma yaran ta sallamasu gaba daya,mmn amir ce keta hidima dasu,hattasu abun ya shafesu,ita kuwa maman amir ko a jikinta,saboda kai kawon yaran da kula dasu da takeyi ya dauke mata hankali gami da debe mata kewa da bacin rai,idan tana tare da yaran sai taji ta manta da wasu abubuwan.
Miqewa tayi ta isa bakin window tana leqen abinda yake faruwa a tsakar gidan,mmn ummin ce zaune saman kujera ‘yar tsugunno,gabanta sabbabin shaddodine ruwan omo,saman cinyarta wasu daga wandunan yaranne tana saka musu tazuge,mubarak na tsaye a kanta da alama yayi wanka ya shafa mai yana jiran ta gama saka masa tazugen tabashi ya saka,yayin da mmn amir din ke aikin tana gyarawa hanifa wankan da takewa usman.
Wani baqinciki da bacin rai ya kamata,wato har wani anko ya yiwa yaran na xuwa daurin aurenshi kenan,ita batama sani ba?,kafin tayi kowanne yunquri baban amir din yayi sallama yashigo gidan,hannunshi dauke da wata shaddar kalar ta yaran,da alama tashice ya amso.
Qurawa fuskarshi idanuwa tayi sanda yake qarasowa gaban mmn amir,fuskar da ada babu wata fuska da takeso da qaunar gani amma a yanzu babu fuskar data tsana take jin haushi da takaicin gani irinta
“Sannu da aiki maman yara” ya fada yana murmushi,har cikin ranshi kuma yanajin dadin yadda take shirya yaran zasu daurin auren tare dashi
“Yauwa” ta fada ciki ciki fuskarta sam babu wannan fara’ar daya saba gani,duk sai yaji jikinsa yayi sanyi,tayi qoqari matuqa kuma tana kanyi,yasani cewa baiwa Allah yayi masa da uwar gida,wadda ta tsaya kai da fata wajen ganin ta hade kan gidan waje daya,ya tabbatar da maryam ce uwar gidansa tofa sai abinda hali yayi,yasani sarai cewa suk maigidan da yayi rashin dacen uwar gida toya kade ya gama yawo,duk wadda zai aura daga baya mawuyacine idan batayi koyi da wasu dabi’u nata ba,uwar gida itace ginshiqin gida,itace kuma kamar turken mai gida da dukka wani ahu daya mallaka,idan ka dace a ita saika godewa Allah.
Yanayin dayaga fuskarta yasa ya gaza wucewa,saiya soma kame kame,inda daga bisani yac”wannan zaman bazaki gaji ba?,kawo tazugen na qarasa saka musu kije ki huta”kai ta kada
“A’ah,barshi kawai,aiba lokacin hutu bane yanzu koda naso na huta din” haka ya tsaya yana ci gaba da tayata gyara kayan yaran har kowa ya sanya nashi sannan ya shige dakinsa donya shirya shima,ta bishi da kallo tanajin wani bacin rai da kishi yana taso mata,ta dauke idanunta taba karanta “hasbiyallau la ilaha illa huwa,alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim”.