
Maryam ta kalli Rahima “Kinji ta ko? Wallahi tunda aka haifeshi take tsangwamarsa Wai Walida ta fishi kyau ko Ina kyaun da katon hanci oho._
Hajiya Suwaiba tayi dariya ” munji ba komu muma da kayan gyara, naki a sa masa ‘yankunne da janbaki mu gani.”
“Ah ah Hjy gaskiya cun fuskar tayi yawa, ki dai rike taki mu rike namu.”
A haka suka ci gaba da wasa da dariya har kusan magriba sannan suka koma dakin Maryam suka yi Sallah. Suna idarwa Hjy Suwaiba ta aiko musu da kulolin abinci wai a kawowa Rahima, da gani abincin yafi karfin ita kadai dole suka ci tare da Maryam din ita ta fasa dora tukunya. Rahima ta kalleta tace ” Don Allah da kika shiga dakinta, kikai Mata magana gashi har kinci abincinta me ya rage a jikinki? Inda za a bude Miki file dinki yau kiga dimbin ladan da kika samu da ba zaki yards ki kara yin gaba ba koda wasa.”
“Wallahi Kuma Nima sai naji wani irin dadi a Raina, duk kuncin da nike ji a zuciyata ya yaye na yarda sai kaso abu ya dameka yake damunka din.”..
Rahima tace abinda har yanzun mu mata bamu gane ba kenan, mu ke creating ma kanmu problems din da zasu dawo su dame mu, namiji ba ruwansa, sai un har kunyi dace da Mai kula ne zai fahimci halinda kuke cikin, wani ko ya gani ba abinda ya damesa tunda yawancinsu sunfi son haka, su tara Mata cikin gida ayita adawa a kansu, ya fito Yana jin dadi da hura hanci ya rinka ikrarin sabida tsananin son da kuke masa kishi ya hanaku zaman lafiya. Wani shaidanin zaman lafiyar ce bai so, yana ganin kun hada kai sai ya kasa sukuni ya shiga zargi da fargaban shifa sai yadda kuka yi dashi kenan domin da wuya daya ta yarda a ci amanar guda shi kuwa bai son hakan, yafi son ya zama bakin ganga, ya buga nan, ya Fadi gaibu can, yai munafunci a nan sai kunada kyakkyawar kula zaku gane in ba haka ba sai kuga kowacce ta fito tana kuri da fankamar ita yafi so.
Idan anyi dace da irin mazan da suka san ciwon kansu sai kiga su zaman lafiyar suke matukar bukata a gidajensu, idan Allah yasa ya dace da matan kwarai sai sai ya kula dasu matuka ya rinka kyautata musu har kiji danginsa na fadin sun mallakeshi sun gama Mana dashi alhalin jin dadin zaman lafiya da kwanciyar hankalin da yake samu dasu ya haifar da hakan. Kin ganni nan Maryam bana shakkar zama da kowacce irin mace Allsh zai hadani da ita matsayin kishiya.”
Ta gatsina baki “Karki cika baki Rahima, me kika sani game da zama da kishiya, kowacce mace fa da nata salon munafunci da kisisinar data kware, idan an debe masu shige-shigen gidan bokaye da malamai don wata ba zata zauna dake da bakin hura wuta kadai ayi kishi ba.”
Tayi murmushi “Aunty Maryam kenan ai ba wani cika baki, in har hakane Kuma Ina iya ce miki yes na cika baki ne domin nima da nawa baiwar da Allah yai min, ba wani abu bane da ya wuce kakkarfar madogora.”
Ta kada Kai “Ko Zan San wane irin madogara ne?”
Ta girgiza Kai “Nima ki bini bashi zuwa nan gaba in har Allah ya kaddareni da auren kiga matsayins zamana a gidan mijin da wajen shi kansa mijin tukunna, yanzun dai muyi sallar isha’i ki bani amsar tambayata ta tuntuni don Ina jin ga wannan karon na fada kogin nan na so da kauna sai dai ko za ku iya tsamo ni?”
05/09/2020, 22:48 – Anty saliha: ..RAHIMA..doc by jami
15
Ta koma gida cike da mamakin Hajiyar, ta zayyanewa Umma dukkan yadda suka yi, Habiba tace “To Allah ya yaji shemu alkhairi ai zaman ya isa haka, muma za muyi adduar, Baffanku ma zaiji dadin labarin nan don da yadda zaiyi da tuni ya aurad dake ga duk wanda ya dace…
Kwanaki hudu bayan maganarsu da Hjy Kaltume ta fara sakankancewa sa ikon Allah, Al-Hakeem gwanin hikima da basira. Bayan adduoin data dukufa yi haka kawai take jin wani irin dadi da nishadi a ranta, zuciyarta ta fara kamuwa da kaunar mutumin da labarinsa kawai taji, ko sunansa Bata m sani ba abinda ta manta ta tambayi Hjyr kenan. Shin wanene wannan mutumin da kaunarsa ke neman mamaye mata ilahirin zuciyarta tun kafin suyi ido biyu dashi? Shin wanene mutumin da yake da kwatankwacin halayenta? Wanene wannan mutumin da take rokon Allah dare da Rana cewan ta hadata da irinsa tun tana budurwa? Shun wane irin gwagwarmarya ratuwa ya fuskanta da yasa Hjy ke jinjinawa?
Tun kafin ta gansa tausayunsa ya cikata har taji ta matsu ta kosa ta gansa ko hankalinta ya kwanta.”
Umman tasu ta sade tsaye tana magana bata ji ba har Saida ta buga kofar dakin da karfi tayi firgigit ta dago Kai…
“Meke damunki haka na dade tsaye Ina magana baki san Ina yi ba?”..
Ta tashi zaune “Umma tunanine kawai ya isheni….
“Kiyi taka tsan-tsan da tunane-tunane nan Rahima, yaro dai ya riga ya rasu, kafin shi maza nawa suka rasu suka nar matansu, ki sahalwa kanki kici gaba da duain Allah ta tabbatar mana da wannan da Hjy tayi batun,itama fa kenan data haifesa ta dangana har itace ke kawo miki wani mijin, don me ba Zaki hakura ba, ko sai kin jawowa kanki wata cutar?”…
Ta mike tsaf tace “Umma naji na daina, bari in shirya inje gidan Maryam, idan kunji shiru can Zan kwana “..
Umma tace “Shine nazo in tambayeki zaki biya ki dauki Abdul ne ku tafi tare?”
Ta girgiza Kai ” A kyalesa can Unma, damunmu za suyi idan suka hadu da Walida..
“Kuma fa gara ya saba da zaman can din ku rinka nesa da juna Kar ayi aurenku ya ishenmu da rigima.”
Ta kalleta “Kaji Umma da wani zance, sai kace an sa ranar auren daga magana, bamu ko San juna ba fa, idan muka hadu abin bai yuwwu ba fa?”
Tace “Ai Ni Ina ji a jikina wannan auren an gama daura shi da iznin Ubangiji.”.
Haka kawai taji sanyi a ranta ko meyasa oho.. Mhmmm ta suri Jakarta ta saka after dress ta lullubeta kanta suka yi sallama ta nufi gidan ‘yaruwa…
Bata sami damar ba ‘yaruwar nata labarin labarin dake cinta ba saboda ta taras da gidan nasu a hargitse, itada Uwargidanta basa ko ga maciji, karin abin haushi harda raba Kan ‘ya’yansu kowa harkarta take da diyanta. Ran Rahima ya baci,hankalinta yai matukar tashi, bata saurari Maryam don ita ta dorawa lefin abubuwan dake faruwa.
Maryam tace “Banyi tsammanin zaki ki fahimta ta ba Rahima, ki duba irin bautar dana yiwa matar Nan da yayanta tun zuwana gidannan tun kafin in haihu na kula da yaranta, Ina bata girmanta, yanzu kuwa na gaji don shiru ba tsoro bane gudun fitina nike yi, yanzun kuwa ban damu ba aje ayi tayi idan tace kule zance cas! Ba abinda zata nuna min, idan tana takama da miji ne nima dashi nike, idan yarane nima ina dasu to sai me? Haka siddan mace ta isheni ta gallabeni tamkar ita ta aje Ni?
“Hhmmmm inji Rahima “Maryam don Allah numfasa ki saurareni da kyau, ya za ayi ki taho ki taras da mace da mijinta da yara kice zaki nuna mata iko? Mijinta fa kika aure…
“Don na auri mijinta sai me, don ita kadai aka halilto shi ne, mijin mace hudu yake, don me idan ta yayo shararta bata zubewa a kansa sai nawa? To na gaji da rainin wayo, ya isa haka.”
Rahima tace “Ban ce bata da irin nata laifin ba don bai yiwwa ace koda yaushe mutum guda ne ke da laifi da duk magana ta tashi, dole ace tanada irin nata problem, kawai so nike ki fahimci bai kamata ki biye mata duk ku haukace koma ince ku kafirce gaba daya ba, haba ‘yaruwa a matsayinki na musulma ki tsiri gaba da ‘yaruwarki musulma, makwabciyarki Kuma?”