Noor AlbiNOVELS

NOOR ALBI 44

Gabaki daya turaren Bois elite ne ke sanyaya palon da qamshin ga sanyin AC daya Gama Kama koina hankalinsu akwance,

 hankalinsa na Kan wayarsa yana kallon sakon LAYLAH yashigo na wasu kisses data turo Masa.

Ya Dan dauke Kai Yana Kama kansa cikin basarwa sbd Abban Laylan dasuke tare Yana zaune shima suna magana.

Dan gyara murya kadan yayi sbd neman sarkewar Dake da emojis din datake sake turowa

Yadauki wayar ya kashe gabaki daya sbd zata iya rikitasa ya Rasa meyake fada gaban Mahmoud dayake basarwa sbd karya gano waye.

Cikin nutsuwa Abba ya kalli Turakin bayan yagama kashe wayarsa ya aje gefe da sautin bayyanarda zallar gadiyarsa a natse yace”

Turaki Babu abinda Zan saka maka dashi sai godiya kawai,

Kayiwa Allah,

Kayiwa abota,

Kayiwa zumuncinka da Zainab,

Kakuma yiwa marayin Allah Dan Haka Banda bakin godiya daga Kai har Anne Ina muku fatar samun sakamakon gidan Aljanna.

Cikin basar da zancen ya Dan kalli Abban yana cewa”

Inaga ai mun rufe wannan maganar right¿

Numfashi Abban ya sauke ahankali da Jin nauyin abinda zai fada

Yadai Daure tunda ba boyo tsakaninsu da Aminin nasa ya dago ya kallesa yace”

Sai maganar Laylah…..

Sai alokacin Turakin ya dago a hankali ya kalli Abban Jin sunanta.

Gyara zama Abban yayi Yana cigaba da cewa”

Nasan Bai kamata ba nashiga zancen tunda ikonta a hannunka yake yanzu Amma tunda kamar alfarmace tun farko kayimin ka amince da Aurenta

Yanzuma Ina riqon Alfarmar karka duba tarayyata dakai idan har bakada raayin auren zaka iya sawwake Mata tadawo gida ko ahakan kayi matuqar kokari da taimakawa sosai wlh……..

Tunda yafara hada shimfida da LAYLAH Bai sake kallon cikin idon Mahmoud ba sai yanzu daya dago ya zuba Masa manyan fararen idanuwansa akansa batareda ya bude Baki yace Masa kala ba,

Abban yasan Turaki farin sani,

Babu halinsa da Bai saniba sai Wanda yaqara daga bayan Nan saidai duk da hakan idon da Turakin ya zuba Masa bazai iya cewa na menene ba

Dan Haka ya Dan muskuta Yana gyara zama jiran mgna ta fito daga bakin Turakin Dan Yama kasa qarasa sauran zancensa…

Ahankali Turakin ya dauke ido daga kan Abban Yana saukewa Kan Tv Dake aiki batareda ya iya cewa komaiba,.

Shi kansa Abban shiru yayi sbd yasan maganar na buqatan nazari Dan Haka ya kalli Turakin murya a mace yace”

Inaga gobe Zan wuce Nima A Abdoul yagama min booking ticket da komai…

Tafiyar safe zanyi saidai idan naji daga gareka.

Har lokacin Turaki Bai iya cewa komaiba sai gyada Kai da yayi Ahankali cikin nutsuwa.

A Abdoul ne yatafi maida Abbansu Laylan daga can ya wuce gida shima sbd dare yayi Daman.

Tunda Mahmoud yatafi Yana zaune inda ya barsa qafarsa daya Kan daya idanuwansa sun sauya sosai ya rufesu ahankali ya bude saiga Ms Na’ima tashigo sanyeda doguwar Riga idonta a hargitse sbd kwanakin gabaki daya Bata cikin nutsuwar zuciya.

Zama tayi gefensa cikin kokarin danne baqin cikin dake cin ranta tace”

Turaki gobe Zan wuce Lagos acan jirgin da zanbi zai tashi komawa zanyi,

Ga Laylah anbarota ba kowa nasan tana cikin kadaici….

Batareda ya waiwayo ya kalletaba Kai tsaye a karon farko tsawon shekarun aurensu dazai fara hanata tafita yace”

Ba yanzu Zaki komaba ki zauna anan tukuna.

Da mamaki ta kallesa tana juyowa gabaki daya suka fuskanci juna

Tace”

Nariga nayi komai na tafiya zakace bazanjeba?

Babu ruwanka da dukkanin tafiye tafiyena sai yanzu Kuma,

Kayi hkr sbd nariga na shirya tafiyata Banga zamanda nakeyiba anan nabaro yarinya ita kadai acan Dan Haka Ni tafiya zanyi….

Jajayen idanuwansa dasuka sauya tun kafin shigowarta ya dago ya Mata kallo daya dayasa gabanta faduwa Amma batajin zata yarda ta zauna sbd  abinda yake gabanta,

Nafada Babu inda Zaki ki

Idan Kuma Zaki tafin ki tafin Amma Kar qafarki ta Isa kofar gidana….

Miqewa yayi tareda daukan wayarsa yabar gurin.

Cikin masifaffen tashin hankali da tsoro harma da firgici Ms Na’ima tabi bayansa da kallo tana shedar da tsananin bacin Rai data hango cikin idonsa,

Karta Isa kofar gidan fa yace????

Batasan lokacinda ta miqe tana neman zunduma ihuba ta fito tana cewa”

Wlh anshiga tsananina da Turaki andau hanyar rabamu….

Ina Zinat ga bala’i Mai zaman kansa na neman sauka rayuwata

Turaki na fadar karna Isa kofar gidan.

##MAMUH#

Mamuhgee 44
Anne shiru tayi Bata sake tada maganar al’amarin takardar cikin ba sbd batasan wa zata Kama zancen dashiba,

Sa’adah dai batace komaiba sai cewa ba nata bane Haka kawai tace musu tabarsu a duhu,

Momy Bata damuba sbd tasan Babu abun daya hada sa’adahnta da wani zancen ciki Dan Haka itama tayi watsi da zancen tunda cikin Laylan Bai shafeta ba.

Abbansu ma share zancen yayi sbd Ganin Anne batace komaiba Kuma yasan tarbiyar yaransa daidai gwargwado duk da yajima baya taredasu
Amma tunda yanxu tarbiyarsu a hannun Anne take bashida ta cewa Akan maganar yabar zancen tunda yasan sunsan abinda suke.

Umma Jamila ce ta daga hankalinta Kan ayi maganar qarshe Sa’adah da kanta tace”

Ba’a son tada zancen ne sbd matar Turakin Ms Na’ima da ake gudun fitinarta.

Wata dariyar bin iska Umma Jamila tayi tana cewa”

Akwai Wanda ya Isa aji shakkarsa akan samu da qaruwa daya samemu na farin ciki,
Ita Ms Na’iman inace da Turakin take takama? To shine ake wani boye boyen karta sani.

Haj Karima dake Shan tea ahankali cikin nutsuwa da takama tace”

Sune sukasan wata Ms Na’ima
Mu abunda yake gabanmu mukeyi,
Ciki dai tunda Allah ne ya badashi ai Babu wata Na’imar dazata sakamu kame kamen rashin fadarsa.

Cikin sanyi Sa’adah Dake sin plantains ahankali tace”

Wlh tanada ban tsoro mama,
Komai zata iya,
Dan Allah abar maganar shine yafi zama alkhairi..

Tsoronta kike kenan? “” Cewar haj Karima tana kallon Sa’adahn a zube.

Ba boye boye tace”

Eh wlh Ina tsoronta mama,
Nasan komai zata iyane.

Umma Jamila ce ta kalli Momy dake saka kayanta cikin akwatinta sbd tafiyar da zasuyi Dan ansallamo Sa’adahn suna gidan Haj Karima daga Nan zasu wuce gabaki dayansu duk da sai Sa’adah Takoma gida ta dauko kayan da zatai tafiya dasu,
Cikin mamaki da takaici tacewa Momy”

Yanzu Zainab Haka Kina kallo Kika koyarda Sa’adah tsoron kishiya?

Sbd ke Taki zuciyar ta mutu gurin jinyar mijin daya zaba Taki kishiyar akanki da yarki shine Zaki kashewa yarinya zuciya da tsoron kishiya kina kallo harda bakinta take fadar tsoronta takeyi.

Rashin Jin dadin maganar da ake fadawan Momy yasa Sa’adah kallon Momy da batace komaiba ita sai shiru datai tana cigaba da shirya kayanta cikin akwati,
Ta maida kallonta Kan umma Jamila dake fada cikin takaici zatai magana Haj Karima ta katseta da cewa”

Yi mana shiru mutuniyar banza,
Shiyasa kika kasa gaba Kika kasa baya acikin gidan,
Kinkoma tamkar Yar riqo a gidan ma Matar gidan ba,
Tsabar rashin yanci a bangaren Mahaifiyarsa aka Baki Palo da daki
Bayan ita tanada makeken bangaren guda a gidan da zata aje irinki guda nawa,
Drivers ke janta da motacin Alfarma tana yawo a agarin Abuja da wajenta Amma ke kece kike tuqa kanki Dan kina ganin ansiya Miki tsadaddiyar mota bayan motocin Turakin da ake fita da ita cikinsu daya zata siya biyar din Taki harda canji Mai yawa…

Umma Jamila da Shirun Momy ke Bata ranta ko yaushe tace”

Ahaka me tasamu bare mu iyayenta muce ‘yarmu na auren Amb AB TURAKI,

Alhaji Qarami Babu shige da ficen da bayayi Dan yasamu ganin Turaki shida honourable kwangila sukeso kamar me ko manyan kudi zasu saukar musu Amma koyaushe yarinyar Nan cewa takeyi baya qasar
Ashe tsoron zuwa gurinsa take sbd kishiya,
Wlh Allah yayi wadaran naka ya lalace.

Previous page 1 2 3 4Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button