
⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐
Abinka da farar fata tuni fuskarta ta kumbura tayi jawur ga wani azabebben zazzabi daya rufeta tun kafinnsu isa gida jikinta sai bari yake
tab aiko Ummi kam ta hatsala fada take tamkar zata aro baki har zuwa bayan maggariba fada take sosai Nenne sai bata haquri take amma ina fada take har su Abba da Ahmad suka shigo gida yayinda bba bello da Yusuf ke binsu a baya .
Yan uwana musulmai ina barar addu,arku ga dan uwana ya Abubakar Wanda Allah ya mai rasuwa ya Allah ya jiqanshi da rahama ????????????????????
By garkuwan Fulani 090,,,,,,
[4/9, 1:48 PM] +234 909 785 3276: ????????????????????????????????
MI,WASMITI…..page 9⃣ Na Aysha Ali Garkuwa
????????????????????????????????
????????Bayan ya bude taron da addu,a ya dan yi gyaran murya ya jinjina kanshi jikin kushin ya dan kalli illahirin Family enshi din haqiqa shi da kanshi yanajin nauyin furicin da zaiyi zuciyarshi Na samun rauni idan ya kalli idanu jikokin nashi yana samun fargaba sosai yanajin tsoron kar yau ta kasance ranar nadama ko ranar baqin ciki ko ranar daukewar farin cikin wani sashi daga cikin sashikan zuriyar tasa jikin jinjina kai ya dan dago kanshi Ya dan zuba musu ido gaba daya a hankali ya danyi gyaran murya ya bude baki cikin sanyin lafazi da taushin baki yace
Bello da kai da sauran qannan ka da matanku da qanwarku da maigidanta da dan uwana da iyayenku mata Yau gashi mu dukkanmu Allah ya kawomu wannan rana da muke fatan isar da wani alqawari da muka dauka idan Allah ya nufa yai shiru ya dan zuba musu ido
sukuma yara daga kan Adam har xuwa kan Aysha ido suka zuba musu cikin yanayi tabbayar wanne alqawarine wannan Ahmad tun wayewar garin bugun zuciyarsa ta zarce tunaninshi sai yanxu yaji abin Na sauqa shiko Adam kallon kakan nasu yayi cikin dan zaquwa yace gsky mu bama son Jan rai kana mgn kana jinkirtawa da sauri baba Umar ya daga mai hannu alamar ba batun wasa ganin haka yasa gaba daya sukayi shiru sai yusuf shi dama baiyi mgn ba asalima kanshi a sunkuye yake Aysha da ke dan manne jikin innayi ta maida kanta tai lamo yayinda Amira ke gefen Adam maryam kuma Na jikin Nenne duk suka maida hankalinsu kan Bappa yayan a hankali yaci gaba da cewa Ahmad
Bai Amsaba sai ido daya zuba mai bugun zuciyarsa Na tsananta ????Ahmad ya kuma kiransa da gyar ya iya amsawa Na,am jin yadda sautin muryar Ahmad din ta fito yasa Yusuf da Aysha dagowa a tare suna klonshi sai yanxu su duka sukaji wani baqon yanayi ya darsu kan zuqatansu sautin muryar kakan Nasu ya katse musu Al,amarin yana mai cewa Ahmad A kullum duk zuriyarmu tana alfahari da kai haqiqa Na tabbata kai mutum ne mai cikir haiba da nazartan hilin da ake ciki Ahmad ina alfahari da kai a zuriya ta Na tabbata kai dayane mai fahimtar kalemen mutum duk kaushinsu da dacinsu
Tun kana yaro baka taba kaucewa
Umurnin iyayenka ba ko yaushe kai mai biyeyyane a garemu
Baki daya shiru ya dan kumayi yayinda duk parlon sukayi sit Yanayin Ahmad kuma yafi kama da wanda tsoro ya cika zuciyarsa sukuma iyayensu gaba daya sada kansu qasa sukayi
Cikin qarfin hali yaci gaba da cewa Ahmad a yau Alfarmanka nake nema kuma da yafiyarka dani da iyayenku baki daya Ahmad muna masu tausar zuciyarka muna kuma buqatar haquri daga gareka
Cikin rashin fahimta yace bappa yaya ni kuma muryarsa har rawa take yaci gaba da cewa ya isa tunda tun forko kace iyayena toh mgna ta kare ba wani neman alfarma tsakaninmu a hankili ya daga kanshi ya kalli qanin mahaifinshi yace Abba ni dai ni din Abba me kuke buqata a gareni da har kuke ban haquri ni Ahmad danku meye rage da baku minba a duniyarnan ???? ya maida dubanshi gun mahaifinshi da mahaifi yarshi yace baba da Nenne kun gama min komai Nenne am Na Dade ina Neman abin da kike buqata in miki a duniyar nan da kema zakiji bakiyi asarar yaranki da suka rasuba cikin ‘yaya 12 da kika aifa sai mu 3 Allah ya bar miki Nenne ni Ahmad ki gayamin meye buqatarku yaku iyayena ya qarishe mgnar
Yana mai zubda qwallah???? ya dan kalli kakanshi yace bappa Yaya gayamin meye buqatarku ko zanji sauqin abinda ka dauramin haqiqa zuciyata ta soku ????in dai bazaku sani Abu kai tsayeba sai kunce kuna Neman alfarma
Ahankili Abba ya daura hannushi kan tsakiyar kanshi cikin wata iriyar murya yace Ahmad Allah yamaka albarka ubangiji ya jibanci Al,amuranka
Cikin muryar kuka nenne tace Amin yusuf kam tuni zuciyarsa ta fara tafasa ganin hawayen biyayenshi Aysha ko kuka takeyi sosai innayi Na tausarta
Gyaran murya yayi yace Ahmad alfarman da muke nema a gareka batun Aurenka da Aysha sai kuna ya sunkuyar da kanshi ganin yadda gaba dayansu jikokin nasa suka zuba mai ido
Haqiqa yusuf yasan wannan zaman kalen fitinane shiyasa ya dago kai fuska a murtuqe yace dan Allah kai mgn kana gasamin zuciya da maganganunka da suke Sa dan uwana zubda qwallah
Ayijar zuciya ya danyi
Yace Ahmad batun aurenka da Aysha babushi dan ita Aysha tana da mijin ????????????
Cikin razana da fargaba da bugawar zuciya ya katse shi da meyasa ? Waye mijin tadin ? A ina yake ? Hannunshi Na dafe da qirjinshi yake wadannan tabbayoyin a take sukar zuciyarsa ta tsananta wani nauyi ya danni maqoshinsa
Zufa ta fara ketomai tsoro mai tsanani ya rufeshi har cikin hanjinshi yake jin sanyi Na ratsashi
Itako Aysha tunda taja wani numfashi sai ta zama mutum mutumi a zaune sai barin da jikinta keyi cikin mmk abin yusuf yace ai wannan mgnar hogice wayeshi da za,a hana dan uwana farin cikinshi akan wani can banxa tun tana qarama yake wahala da ita wlh ni dinnan a matsayina Na yayanta ni zan aurar da ita ga dan uwana Adam ya dan kalli Bappa Yaya a fakaice yace cikin yanayin kaji tsohonnan da zance shirme ai wanan ba huruminka bane sai ka bari iayenmu suyi ikonsu a kanmu Allah sarki Ahmad duk sun rikice sabida bidar farin cikinsa dama Ku hausawa kunce nagari Na kowa
Su Usman ma duk sunyi zurui Abdul mai saurin kuka shikam da Sadiq kuka suke sosai Rabi,u kuma sai kada kanshi yake a hankali yace (nayeku Na ko jibare ) tsufa ko rikicewa ne
Baba bello ne ya dan rinqa musu fada cikin qarfin hali yana sabida me zaku samu a gaba kuna kuka ko ance muku mutuwa akayi da gyar dai suka dan tsaqaita sai yanxu Bappa Yaya yaci gaba yace Ahmad tabbayoyinka harsunmin yawa duk da dai zan amsa ma ka su yanxu wasu kuma sai wataran zakuji amsar sai batun aurenka da Aysha babu shi domin kuwa ita tana da miji
Amman duk da haka ba hanaka sure za,ayiba tunda an dakatar dakai kan Aysha haka nan kuma an mayarma ka da yar uwarka Maryam a madadinta
Sai yaxu Usman yace toh wai waye ne wannan da za,abashi Aysha a hana ya Ahmad ita ?
Yusuf ne shine mijinta shine Abokin rayuwarta shine tsohon alqawarin zuriyar nan ya basu amsa
daram duumm ras ras zuqatansu suka rinqa amsawa cikin firgici da razana ta dago kanta a take zufa ta keto mata bakinta har rawa yake tana waye kace?
dan uwanki yusuf nake nufi Adam ido ya zazzaro waje cikin dimuwa yace (hey ado andi ko a yeccata bo) kai Kasan abinda kace kuwa shiru yayi bai bashi amsaba
????????????
Cikin dimuwa da fargaba Ahmad ya dan ja guiwarsa ya qarisa gun Abba hannushi ya daura kan guiwowinshi ya dago kanshi ya zuba mai ido cikin wani can ji da muryarsa tasamu yace Abba gskanta min furucin mahaifinku shin zancenci gsky ne ya kuma batun haramcin auren nasu Abba ko ya mantane Aysha da yusuf uwa daya uba dayane ? Abba matuqar ka gskan tamin toh nayi alqari koda zan rasa raina nane
Da sauri yusuf ya qarisa gunda yake yasa tafin hannushi ya rufe bakinshi