HARIJI COMPLETENOVELS

HARIJI 1 & 2

HARIJI COMPLETE HAUSA NOVEL

     *HARIJI* 

(Original Romantic love story)

  *Shimfida*

Ana yawan Tambayata banbanci tsakanin Jarababben namiji da harijin namiji finally a wannan littafin zan banbance mana tsakanin zare da abawa
Matan Aure zallah in budurwa ko namiji ya karanta ban yafeba
In kika zageni kema allah ya isah.

*Gameda labarin*

Labarin Hariji kuma jarababben namiji ,ya kasance juyayye uncontrollable wai meye maganinsa…kuma wata mace ce zata iya masa?

Indai ke matar aurece ko bazawara ina baki shawara da kibi littafin nan kar kiyi missing ,zaki qaru da yawa Allah ka barmu da mazajenmu

In the name of Allah

Free page 1&2

The Agony of destiny????

Tsugune take qarqashin murhun duwatsun dake tsakiyar gurgurarren gidan Jan lakan tana hura wutan da bakinta cikeda qosawa
Shikam wutar banda bulbulo da wani irin hayaqi me toshe qofofin shaqar iska ,dasa idanu tsiyayar qwalla na zallar iccen damuna ba abunda yikeyi

Rumtse idonta tayi ta bude saboda sarewa da tayi wutar baida alamun kamawa، tsabagen wahalallen sullutayen iccen dake jikin murhun da suka jiqe jagwab ba alamun zasu ruru

Miqewa tayi tana gyara daurin dankwalinta sannan ta kama ha6ar zaninta ta sharce hancinta
Idonta ya kada yayi jaxur

Dakko wayarta tayi rakani toilet tana duba lokaci
Takwas ya gota Na safiya

Cikin sharar qwalla ta d’auki buta ta wuce Bayan d’akunan gidan ta wanko jikinta ,dukda hururuwan sanyi da akeyi hakanan take kwara ruwan mai kama da qanqara

Cikin gaggawa ta shafa Vaseline er had’in gida

Ta dakko uniform masu ruwan ganye ta saka ta saka qaramin farin hijabi ta d’aura wani tsohuwar abaya baqa ta saka baqar takalmi mai rufi

Sannan ta dage tattararren labulen d’akin

“Na wuce ummah”

“Au tafiya xa kiyi ummy bazaki tsaya ki karyanba”

Muryarta rawa ya kama yi alamun za tayi kuka

“Ummah zan makara kuma wutan yaqi kamawa tun shida da rabi ga yanzu takwas da rabi’

To ai Cikin ki qaryan kafiya kikeyi ,acedai ga en uwanki sun dawo da banqararrun kaji yaji yajin cittah ke kice dole bazaki ci abunsu ba baki horu bane”

Shiru tayi mata haka tayi mata sallama ta gangara general hospital dinda take aikin voluntary a qasa in wata yayi maaikatan suna dan sammata wani Abu

Sashen d’akin haihuwa ta nufa da gaggawa ta shige ba tareda ta tsaya a wajen nurses station dinba bare metron din ta ganta tayi mata fad’an makara

D’akin da suke ajiye kayansu ta shiga ta cire jallabiyar da takalmin ta ta zura wani soson takalmi da ake masa laqabi da shaku shaku

Sannan ta shige d’akin kar6an haihuwa

“Yawwa TBA(traditional birth attendance) zo ki gwada mana VE (vaginal examination) din matar nan”

Wata nurse tabawa ummy umurni,tana nuna mata wata hajiya da zatakai shekaru talatin da biyar

Da sauri ta zari safan hannu ta je ta wanke hannunta ta saka safan ta Debi antiseptic ta kwara a gaban matar sannan ta nitsa hannunta tana laluben saman kofar cervix din

Jimawa kadan ta zare hannunta ta fito tana rubuta findings dinta a folder din client din

Sannan ta chanjawa matar kayanta zuwa na haihuwa ta kaita delivery bed ta kwantar da ita
Ta dakko wani Leda me belt ta d’aura mata belt din asaman cikinta ledar a kasan duwawukanta

A nutse ta fara harhada kayan haihuwar ,wannnan ya tabbatar ma da matar haihuwarta yazo kenan


Bayan awa daya TBA ummy ta yaye screen din da ya kare matar da ta haihu ,ta tafi ta ajiye fine baby girl din akan scali ta gwada nauyin jaririyar sannan ta wuce tana gogewa yarinyar jikinta da olive oil

Saida ta kimtsa yarinyar da uwar tsaf sannan ta nado baby cikin showel ta fitoma da mijin matar gurin zaman relatives d’in

Wani qasurgumin Alhaji ta gani kuma da gani naira da boko ta gama tsumasa yina safa da marwa yina tsatsafe zufan goshinsa

A hankula ta taka gabansa tana rungume da babyn

congratulations Mr. Your wife gave birth to baby girl

(Ina tayaka murna ,matarka ta haifi d’iya mace)

“Mace ko maza”ya fad’a a qagauce

Mamaki abun ya baiwa ummy ace matarka ta haihu amma kana tambayar mace ko maza da yawa

“Sir macen dai guda d’aya” ta fad’a tana dan sakar masa da murmushin tabbatarwa

Kallonta yayi ,irin kallo mai ma’anoni iri iri
Sannan ya doka mata tsawa
“Ke !
Sa idonki cikin nawa ,dama Ku unguwar zoma kun yi qaurin suna wajen Satan jarirai…me kike nufi zaki fitomun da yarana maza biyu ,ko ko kuwa sai nakai zancen sama…?”.

Mamakine ya kama ta sosai,a take ya fara bata tsoro ,ganin yanda a take fuskarsa ya hade zuwa ruwan rikici da tashin hankali

A hankali ta fara ja da baya da baya ,yina biye da ita har suka kai gaban nurses station d’in

Murya ya soma bud’ewa yina zuba ruwan bala”i yina qoqarin qwace yarinyar a hannunta ,a yanda ta lura dashi tasan tabbas zai iya buga yarinyar da bango ,hakan yasata qanqame yarinyar ta soma kuka

Cikin fushi metron Abimaje ta miqe tana kallonsu duka

Wai lafiya kuwa…nan fa asibitine ba wajen tashin hankali ba in fitina ya kawoku cikin sauki Ku futa waje kuyi”

“Karki raina mun wayo kinji…ko a fitomun da twin gentle babies dina ko kuwa inyi qarar asibitin gabad’aya


A hankali qaramin case ya zama babba police har sun shiga maganar ,allah sarki ummy en sandan na zuwa suka saka ta a motansu da sauran midwives din da suke on duty

Nigeria gajaniya ,shigarsu be wuci da awa biyu ba duk aka fiddasu itakuma aka wuce da ita cell ،zata zauna a ciki har sai an gano inda jariran suke ko kuma ranar shiga kotu yayi,don har ya shigar da qara kotu


Qarfe Tara Na Daren ranar tana takure a cikin cell da baqin duhu ga kayanta masu duhu hakan ya qara jawo hankalin saurayen wajen dawowa kanta ,banda kudin cizo da suke watsowa daga saman silin din kamar zasu tsotseta danya

Ihu take kurmawa tana bibbige fatar jikinta
Hakan yasa wata er sanda leqowa da er iccenta a hannu

” yi mana shiru makira ,kina er talaka ana hada baki dake kuna sace jariran mutane to yau dubunku ya cika …gwara kiyimun shiru kafiin in amso makulli inzo in lallasaki”

A wajen reception din kuwa Hajara yayan ummy ne da akafi yiwa laqabi da keken maza ta shigo tana rangaji cikin wani matsatsen siket da Riga na atamfa ,dankwalin kayan ta riqesu a hannu da jaka mayafin rabin kanne kadai ya rufe da mayafin kayan

Tana tafe tana rangaji nonuwan ta na boosting suna bajewa a cikin breast cup duwawukanta suna wani irin girgiza amma dukda haka ta tattaro duwawun ta hanyar Jan siket din sama zuwa qasan duwawun nata

Zuwa tayi gaban wani dan sanda dake da alhakin sakaye mutane a Bayan kanta

“Officer ,inspector garba na ciki kuwa?”

Ta tambayesa tana karkada idanuwa tana faman taunan cingam,yina bada sautin qaran qarararas

“Yina ciki shiga kawai hajiya”
Godiya tayi masa sannan ta fyallo #500 ta basa

Yina godiya yinabin gima giman mazaunanta da kallo yina had’iyar yawu maqollatom wuyarsa na mommotsawa

Sarai ta lura da dauke wutarsa .don haka da gayya take Dada mommotsasu har ta shige

Knocking ta danyi sannan ta shige ciki tana wani irin cat walking kamar sardines

A nutse taje gaban tebur dinsa ta ranqwafa tana watso mata ba Shanunta a saman fuskarsa

“Barka da dare officer zan iya zama ?”

Bul! Yaji hajiyarsa???? ta motsa ta cikin wandon uniform dinsa

Washe ilahirin haqoransa yayi waje sannan yace

“Ahhh zauna mana ” ya fad’a yina nuna mata kujeran gabansa amma kyar idonsa suke kan Na shanunta baisan ko qyaftasu

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button