HARIJI COMPLETENOVELS

HARIJI 11 AND 12

Free page 11&12

Alheri writers Asso.

By…Oum Aphnan

Masu zagina na barku da illalah akwai madakata ,so if u lyk ki cigaba da zagina ohum bayi tsiro ????‍♀️Amma ki sani Bana fada a social media ,don’t allow me to start ta kanki….oh allah is it by force ehennn?so oum Aphnan ta dasa alkalaminta no going back ,so don’t exhaust ur time jareee????

Ana qare qarar su ummi ,en sanda suka taho da Ankwa suka umurceta da ta miqo hannu,a sagala mata a wuce da ita gidan yari zuwa lokacin zaman kotun na gaba….

hawayen bakin cikine ya fara tsatstsafo mata a kwarmin idon ta,talaka! Talaka bawan allah ,ace yau duk bautar da tayiwa likitocin asibitin nan ba Wanda zai tsaya mata? Haba wato kowa yina tare da Kaine zuwa wani lokacin gazawa.

Girgiza kai tayi kurum ta miqa masu hannun suka saqala mata ,er sandar haka ta shiga ingixa qeyarta tana tangadi ,tamkar zata kifa

A tarikhin rayuwar ummi in ance mata wani rana zaizo da za tayi abunda za a kaita koda police station to zata qaryata,to bare wai gidan yari ! Ya ilahy????


Quliya ,bai cire idonsa akan talabijin ba,saida aka nuna inda aka hankada keyar ummi cikin motar en sandan

Wani kakkauran numfashi ya furzo zuwa waje mai d’umin gaske

A take ya d’auki wayar salulansa commissioner of police ya kira ,bugu biyu ya dauka ya soma gaishesa cikeda girmamawa

A gaggauce ya bashi umurnin dakatar da yaransa ga maltreating din ummi da sukeyi
Kuma a wuce da ita headquarters dinsu,yanzu nan zai turo lawyansa na musamman don a daukaka qaran zuwa federal ,inyaso sai idan sun nadi sahihan bayanai a bakin ummy a maida ita gidansu safely


Qarfe biyu da rabi na dare a birnin Abuja, Nigeria

Matasane kusan su biyar suka fito daga cikib wani club da naga daga sama an rubutun sunan da golding blue light kamar haka Recreation club

Wani matashin yaro da bazai Gaza shekaru ashirin da tara ba ,ya fara danewa Bayan wata d’irmemiyar mashin Wanda ake tseran gudu da ita ,A qiyasin kudin Babur d’in kuwa takai miliyon takwas

Sanye yike cikin gajeran wando da singlet mai roba roba da ya dace da hadadden fatar jikinsa mai dauke da lufluf din kwantaccen gashi,kai da gani ba tambaya kasan yaron inba balarabe bane to tabbas ya had’a tsatso da larabawa ,tun a yanayin layalayan gashin kansa da akayi masa askin funck ya saisaye wajen qeya ,ya tarashi cukus ta gaba
Sai gashin gemu da ya Tara cunkus har kusan saman kirjinsa tamkar jikan sheqau
Da gaske kallon farko xaka aza cikakken mutum ne da zai kai shekaru talatin da biyar haka,duba da tsuvurin gemun da ya bari ,sai yana taqadaranci ne ko kuma yina zubo wauta zaka gane yarone danya sharaf

Da fofoti suka fito club din shida abokansa, alamu ya nuna su din gayune kawai amma basa shan komai ,inma da abunda ya kaisu club din to bai wuce kallon rawa ba da rashin ji irin na yaran manya da suka saba da rayuwar qasar waje

Wata wargajejiyar mashin mai fad’i da yawan fitillu ya hau ,sannan ya maqala hulan kwanon dake sagale da hannun mashin din

Wata irin keyy ya sakarwa mashin din kurum ya fara cin taya ,kafin ya fice da gudu giyan qarshe

Ihu sauran samarin suka saki ,suka dafe mashi baya a tasu mashinan
Suna kiran sunan sa tamkar Wanda suke filin tseran gudu ba kan kwaltan filin tarayya abuja suke ba a wannan daren ,sunadab da shiga uturn din da zai dauke hanyar Asokoro yaji tayarsa na gaba ta caki wani abu a take ta fara tangal tangal

Unknown to all of them fataken darene sukayi target dinsu tun fitarsu

Yina ankarewa da hakan ,kurum ya fara daddanna wasu wurare ta gaban mashin din ,a take mashin din ta fara wani irin qara tana jajjan kacocin mashin din tamkar zasu farfashe,saida ya gama daddanna komai sannan yaja burki ya tsaya

En fashin da ada suka daddaga bindigoginsu ,gamida saitin tayoyinsa ganin ya yi saranda ya tsaya yasa suka sauke hancin bindigogin suna kallon qasa ,a gadarance suke qarasowa kamar Wanda suke falonsu

Saida sukazo dab da shi kurum sukaji sautin woyyyyyyy
Saidai sukaji mashin dinsa ta fyalla da gudu ,a take suka fara masa 6arin alburushi saidai Ina ,har tashi sama mashin din takeyi in sun saita sama ya dawo yina gudu a kwalta

Abokansa ihu sukaeyi ” Adnannnnn ka tsaya kudi ne za a basu…”

Basu samu cafkesa ba har ya shige get d’in dake kewaye da gidajen anguwar gabad’aya Wanda manyan sojoji maras imani ke gadinsu,amma saboda kowa yasan Adnani baya harkan qoro yasa in har yike qasar ake barin get din shiga unguwar a bude da zaran zai fita yawon darensa kofa a bude take….

Da hannu daya yike murza hannun mashin din sakamakon hahharbinsa da sukayi a hannu da cinyar qafarsa ,gudu kuwa da tayar baya kadai tsabagen gudun tashin hankali, don haka suna ganin ya shige sukasan ya tsira
Don haka a karce suka juyo suka tasa qeyar abokan zuwa ma6oyansu dasu


Adnan kuwa Bai fara jin ciwoba saida suka rabu da en fashi ,ya kasa qarasawa gida saidai aka qarasa da shi

Gidane tafkeken apartment mai daukeda 6angarorin matan aure hudu ,da qawatacce daga tsakiya wanda ya kasance Na me gidan ne,sai kuma 6angaren mazan gidan su biyu Adnan da Arif dan shekaru sha takwas

Zakayi mamakin duk girman gidan yara hudu tak mai gidan ya Haifa maza biyu mata biyu ,Sai matan aure uku,d’aya bayarbiya daya banufiya d’aya Igbo

Zaman kishi
Tunda aka shigo da Adnan gidan ba mata daya da ta fito a cikin mata ukun da suke cikin gidan

Tun dare yike burgima a cikin jini yina ihu amma ba mahalukin da ya fito ,ciki kuwa harda irfan qaninsa ,kuka adnan ya ringayi yina dakacen rashin mahaifiya ga mahaifinsa ba mazauni ba ,a gaban qofar d’akin quliya ya kwana cikin halin tsananin jinya…


Sala kam gum tayi da bakinta don kuwa ance fadar da yafi qarfinka kamaisheshi wasa
Kowa a garin nan yasan sanda tayi tashen quntatawa hausi ,taso ya auri uwalene su had’u suyi ta ganawa er tahalika azaba ,sai tsamiya ta juyewa mujiya…don haka haquri tayita bata hardai ta mike ta tafi.


Yau qarfe takwas na dare duk su bello sun hallara a tsakar gida a babbar tabarma suna cin tuwon dare
Itakuwa ,uwale sai mutsu mutsu da cinya takeyi tamkar Wanda ake mintsili
Don haka sai zungurar bello takeyi da qafa a dole ya tashi su tafi daki.
Baba tana lura da ita ,don haka sai tura mata sakon harara takeyi ,amma ina aikin banza batama San tanayi ba

Shikuwa bello yina lura da haka ,gabansa ya soma bugu dum dum,kwata kwata kwanansa goma da aure uwale amma harga allah tsoronta yikeji ta gama qare masa ruwan kai

Ana cikin fira hausi tayi miqa tai masu sallama ta wuce daki,mintoci kadan bello ya mike tsidik yayi d’akin hausi ya maida bida ya kulle
A tsorace ta fito tana qwala kiran waye tana gyara daurin kirjin da tayi

“Lafiya bello? “
Tsaki yaja ,kafin yahau sababi

“Yau naji ikon Allah mutum da gidansa don ya shigo d’akin matarsa to meye ba tambaya…amma tunda kin tambaya kwana nazo yi a dakinki”.

” wa??? Ai wallahi saika koma d’akin amarya ,kaifa kacemun in maka qari,kaje can a cigaba da gwangwajewa a gado,inma ka cinye kwanakin da na baka ganin dama nane in qara maka wasu kwanakin”

“To wallahi baki isah ba ,na gama lissafi yau kwananki ne a dawo kwana bibbiyyu ,haba hausina ki tausaya mun kefa tawace ,wallahi matarnan zata kasheni ne ,ni tsorona ma in batada kini da mayu? Saboda dare firrr fa bata barci saidai tayita cinyeni “

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button