JIDDATUL KHAIR 7

Abuturrab na kwance cikin resting cabin din jirgin da yayi piloting tare da Co-pilots dinsa daga lagos xuwa kano, ko minti talatin basu yi da alighting ba, idonsa a lumshe suke duk da ya rufe fuskarsa da hulan uniform dinsu na pilot dake jikinsa, tapping dinsa aka yi a kafa, ya xame hulan a hankali, Co-pilot dinsa ne tsaye kansa, pilot din yyi wani sigh yace “Done with the Secure Cockpit checklist…. Can we??” Abuturrab ya mike xaune yace “Alright…” Pilot din yace “Ain’t you changing??” Abuturrab ya kalli uniform din jikinsa yace “Not at all” Jakunkunansu suka dauka suka sauka jirgin, sai da suka gaisa da incoming crew da suka hadu da sannan suka shiga cikin airport din. Driving Abuturrab ke yi cikin motarsa da yake bari a airport, hotel din da yake sauka yawanci idan yana kano ya nufa, duk da Abbansa na da gida nan kano wanda ke a kulle babu kowa ciki baya sauka gidan don baya son xama shi kadai shi yasa ma idan kwana ya kamasa a Abuja, it’s either su kwana gidansa tare da Ahmad ko Aneesah ta xo tayasa xama, ya so tafiya kaduna yau amma bai samu flight me xuwa kaduna ba or even private jet, yana shiga hotel din ya karbi daki kamar yanda ya saba, wanka yyi ya sauya xuwa kananun kaya, yayi sllh sannan ya bude pepper soup din hanta da ya sa a kawo masa with cup of coffee, ya fara ci a hankali, ajiye spoon din hannunsa yyi tunawa da yayi bai samu Mu’axxam yayi masa magana ba a kan yarinyar nan ta Hayin rigasa, ya dafe kansa don shaff ya mance, tun a jirgi da ya tuna yake Allah Allah suyi alighting ya samesa da maganan, he can even go to d extent of taking all the marriage responsibilities in har Mu’axxam din yace bashi da hali, tsaki ya d’an yi don gobe da sassafe yake son driving xuwa kaduna baxai shiga airport din ba, a hankali ya ci gaba da shan pepper soup dinsa har ya ji ya ishesa sannan ya tashi ya shiga bandaki ya wanke bakinsa ya fito yayi kwanciyarsa. Washegari Saturday karfe goma saura Abuturrab ya shigo compound dinsu… Parking yyi kusa da motarsa da yake amfani da a kaduna, ya sauka sannan ya shiga ciki, part din Aunty ya fara nufa ya sameta parlonta tana breakfast, ganinsa tace “Daga ina haka kamar an jefoka captain?” ya xauna kasan lallausan carpet din parlon yana murmushi yace “Daga kano nake” tace “Ikon Allah welcome son…” Yace “Ina kwana Aunty?” Tace “Lafiya lau ya hanya?” Yace “Alhmdlh” mikewa tayi tace “Let me get u breakfast” Bata jira cewarsa ba ta fita, sae gata ta dawo tare da mai aiki rike da tray din breakfast din, Mai aikin ta gaishesa sannan ta ajiye, ganin kallon da yake ma tray din Aunty tayi dariya tace “Taimaka min kawai tayi ta dauko flask din ba wai ita ta hada maka ba…” Bai ce komai ba ya dau cup dake a kife ya juya yana kallon ciki keenly kamar yana neman abu, Aunty tace “To yanxu da ba Aneesah bace budurwar ka ya xaka yi da wannan kyankyanin captain, yan matan yanxu da son jiki duk ya sa sun xama kazamai” Ba tare da ya kalli Aunty ba yace “Allah ya ga xuciyana shi sa bai hadani da mara tsaftar ba” Dariya kawai Aunty tayi tace “Jiya ma Aneesar ta kirani mun gaisa ashe ta koma Abuja” Yace “Ehh ta koma…” Tace “Idan ka gama sai ka ajiyeni U-rimi don Allah, driver baya nan kuma bana son driving” Yace “Alright” Yana gama breakfast din kuwa ya mike, tuni ta dauko mayafinta da yar jaka, yace “Salem fa?” Tace “Tun yaushe Salem ya koma makaranta” Abuturrab yace “Ohh yea mun yi chatting ya gaya min, but na manta” Sai da suka fita parlon ya tuna bai je gaida Umminsa ba, ya d’an buda ido yace “Aunty bari in shiga in gaida Ummi yanxu in fito” Ta d’an 6ata rai tace “Yanxun nan fa xaka ajiyeni ka juyo Captain, cikin mintuna kadan xaka dawo ai” Bai ce mata komai ba ta fara tafiya ya bi bayanta walking slowly. Abuturrab bai dawo gidan ba sai bayan la’asar tare da ita, tana rike da ledojin atamfofi da ta sa ya siya mata a gidan da suka je, ta nufi part dinta, shi kuma ya shiga bangaren Mahaifiyarsa, kanwarsa Ramlah kadai ce parlon tana shara yace “Ummi fa?” Tace “Ta fita tare da driver yanxu” Ya shafa kansa yace “Ohk…” Juyawa yyi xai fita tace “Shine baka shigo ka gaisheta ba kuma tun safe ka dawo yaya” Ya juya ya mata wani kallo yace “Yaushe na fara wasa da ke?” Shiru tayi bata ce komai ba, yyi kwafa ya fice daga parlon. Bedroom dinsa ya shiga, sai bayan da yyi wanka ya sauya kaya sannan ya fito main parlor rike da makullin motarsa, har xai fita ya nufi kitchen jin movement a ciki, Safiyya ce a kitchen din da Ramlah sai mai aiki da alama dinner suke dafawa, yace “Is there anything to eat here?” Safiyya ta kallesa tace “Aa ba a gama ba” Juyawa yayi ya fita daga kitchen din ya bar parlon gaba daya, sai da yayi sllhn magrib sannan ya bar anguwar… Parking Abuturrab yyi yana kallon cikin karamin layin da babu haske banda na wata, yara ne bakin wani tap suna ta diban ruwa suna wasa da ruwan, tun da yamma ya so xuwa amma sbda comment din Umar a kansa ranan a hospital yasa ya ki shigowa anguwar da yamman, ya sauke glass yana ta kallon yaran, da hannu yyi ma wani yaro cikin yaran alamar ya xo, yaron ya taho da sauri, dari biyar ya dauka cikin motar ya mika ma yaron yace “Kaje can gidan da ake siyar da awara ka kira min yarinyar dake siyar da awaran” Yaron ya ruga da gudu xuwa gidan, yana isa ya kutsa kai ya shiga, Hansai na xaune tsakar gida Bibalo na haska mata fitila tana daure busasshiyar kubewa a leda, Yaron yace “Ina wuni maman Bibalo” Hansai tace “Lafiya lau, me xaka siya?” Yace “Aa wani me mota ne yace in kirawo me awara” Hansai ta kalli Jiddah dake duke bakin kwaroron wanke wanke tana yi, Hansai tace “To ai kuwa xuwa xaki yi ki ji me ke tafe da shi, tunda yasan yanayin garin kilan wani alherin ya xo mana, ko kuma Bibalo ta je, yan sa idon anguwar nan sae su iya juya mana xance yanxu yanxun nan….” Jiddah dai bata dago ba ta ci gaba da abinda take yi, Mikewa Bibalo tayi da sauri ta ajiye fitilan hannunta tace “Bari in je ni” Mayafi ta figa ta fice daga gidan tana ce ma yaron taho ka nuna min inda yake, can bakin titi yaron ya nuna mata, Abuturrab ya dinga kallonta daga cikin motar, tun daga tafiyar ya gane ba jiddah bace har kuwa ta iso bakin titi, tsaye tayi jikin motar, ya sauko yana kallonta, tayi fari da ido tana wasa da mayafin kanta tace “Sannu da xuwa….” Yace “Ina ‘yar uwar taki” ta buda ido sosai tace “Yo ae ta daina fitowa ynxu sbda bikinta sati me xuwa ne, kasan har iyayen iliya sun xo anyi komai yau…” Kallonta ya dinga yi ko kiftawa babu, tace “Idan wani abu ne gani ni ka bani in ji Baabarmu in kai mata” Ya dauke kai daga kallonta yace “Mu je xan ba Baabar taku da kaina” Da sauri ta shiga gaba yana biye da ita, sae wani rangwada take har suka iso kofar gidan, tace “Bari in je in mata magana” daga haka ta shige ciki, Hansai na ganinta tace “Me ya baki?” Bibalo tace “Yace ki je yana kofar gida” Da sauri Hansae ta figi gyale ta yafa ta fita kofar gida, dukawa tayi ta gaishesa ya sauke idonsa shi ma ya gaisheta, ta amsa cike da nutsuwa tace “Sannu da xuwa Alhaji”
07087865788✍🏻