KUFAN WUTA COMPLETE HAUSA NOVEL

KUFAN WUTA COMPLETE HAUSA NOVEL

TEAM ZAFAFABIYAR13

YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:

THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME

DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN???????? 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU

KHUMRAHS
KULACCAMS
TURARUKAN WUTA
NA TSUGUNNO
NA KAYA
NA GIDAH
NA GASHI

NA WANKA
NA WANKI
NA MOPPING

AIR FRESHENER
CURTAIN AND CHAIRS SPRAY
WARDROBE BALLS
SCENTED PEBBLES

ARABIAN OIL PERFUMES
HAIR SPRAY AND CREAM
DILKE AND HALWA SET

KABBASA
BURNERS
KASKO
TONGS
COAL IGNITERS

SKIN CARE PRODUCTs
OUR TURARE SAMPLE SETS
BRIDAL SET (SAITIN AMARE)
KUJERAR TSUGUNNO

SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA

MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE

SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED

instagram:yerwaincense_and_more*

WhatsApp: 08095215215


   Matashin saurayi ne tsaye a bayanta,fari qal,wanda har wani yellow yake saboda haske,ma'abocin kyau na gaske,wanda fuskarsa ta cika da baqin gemu da kuma sumar kai,ba siriri bane kamar yadda yake ba mai qiba ba,jajayen lips dinsa dauke suke da murmushin da ya bayyana fararen haqoransa,yana sanye da wata muguwar shadda daketa faman zuba qyalli da maiqo,ruwan hanta wanda ta dace da fatarsa da kuma fitar da kyansa muraran,hannayensa na goye qirjinsa,wanda hakan ya bayyana muqullin motar dake soke cikin daya daga cikin 'yan yatsunsa.

      Tsoro ya sanya ta sake ja da baya ganin yadda yake ci gaba da kallonta,murmushi shimfide saman fuskarsa,cikin wata murya mai zaqi ya sake cewa

“Gashi nadin yayi miki kyau sosai da sosai,saidai kuma kuma baki iya daurawa ba,halan mama ce ta daura miki kafin ki fito?” Rasa amsar bashi tayi sai idanu da take rarrabawa

“Wannan auta ce da alama” ya sake fada yana komawa da baya a hankali ya zauna saman kujerar concrete dake wajen,har yanzu bai janye idanuwansa daga kanta ba,hakanan murmushin da yakeyi baibar kan fuskarsa ba

“Iman…..iman” sautin muryar munira ya fara shigowa wajen,da alama ita take nema

“Uhunnn…..da alama ke suke nema,abokan tafiyarki ne ko?” Ba tare daya jira amsarta ba ya dora
“ki daura abarki,lemme close my eyes” ya fada yana lumshe qananun kyawawan idanunsa.

     Ta tabbatarwa kanta ba zata iya fita a haka ba,saboda al'ummar dake harabar wajen sun ninka shi a yawa,saita leqa a hankali,ta tabbatar da gaske idanunta a rufen suke,don haka cikin sauri ta fara daurawa.

“Are you finished……an min izini na bude idanuna?” Ya fada a tausashe

“Eh” ta amsa cikin sanyi,ya bude idanun nasa tarwai saman fuskarta

“Wow…..wow I didn’t realize yadda ta miki kyau kamar yanzu da nake kusa dake, please ke wanne yare ce?……i think kanuri ne suke amfani da ita ko?” Yadda yayi maganar har saman fuskarsa ya nuna da gaske so yake ya sani,don haka ta gyada kai

“Eh sune”
“It means ke din kanuri ne?” Kafin tace komai munira ta iskota

“Canza waje kikayi kenan inata bul……” Maganarta fa maqale a maqoshi sanda idanunta suka sauka a kansa,saita rusuna da sauri cikin girmamawa

“Yallabai barka da yamma” cikin wata dakiya wadda bada ita yanzu yanzu suke magana da iman ba yace

“Barka” kafin wani a cikinsu ya sake magana wata muryar ta sake cika wajen da kiran sunan

“Bassam…….bassam”
“Hey guys…..wannan kiran fa?” Ya fada yana daga sautun muryarsa dake da zaqi,wanda har sai da iman tadan sake kallonshi.

    Mutum biyune suka qaraso wajen,dukkansu samari ne da kana musu kallo daya zakasan sunaji da jini da ajiki da kuma tashen samartaka,kowannensu kalar shigar dake jikinsa zata fallasa maka wadatar da yake ciki

      "Shege....baka da mutunci wallahi,na dauka da gasken kayi tafiyarka" daya daga cikinsu ya fada yana cika yana batsewa,tare da jifansa da harara,baki ya tabe kamar yadda mata kanyi

“Gab nake da tafiyan ai,rabo yasa na ratso ta nan” yayi maganar kansa tsaye yana nuna iman da yatsan hannunsa,dukka suka waiwaya suna kallonta,abinda ya sanyata gaba daya taji ta tsargu ta kuma takura,

“Rabon samun matar aure” kamar saukar tsawa iman taji maganar,wanne irin magana ce wannan yakeyi,bayan har yanzu basu zarce mintuna ashirin da fara ganin juna cikin rayuwarsu ba,batasanshi ba bai santa ba,har yanzu ko kalma daya tak bata furta gareshi ba,saita rutsashi da kallon mamaki,ganin haka shima ya tsareta da nasa kallon tare da murmushi mai qawatarwa

“Yes,da gaske nake” ya tabbatar mata yana lumshe idanunsa tare da budesu a lokaci guda

“Muni……qawarki ce?” Daya daga cikin wandanda suka shigo wajen ya tambaya,cikin murmushi tare da madaukakin farincikin da muniran keta qoqarin dannewa tace

“Eh yaya ahlan,aminiyata ce……”
“Zaku iya bamu waje mu tattauna?” Matashin da aka kira da bassam ya fada still bai iya dauke dubansa daga kan iman ba,sai ahalan din yaja da baya

“Baka da matsala,but kada ka dade da yawa”

“Alright” ya amsa a taqaice,dukkaninsu sai suka juya suka fara barin wajen,yayin da iman ta bisu da kallo cikin taraddadi,tamkar ta bisu amma ta gaza daga qafarta daga wajen.

“Have a seat please” ta tsinci muryarsa yana tsaye daga bayanta kamar wani bodyguard da uban gidansa,ya tashi daga mazauninsa ya bata daman zama,bata da abun cewa illa qarasawa da tayi,a hankali ta zauna kamar yadda ya buqata,saidai bata wani saki jikinta ba kamar wadda ke dosane saman garwashin wuta.

       Qarasowa yayi a hankali,ya shimfida handkerchief a gabanta qasa saman grass carpet din yayi xaman dirshan,tazarar dake tsakaninsu ba me nisa bace,saidai bai kusantota da yawa ba,ya aza mata dukka idanunsa sannan ya fara magana da ita.

  "sunana bassam balarabe madaki....." Kai tadan daga kadan ta kalleshi,kamar tasan sunan,kamar tana dan jinsa cikin kafafen yada labarai

“Nine da na uku a wajen mahaifina,da na farko a wajen mummy na,shekarata ashirin da da takwas,’yan kasuwane mu duk da muna karatun boko me zurfi,hasalima nine jagoran dukka kamfanonin madaki general enterprises,ban taba aure ba,saidai for now zan sanya damba,domin kuwa naga matar aure,sai kuma inda qarfina ya qare,ki daga kanki ki kalleni da kyau kiga nayi miki ko banyi miki ba,saboda ni din mutum ne kaifi daya,banason boye boye kuma ban iyasa ba…..”shuru ne ya ratsa tsakani,bata ko motsa ba bare ta daga kai ta kalleshi,sai wani bugu da zuciyarta keta famanyi,saboda tsayin rayuwarta bata taba tsaiwa da wani da sunan saurayi ko soyayya ba saishi.

   Duk yadda yayi kan ta dubeshi ko tace wani abu taqi,har wayarta ta dauki tsuwwa,sunan inna ya bayyana,abinda ya sanyata miqewa zumbur kenan

“Innata ke kira,tun daxu muka fito,kuma tacemin kada nakai dare a waje” tayi masa bayanin tana qoqarin bin bayan kiran inna daya katse.

    Wayar ya zubawa idanu har zuwa sanda kiran ya shiga,a dan rude takewa innar bayanin gata nan a hanya,bata saurareta ba sai fada da taketa tsula mata kamar xata rufeta da duka ta cikin wayar,dai dai sannan munira ta sake shigowa.

    "Kije xan rakota zamu fito" amsar daya hawa munira kenan,saidai kafin ya miqe iman har tabi bayan munira,cikin azama ya cimmata suka jero.

        Sai gaba daya ta duburce saboda yadda idanuwa suka dinga yawo a kansu,suka dinga jan hankalin mutane,ta lura sam ko a jikin bassam,sai hira da yake janta dashi cikin lanqwashashiyar murya,idanuwansa a kanta duk bayan sakan uku zuwa biyar,har suka qaraso parking lot na gidan.

      Milk color din wata jibgegiyar mota ya bude mata yana fadin

“Bismillah” baya taja,idanunta na nuna alamu na tsoro

“Xan qarasa titi nahau napep” waiwayawa yayi ya kallo munira

“Ke baki gaya mata anguwarnan ba’a samun abun hawa na haya ba?”

“Bata sani ba” munira ta amsa masa cikin wani salo na yauqi irin na ‘yammatan da suke ji da kansu

“Ok,muje na fitar dake titi a motar,amma bisa sharadi daya……idan ba’a samu abun hawa ba,zan kaiki unguwarku” a jikinta takeji zaa samu,don haka tace masa ta yarda,saiya gyada kai yana murmushi

“Allah kasa nayi winning”, ya fadi harda daga hannayensa sama,tadan dauke kai kadan yana son bata dariya ganin yadda ya haqiqance bilhaqqi.

     Wani sassanyan qamshi ke tashi cikin motar,ko ba'a gaya maka ba kasan turaren da yake amfani dashine ya hadu da qamshin freshener na mota da kuma sanyin ac ya bada wani yanayi me mugun dadi,tun daga waje dama zakasan motar sabuwa ce,cikin motar kuma shi xai qara tabbatar maka da hakan.

    Addu'ar bassam itace taci kuwa,don sun jima suna tsumayin samun abun hawa saidai babu shi,dole hakanan tana ji tana gani suka dauki hanya zuwa unguwarsu,zuciyarta ta dinga bugun uku uku,ranta cike fal da tsoro da kuma fargabar kada ta hadu da wani dan gida.

      Tunda suka soma tafiya yake janta da hira,cike da nuna tsantsar kulawa da wani salo dake nuna zallar shauqi,baiji kunya ko nauyin ganin idanuwan munira ba ya dinga fayyace mata zuciyarsa,kalamansa suka dinga yi mata nauyi aka,har kunya tasa ko cikakken motsi ta kasa,karo na farko da wani ya zauna yana shirya wasu manyan kalamai wai duk don saboda ita,ta yadda lallai kamar yadda ya gaya maya ne,shi din bashi da boye boye ko kuma rufa rufa,a haka har suka iso dab da layinsu,tasa ya ajjiyeta daga baya baya.

     Har tasa hannu zata buda murfin motar da hanzarinta,ya danna mata Lock

“Ya zaki tafi ki barni haka?,babu gamsashshiyar amsa,sannan kuma babu madafa,so koke gobe ayi jana’izata?”

“Me kake buqata?”
“Phone number dinki” ya amsa mata kai tsaye,so take ya barta ta wuce don haka ta fara karanta masa yana serving,duk da haka bai barta ba har sai daya kira yaji ta shiga sannan yace

“Thank God” ya furta yana fitowa shima da sauri dava motar,ya zagayo inda take ya bude mata cikin girmamawa.

       Waiwayowa tayi ganin ya fara take mata baya yana biye da ita kamar wani bodyguard,ta buda baki zatayi magana,ya ritsata da kallon nan nasa

“Tattaki zan miki angel….”ya amsa mata tambayarta tun batakai ga yinta ba

“A’ah,don Allah ka bari,wallahi na gode,zan qarasa,munira zata rakani” hannayensa ya sanya ya rufe fuskarsa kadan yana furzar da iska

“Banso kika dakatar dani ba….but,ba yadda zanyi,abinda zuciyarki keso ya zama kamar umarni ne a gareni…..munira” ya kira sunan muniran da tayi mutuwar tsaye a gefe

“Ki kulamin da ita,har ku isa gida banaso ku quda ya tabata…..deal” tunda ya fadi hakan tasan me yake nufi,ko banza yau za’ayi mata yayyafin kudi,tasan a zaune take wannan,haka suka jera da iman din zuwa cikin layinsu,bassam ya bita da idanu,yana jin kamar ya hadiyeta,wani wawan kamu soyayyarta tayi ma zuciyarsa,irin kamun da ba’a taba yi mata irinsa ba,bayajin zai iya haqura da yarinyar ba tare da ya mallaketa ba.

ZAFAFA BIYAR

BIYAR : DUBU DAYA (1k)
HUDU: 700
UKU: 500
BIYU: 400
DAYA: 300

AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE  MU TA:

ZAKU BIYA KUDINKU ANAN????????

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya????????

09032345899

KATIN MTN????????

09166221261

YAN NIJAR ????

+227 95 16 61 77

Ga ‘yan nijer zasu tura katin moov ko Airtel zuwa wannan number

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18Next page

Leave a Reply

Back to top button