
Ta bayyana haka ne a wasu sakonni da ta wallafa a shafinta na Tuwita ranar Asabar BbcHausa ta rawaito.
Stop giving birth to children you know you’re not capable of taking care of ????????♀️.
— Nafisat Abdullahi (@NafisatOfficial) April 16, 2022
“Ku daina haihuwar ‘ya’yan da kuka san ba ku da halin kula da su,” in ji Nafisa.
Ta kara da cewa Allah zai tuhumi mutanen da suke haifar ‘ya’ya ba tare da sauke nauyin da ya dora musu ba.
A cewarta: “Kun ga dukkan mutanen da ke haifar ‘ya’yan da ba su ji ba ba su gani ba, domin kawai su aika da su almajiranci, kuma su ci gaba da haifar karin ‘ya’ya, Allah sai ya saka wa yaran nan!!!”
Ta bayyana matukar bacin ranta kan yadda wasu iyaye suke tura ‘ya’yansu ‘yan shekara biyu zuwa uku almajirci.
Tauraruwar ba ta ambaci sunayen wadanda take yi wa wannan gargadi ba, sai dai dama ba sabon abu ba ne yadda a kasar Hausa ake tura kananan yara almajirci.
Wannan lamari ya dade yana bata wa mutane da dama rai, musamman ganin cewa wasu na zargi ana amfani da irin wadannan yara wajen aikata laifuka.
Martani
Sai dai kalaman tauraruwar sun jawo martani daban-daban inda wasu suke yaba mata yayin da wasu suke sukar ta.
Da yake tsokaci, M.M Dambatta, ya jinjina wa tauraruwar sannan ya ce “har yanzu na kasa fahimtar yadda uba zai aika dansa dan shekara biyar domin ya kula da kansa da sunan almajirci. Ya kamata a tsayar da wannan lamari.”
Wlh kam, that’s why most of those children are on the streets begging. I’m still having it difficult to comprehend how a father will send his 5 year old son to Cather for himself all in the name of Almajiranci???? this has to stop.
— M.M Dambatta (@M_Dambatta) April 16, 2022
Shi ma IAOgundele ya ce haihuwa barkatai ba tare da lura da ‘ya’ya ba ita ce sanadin matsalolin rashin tsaro da ke addabar Najeriya yana mai cewa “albarkatun da ake da su sun gaza ciyar da yawan mutanen da ake haifa.”
That’s major problem confronting the Nation….look no further as to why insecurity, hunger continue to linger.. Available resources fell short of increase in population
— OAI (@iaogundele) April 17, 2022
Sai dai Murtala Ubale ya tambayi tauraruwar cewa “wacce gudunmawa za ki bayar dan a daƙile cigaban hakan?”
@Nafisatofficial wacce gudun mawa Zaki bayar dan a daƙile cigaban hakan
— Murtala ubale (@Murtalaubale5) April 16, 2022
Shi kuwa Autan Gwaggo cewa ya yi “kina kwance a kan gadonki, kina wani cewa Allah sai ya saka ma yaran nan.”
Kina kwance a kan gadon ki , Kina wani cewa Allah Sai ya sakama Yaran nan . Ae daman ko Baki fada ba, Allah baya goyan bayan Mai zalunci .
— Autan_Gwaggo (@autan_gwaggo) April 17, 2022
[ad_2]