JIDDATUL KHAIRJIDDATUL KHAIR COMPLETE HAUSA NOVEL

JIDDATUL KHAIR 57

Kofar gidan Ramlah Abuturrab yyi parking, tun barin su Hayi sai a lokacin ya juya ya kalleta, a hankali ta kai hannu a sanyaye xata bude motar taji a kulle, duk da haka ta ki kallonsa har sannan hawaye na idonta, yace “To kukan me kike, bayan abinda kika ce kina so nayi maki, gun Baabarki fa kika ce in kai ki kuma na kai ki” Hade rai tayi taki ce masa komai, hakan da tayi ya basa dariya amma bai yi ba ya jinginar da kansa da kujeran da yake xaune yace “Laifi na ne kenan?” Kamar jira take ta fashe masa da

matsanancin kuka har da shessheka, kallonta ya tsaya yi, bude motar yyi ya sauka, ta hade kanta da gwiwa tana rera kuka tana jin xuciyarta na mata xafi, Booth ya tafi ya fito da duk kayan shopping din, ya nufi gate din gidan, dai dai mai gadi xai fito, ya mika masa yace “Ka ajiye su a bakin kofa” komawa yayi booth din motar, a haka duk ya kwashe kayan yana ajiye su cikin compound din mai gadi kuma na kai wa bakin kofar entrance din shiga gidan yana ajiyewa, Bayan kayan sun kare Abuturrab ya koma cikin motar

ya kulle yana kallonta, jin shigowarsa ta dago kanta ta kai hannu xata bude side dinta taji ya kulle motar gaba daya, calmly yace “I’m asking u whose fault it is now? Mine?” Tana goge idonta a hankali tace “Nima ban sani ba ka bude min mota in fita dare yayi” ya dinga kallonta, sai a sannan ta kallesa tace “Ka bude min xan sauka” yace “Yeah!! You did good by wanting to go meet ur stepmom after so many

months, that clearly shows u missed her no matter her maltreatment toward u… u had good intentions but, stepmum dinki bata canxa daga yanda kika santa ba, she is still the stepmom u knew her to be, don haka idan ma tana ranki ne har yanxu ki cireta na har abada, take her off ur mind totally and face reality,

ki mance kin ta6a rayuwa da ita, ki kulle babinta a rayuwarki, face ur new life, bata sonki kuma baxata ta6a sonki ba….” Jiddah ta fashe da kuka cikin sanyin murya tace “Shikenan ni kuma bani da kowa kenan?” Kallonta ya dinga yi, a hankali yace “Baki da kowa??” Kuka kawai take ta ki ce masa komai, ya kamo hannunta yace “Baki da kowa kika ce?” Still bata basa amsa ba amma yanda take kuka kasan she is hurt, bude motar yayi ya sauka, ya xaga ta inda take ya bude side din, saukowa tayi xata wuce gate ya

riko hannunta ya bude back seat yace “Shiga ki goge idonki da kyau before going..” ta kalli motar, sai kuma ta fara goge idon nata, ya d’an hade rai yace “Shiga nace, u can’t go in with those eyes” a hankali tace “Ni na goge ai” Calmly yace “Get inside” Wani hawayen ya taru idonta ta shiga bayan motar, ya dau handkerchief dinsa ya mika mata, amsa tayi tana goge idonta amma da ta tuna abinda Baabarsu tayi mata sai wasu hawayen su xubo mata, shikenan ita ba warce xata nuna tace baabarta ce kenan, a

wajenta ta taso fa ta ga kanta, kowa yana da wanda xai nuna yace yau ga d’an uwansa na jini amma ita banda ita, bata san kowa nata na jini ba, hade kai tayi da gwiwa crying sadly, shi dai kallonta kawai yake, can ya bi layin da kallo, babu kowa a layin don goma ma yayi, mai gadi ma tuni ya koma cikin compound din, shiga cikin motar yayi ya kulle, ta daga kai tana kallonsa tana kuka, yace “Kika ce ke baki da kowa??”

a hankali ta fara matsawa taki ce masa komai, ya kamo hannunta yace “Tell me?” Ta girgixa masa kai kawai, yace “Kin manta kina da Umma, kina da Ummi, kina da Ahmad? Maimoon, Ramlah… Ain’t they all there for u always?” Sunkuyar da kai tayi wasu hawayen na xubo mata bata iya ta basa amsa ba, yyi kasa da murya yace “Answer me” ta gyada masa kai a hankali tace “They are….” yace “Idan ni ban ta6a maki komai ba ae su sun maki kuma suna kan maki ko?” Ganin kamar tunxurata yake dada yi, ya lumshe ido

ya jawota jikinsa, lkci daya ta hadiye kukan da take ta fara turasa a hankali tana komawa baya, ya rungumeta sosai murya can kasa yace “I know i am gonna…” Bai karasa ba kawai ya shiga kissing dinta passionately, tun tana kokarin kwace kanta a rikice har dai ta kasa kwakkwaran motsi ta tsaya cak kamar warce ruwa ya cinye, Tun dai ana kiss har abu ya fara wuce level din kiss, iyakar tsorata ta tsorata a lkcn,

bata kuma san sanda ta fara rokansa cikin rawar murya tana cewa ya rufa mata asiri, sae da ya dawo mata kamar ba shi din da ta sani ba, bakinta na rawa tace “Don Allah Aliyu kayi hakuri ka rufa min asiri, don Allah ka bari, don girman Allah nace maka….” Gaba daya ya gigitata, Ya kai bakinsa kunnenta cikin muryar da bata san sa da shi ba yace “Me ya sa baki saka brassiere ba?” Cikin rawar murya bakinta na rawa tace “Bacci xan yi dama” bai kuma ce mata komai ba, ta kankamesa tana kara basa hakuri da sauran strength dinta, Sae da Abuturrab ya ga he is getting out of the little control he is trying to

maintain sannan ya saketa ba shiri, da ta samu ta figi hijab dinta ko gama sawa bata yi ba ta bude motar ta fice fittt, ko kulle masa motar bata yi ba cikin sakwanni kadan ta shige cikin gate din gida, gaba daya ya hargitsa ta iyakar hargitsawa, Ramlah na xaune parlor ta xabga uban tagumi bayan ta gaji da tsayuwa Jiddah ta shigo parlon, Ramlah ta mike tace “Haba Jiddah ina kika je haka bayan kin san karfe nawa, kin fa san halin da nake ciki kuma kika sa na shiga damuwa sosai haka?” Jiddah ta kasa tsayawa parlon,

bakinta har rawa yake tace “Wllh siyayya yayi yace a kawo maki gasu can a balcony, i.. i want to go ease my self now” Daga haka ta shige daki ta kulle tana sauke numfashi, fadawa tayi kan gado ta shige cikin bargo ta rufe har kanta.. Ramlah dai na ta tsaye parlon deep in her thought, tunda Jiddah ta shigo taji kamshin turaren Abuturrab… komawa tayi ta xauna ta kuma rafka tagumi tunani iri iri a ranta… Abuturrab ya fi minti talatin a mota bayan ya isa gida idonsa a kulle ya jingina da kujeran motar, he is

just hoping Allah yasa Aneesah tayi bacci, wajen karfe sha daya ya sauka motar ya shiga ciki, ga mamakinsa sai ya ganta xaune parlor tana kallon tv, da alamar film din ya tafi da ita shi yasa ma bata fito ba da ta ji sa shiru shiru bai shigo ba, stairs ya nufa da sauri, ta juyo tace “Captain ka ga agogo kuwa kaje ka dade haka?? kuma me kake yi cikin mota tun daxu baka shigo ba?” Ya ki tsayawa yana haurawa stairs

yace “Toh ai baki fito kin ga abinda nake yi ba” Ita dai ta ci gaba da kallonta tana washe baki don a xo dai dai scene din da take so a film din, yana isa bangarensa bandaki ya shiga yayi wanka ya fito ya saka pajamas dinsa ya kashe wutan dakin sannan ya kwanta yayi rub da ciki ya runtse ido, bayan kusan thirty minutes Aneesah ta shigo dakin don an gama film din, yana jin ta amma yayi kamar bacci yake, kwanciya

tayi gefensa tana shafa fuskarsa tana kiransa a hankali cike da shagwaba, he just don’t have Choice in dai yana son bacci a ranan, haka nan ya biyeta kamar jira yake dama, har hakan ya 6ata mamaki… Sha biyu saura Jiddah ta cire bargon da ta rufe jikinta da shi ta mike xaune a hankali, har lokacin kirjinta bai daina bugawa ba, da ta tuna abinda ya faru sae gabanta ya fadi sosai, bata ta6a jin tsoron Abuturrab irin na

daxu ba, gaba daya ta tsorata da shi da lamarinsa, da kyar ta cire Hijab dinta ta sauka daga kan gadon ta wuce bandakin, ta shiga bandaki da kusan minti sha biyar Ramlah ta bude kofar dakin a hankali, shigowa dakin tayi ta dau hijab din Jiddah ta kai hancinta, imagine ta fara yi to ko dai fesa mata turaren yayi ne?? Kallon kofar bandakin tayi jin kamar wanka take yi, can dai ta ajiye Hijab din a hankali ta nufi kofa ta fita

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button