KUFAN WUTA COMPLETE HAUSA NOVEL

KUFAN WUTA COMPLETE HAUSA NOVEL


ZAFAFA BIYAR

VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)

VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.

TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.

TEAM ZAFAFABIYAR[04/06, 4:54 pm] +234 903 165 5683: 14
YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:

THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME

DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN???????? 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU

KHUMRAHS
KULACCAMS
TURARUKAN WUTA
NA TSUGUNNO
NA KAYA
NA GIDAH
NA GASHI

NA WANKA
NA WANKI
NA MOPPING

AIR FRESHENER
CURTAIN AND CHAIRS SPRAY
WARDROBE BALLS
SCENTED PEBBLES

ARABIAN OIL PERFUMES
HAIR SPRAY AND CREAM
DILKE AND HALWA SET

KABBASA
BURNERS
KASKO
TONGS
COAL IGNITERS

SKIN CARE PRODUCTs
OUR TURARE SAMPLE SETS
BRIDAL SET (SAITIN AMARE)
KUJERAR TSUGUNNO

SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA

MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE

SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED

instagram:yerwaincense_and_more*

WhatsApp: 08095215215


   Cikin wani irin zumudi da zakwadi munira tayi hanzarin kamo iman suka jera

“La’ilaha illallahu,wallahi kin cika ‘yar baiwa iman…..dama ni jikina yana bani ke matar manya ce,da alama ke zaki zama tararuwar gidanku…..iman,kinsan kuwa waye bassam a karan kanshi kafin akai ga mahaifinsa?,kinsan yammatan dake layi da kai kawon kama qafa dashi?,bakya amfani da social medias ne,amma da basai na gaya miki waye bassam ba” hankalinta duka yayi gida,saidai tana saurara gami da fahimtar kowacce magana ta muniran ke magana akai

“To sai akayi yaya?”
“Don girman Allah kada kiyi mana baqulu da baqinciki,don wallahi bake kadai ba,hatta ni na warke,na kuma sake zama babbar yarinya,don Allah kada ki qauron baki,kada kice baki sonshi,saboda bassam irin mazan da kowacce mace ke buri da qauna ce” munira ta fada tana marairaicewa

“Nifa tsaya kiji,na yiwa ya al’ameen alqawarin bazanyi soyayya da kowa ba” idanu munira ta fitar kafin ta maidasu

“Kamar yaya?”

“Eh,yace idan lokaci yayi zai fitarmin da miji” dariya ta saki sosai cikin nishadi

“Dalla can,ashe ke baki da wayo,ya fadi hakane fa a sannan saboda qananun shekarunki,kada farinjinin da kike dashi maza suyi amfani da kya da kike dashi su yaudareki,amm kawo yanzu ai kinkai munxalin fara zance ma,tunda dukkanmu zance muke,ga wasu ma an fara aurarwa,koshi yaga bassam zai miki sha’awarsa,zai kuma so ya zama surukin gidanku” kai iman ta kada

“Duk abinda ya al’ameen ya fada yana nufin abinda ya fada din”

“Ikon Allah,nifa ban ganewa wannan dagiyar ta ya al’ameen ba,banda yayanki ne ai da sai nace ko kansa yakewa tanadi ne?” Waiwayawa kawai tayi ta kalli muniran,saita dauke taci gaba da tafiya batace komai ba,kunnuwanta na sauraren magiyar muniran kan kada ta tankwabar da soyayyar bassam kamar yadda ta yiwa dan uwata sadam

“Ke kamar bakisan rayuwa ba iman,wasu har rubutu da maganin farinjinin samun mai kudi ake musu,ke kuma kin samu daga Allah amma zaki wofantar da damarki,ki godewa Allah wallahi,koda bakison sadam ko qawance kukayi wallahi saikin tserewa sa’a a cikin dangi da qawayenki,saikin wuce kallon raini,ke ba zakisan haka ba,amma ni naga abubuwa da dama kuma ina kan gani cikin dangin umma na,saboda mahaifina ba kowa bane,mahaifiyata tana auren mutumin da ba wani ba” wannan hirar ita ta kaisu ga qofar gidansu iman,wanda babu mutane sosai,sai dai daikun daliban malam da suka dawo daga gurare daban daban akayo gida kuma,wasu na cin abincinsu na dare wasu na hira,saboda yau din ba ranar karatu bace,uwa ba kuma alamu na nuna malam din baya kusa ma.

  Kallon da inna ta watsa mata sanda ta shiga shi ya sanyata ta shiga taitayinta,munira ta qaraso ta rusuna gaban inna

“Don Allah inna kiyi haquri,wallahi gidan qanwar umma ta rakani,ummance kuma ta tsaidani zamu amshi saqo mu taho mata dashi,don Allah inna kiyi haquri,laifina ne”

“Allah ya tsare gaba,amma ku kiyaye,kada ku bari ku dinga yin dare a waje,’ya’ya mata ne ku”

“In sha Allahu inna,ayi haquri,na gode” munira ta fada tana miqewa,suka qarasa dakin iman din

“Don Allah qawa na roqeki,nasan zai kiraki,koda baki sonshi ki tsaya ki saureshi a rabu lafiya” munira tace da iman cikin lallabawa sannan ya fito bayan sunyi sallama.

    Kayan jikinta ta fara cirewa ta sanya na zaman gida,sannan ta daura alwalar sallar isha'i,ta dawo dakinta ta tayar,data idar tayi zaune saman abun sallar,tana jin gajiya na nuqurqusarta,ta daga kai ta dubi agogo,bataji duriyar alameen ba,da alama bai dawo bane,da tuni ya nemeta.

      Idanunta suka sauka kan ledar da munira ta ajjiye mata me kayan takeaway na bikin data hadota dasu,ta janyo ta bude ta gani,su souvenir's ne kala kala harda na banza da rashin sanin ciwon kudi,sai kuma kayan ciye ciye.

     Jakarta ta zaro cikin kayan ta bude don ciro wayarta,hannunta ya sauka kan wasu abubuwa,ta zazzagesu da hanzarinta. Sabbin kudade ne fil a miqe,yan 200 bandir guda,idanu ta fiddo waje cikin tsoro da mamakin yadda akai kudin suka samu,sai kuma tayi tunanin na munira ne,tunda jakar na hannunta,don haka ta dauki wayarta ta cire lock din ta fara qaqarin nemanta,saita ga alamun tex,ta buda don duba daga ina yake.

      Ta zaci daga kamfanin mtn ne,don su kadai ke tura mata saqo,saidai a yau din akasin hakanne,don kuwa wata tsararriyar number ce dauke da wani zazzafan saqo,wanda ke cike da wasu shiryayyu kuma tsararrun kalamai dake nuna zallar shauqin soyayya da ma'abocin saqon ya tsinci kansa a ciki.

     Sau uku tana karanta saqon tana komawa farko,sai daga qarshe idanunta suka kai kan sunan bassam,ta maimaita sunan sannan ta goge saqon da sauri,zuciyarta na bugawa,ta fita ta kira munira

“Kinyi mantuwar kudinki cikin jakata fa”

“Ba nawa bane,naki ne,bassam yace a baki” kicin kicin tayi da ranta

“Amma me yasa zayimin haka?,kinsan dai bana karbar kudin kowa ko?ko sadam da yake dan uwanki ban karbi kudinsa ba kin sani,bare wannan da bansan kowa nasa ba”

“iman…..wai me yasa kike haka ne?,kinsan dai babu kyau maida hannun kyauta baya ko?,ya zaa dinga miki alkhairi kina qin karba?”

“Na karba idan an gani a gida nace me?”

“Dama ni bance ki nuna ba,idan kinsan za’ayimiki fada ki ajjiye abinki ki dinga zara kina amfani dashi”

“Banaso munira,kizo kawai ki karba abinda ki maida masa” dariya taji ta qyalqyale dashi

“Toni ina zan ganshi yanzu?,bayan kin fita daga motar naji yana waya,a taqaice dai a abuja zai kwana ba’a kano ba,sannan na riga da nayi masa alqawarin zame masa jagora wajen samunki,kinga idan kina tsoro ma kina iya bashi dama yazo gida yaga malam……hakan zaisa kuyi tarayyarku babu tsoro ko shakku,kiyi amfani da kudinki kawai malama,sai da safe” munira ta katse wayarta abunta ta barta da waya a hannu.

     Karar shigowar kira ya sanyata zabura,saura kadan wayar ta subuce a hannunta,tayi qoqarin saka wayar a silent sannan ta nutsu ta duba me kiran,idan har idanunta dai dai suke nuna mata number dazu ce data tura mata saqo,saita samu kanta da latsa ok,ta kara wayar a kunneta.

     Zazzaqar muryarsa ce ta fara dukan kunnenta,a hankali ta amsa masa sallamarsa

“Kin tafi kin barni da kewarki,inajin kamar ba awannin da suka shude bane muka rabu,kamar wasu shekaru ne suka raba tsakaninmu…..” Yayi maganar cikin salon iya jan hankalin diya mace,da kuma zallar qwarewa wajen sace zuciyar diya mace

“Don Alla kice wani abu kafin zuciyata ta fashe imani……zuciyata ta kamu da mahaukacin sonki,wanda har ta fara hasashen yadda rayuwa zata kasance mata babu ke”. Wata ajiyar zuciya cw ta subuce mata saboda nauyi da kalamansa suka fara yiwa zuciyarta

“Me zance maka to?” Ta samu kanta da furtawa

“Koda bakice komai ba ki saki jiki ki bani dama,don koda baki fada ba na samu labarin nine mutum na farko da zan fara bude zuciyarki,so inason ayimin alfarma a kuma bani dama,nayi dashe me kyau,wanda zai bada kyakkyawar yabanya……don Allah beauty” ya qarashe maganar cikin marairaicewa.

     Murmushi mara sauti ya subucewa fuskarta,ashe itama watace,ashe takai a gaya mata kalamai har haka anema soyayyarta,itama ashe takai,kalaman baqine ga kunnenta,saboda haka nan da nan ta sake ta bashi kunnuwanta,yayi amfani da wannan damar ya dinga mata hira me matuqar dadi,yana kodata gami da yabata takowanne fanni,tare da kuranta matsayin data samu cikin 'yan daqiqu,da kuma yadda zuciyarsa ta mato mata.

       Kiran sunanta da taji inna nayi daga tsakar gida ya dawo da ita daga nisan kiwon da tayi,cikin hanzari ta katse wayar,ta kuma kasheta gaba daya ta tura qasan filo,cikin yanayi rashin gaskiya ta kwasa ta yiwo waje da sauri ta tsaya kan inna

“Gani inna” kallo ta bita dashi a nutse kafin daga bisani tace

“Me kika shiga daki tun dazu kika zauna kinayi ko abincinki baki dauka ba?”

“Sallah nake inna?”
“Qara’insu kikeyi?” Da sauri ta girgiza kai

“A’ah inna,isha’i ce kawai,gajiya tasa dana gama nadan kwanta,kinsan munsha zaman lalle”

“Yayanki ya shigo,bakiji shigowarsa ba?” Tayi mamaki,don har ga Allah bataji shigowar tasa ba da gaske,karo na farko da irin hakan ta faru,don babu wani abu dake shagaltar da ita ta kasa jin shigowar al’ameen din

“Banji ba inna,gyangyadi ya saceni” ta fada tana istigfarin qaryar data sharara

“Dauki abincinsu kikai musu,daga nan ki cewa sadiqu yazo ina kiransa”

“To inna” ta fada tana daukar babban farantin kayan abincinsu tayi dakin.

    Kamar ko yaushe sai data tsaya tayi sallama aka bata izini sannan ta cusa kai,dashi idanunta suka fara karo,hannunsa riqe da wayarsa yana kallon wasu styles na dogayen riguna daya dora a account dinsa na Instagram,wanda bai jima da budeshi ba bisa shawarar sadiqu.

     Sexy eyes dinsa da suka sake lumshewa saboda gajiya da yunwa ya buda a hankali ya sauke a kanta,ta qaraso a nutse ta ajjiye farantin

“Sannu da zuwa yaya”

“Yauwa queen…..ya gida?”
“Lafiya lau yaya,ya aiki”

“Alhmdlh,zubamin abincin” ya fada yana zamowa daga saman kujerar zuwa qasa,hankalinsa akan lallenta baqi da ja wanda yayi masifar zanuwa saman farar fatarta me haske sosai

“qunshin yayi kyau sosai queen” ya samu kansa da fadi sanda take qoqarin zuba masa abincin,saita daga kai suka hada idanu,cikin jin nauyinsa tace

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18Next page

Leave a Reply

Back to top button