HAUSA NOVELNOVELSSADAUKI RAZMIR Complete Hausa Novel

SADAUKI RAZMIR Complete Hausa Novel

 

 

 

 

Dodo darzaku yana zaune nehh acikin wani mugun Daji a arewa da birnin romaniya Ku sani daga nan Zuwa birnin romaniya tafiya ce ta wata biyar a doki koh rakumi sannan bayan min isa wannan birnin sai mun ratsa wadansu miyagun dazuzzuka guda uku Daji na farko wadansu manta manyan kunamu nehh masu cin naman mutum a dadin wadannan kunamu ya kai dubu daya sama da shekara biyu ba ya ba a samu wani mahaluki daya iya ratsa wannan Daji ba ya fita lpy

 

 

 

Daji na biyu wadansu manta manyan tsuntsaye nehh masu kan mutum adadinsu ya kai Dari uku da doriya sama da shekara biyu baya ba a samu wani mahaluki da ya iya zuwa wannan Daji ya wuce ba a Raye

 

 

 

Daji na uku wanda shine na karshe wani kogi nehh mai dauke da mamyan kadoji da kifaye da dodanni a tarihin wannan Kogi ba a taba samun mahalukin daya iya wucewa ta cikin sa ba

 

 

 

 

Bayan mun wuce wannan daji zamu tsinci kanmu a dajin sautil maut wanda anan nehh gidan dodo darzaku yake akan wani dogon tsauni duk shekara dodo darzaku yake hada wannan tsumi nasa yana sha

 

 

Wannan tsumi shikadai nehh maganin lalurar ka kasani cewa ba mu kadai ZAMU yi wannan tafiya ba dan muna bukatar abokan rakiya acikin wadannan abokan tafiya tamu akwai jarumi sarjun sai jaruma famila sai sadauki narkus

 

 

 

Sadauki surjan a duk wannan nahiya ba wani jarumi daya kaishi iya sarrafa takobi abinda yasa ZAMU tafi dashi kuwa ba komai bane ba illah wata masoyiyarsa da yake matukar so saidai kash sadauki surjan shikuma bayajin sha’awar mace kwata kwata ita kuma tace sai shi sabida haka nehh suka zo gurina da batun su na fada musu tsumin dodo darzaku nehh kawai maganin wannan cuta tasa ya bari akwai lokacin da za aje a debo wannan tsumi idan lokaci yayi zan masa mgn wannan shine lokacin sabida haka kawai biyawa zamuyi mu dauke shi

 

 

Sai jaruma famila wadda masani suka tabbatar kaf nahiyar nan ba wata jarumar data kaita zafin nama a fagen yaki ita kuma batada matsalar komai a rayuwata amma ZAMU je mata da batun aure a rayuwar jaruma famila ba abinda takeso kamar gahurtaccen basarake sabida haka idan ka nuna mata zaka aureta tsaf zata amince da batun ka

 

 

 

Sai jarumi na uku wato sadauki narkus shikuma masani masu bincike sun tabbatar da akaf wannan nahiyar ba wani jarumi da ya kaishi karfin dantse da tsagwaron iya yaki sai sarki Darraju da yarima mangul kai kuwa yarima mangul yanxu ka zama babu dan haka shima zai taimaka mana acikin wannan tafiya

 

 

 

Kasani a rayuwar sadauki narkus ba abinda yakeso kamar kudi da daukaka idan kayi masa alkawarin duniya mai farin yawa da matsayi mai girma zai yarda ya bimu wannan tafiya amma fahh kasani baxamu taba tafiya da sarki Darraju ba sabida abokan gabar dake kusan toshi

 

 

 

Ya kai sarkin sarakuna ka sani cewa dan sarki hawwasha da kayiwa juyin mulki ya girma a yanxun ya zama gawurtaccen jarumi mai dakawa maza gunba a hannu kuma a yanxu duk duniya ba mutum da ya kaishi karfin gudu a kafa sai kai maganar da nake maka a yanxu haka ya yayi tafiya mai dogon zango dan ya dawo ya fuskanceka ya karbi karagar mahaifin sa dan haka kenan da kai da yarima duk kuna cikin tsaka mai wuya kenan dan haka sai kuyi tunanin mafita ni dai a shirye nake yarima mangul idan ka shirya hadimina najiram mu a waje dan mu fuskanci wannan tafiya dake gaban mu koh da boka barnuhul masul yaxo nan a zancen sa sai yayi shuru yana Mao sauraren da da mahaifinsa,,,,,,,,,,

 

 

 

 

 

 

WANNAN KENAN

 

 

Al’amarin su sadauki Razmir da gimbiya Numaira kuwa lokacin da aljani shabrul ya daukesu suka fara tafiya saida sukayi tafiya sa’a daya da rabi sannan suka shiga yankin birnin sin

 

 

 

Haka suka ci gaba da tafiya ba tare da tsoron komai ba bayan wadansu dakiku nehh gimbiya Numaira tayi gyaran muryanta Alamar tanada bukata nan take aljani shabrul y sauko kasa luuuuu bai dira ako ina ba sai acikin wani daji mai matukar muni da ban tsoro suna sauka acikin.dajin sadauki Razmir yasha jinin jikinsa kawai sai ya fara kallon yanayin dajin yana nazarin ko ina

 

 

 

Dajin ya kasance yana da manyan bishiyoyi dogaye wadanda ba a iya hango karshen su sannan dajin yana da matukar duhu tamkar dare nehh lokacin

 

 

 

Ba tare da bata wani lokaci da gimbiya Numaira ta zagaya bayan wata bishiya dan kawarta da bukatar ta

 

 

 

 

Bayan wadansu dakiku nehh sadauki Razmir ya jiyo ihun gimbiya Namaira cikin bakin zafin nama ya tare takobin sa da gudu yayi bayan bashiyar yana isa yaga wani Abu ya sumgumi gimbiya Numaira ya zubata da mugun gudu cikin bakin zafinnama sadaiji Razmir ya rufah masa baya suka kasa tsere nan take ya kama shi ba komai bane ba sai wani gwagwgwan biri nan dai suka ci gaba da gudu shi birin bai tsaya ba shikuma sadauki Razmir ya kasa kamoshi saida suka shafe sa’a daya da rabi suna wannan gudu a sannan nehh suka iso wani fili fetal filin ya kasance makeke birin yana zuwa gurin nan ya tsaya yana mai fuskantar sadauki Razmir wata kururuwa yayi kawai saiga birirrika suna fitowa daga ramuka wasu daga cikin daji kan kace wani Abu sun yi wa sadauki Razmir kawanya tako ina

 

 

 

 

Shiko sai ya gyara tsayuwarsa yana mai fuskantar birirrikan ana kallon kallo………………

 

 

 

 

 

KAKA KARA KAKA YANXUN FAHH AKA FARA LBRN MUJE ZUWA COMMENTS DINKU KAWAI NAKE BUKATA

 

 

 

vote
Comments and shared

 

 

WhatsApp number 08143314152

 

 

 

By fast class
????????????????????
SADAUKI RAZMIR
(Adventure story)
????????????????????

Writing by

ALIYU H ISHAQ
(fast class)

________________________________

*AREWA WRITER’S ASSOCIATION*
_________________________________
*????{Arewa ginshiƙin al’ummah}????*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com

DAGA MARUBUCIN

UMAR FAROUQ
KAUNAR UWA
TARTSATSIN WUTA
(Adventure story)
SANDAR GIRMA
(Adventure story)
HAEEDARR
And now

SADAUKI RAZMIR
(Adventure story)

 

IG, haidar_Ishaq_576

Email,  haidarishaq@gmail.com

WATTPAD, @FASTCLASS

Facebook, haidar ishaq

 

…………Lokacin da sadauki Razmir suka fafata kazamin yaki da shugaban wannan biririkan har ya bamu nasarar kashe shi nan fahh labari ya sauya ga dai na Razmir a tsaye cikin mawuyacin hali amma acikin wadannan birirrikan an rasa wanda zai yi ta maza ya kawo masa wani farmaki

 

 

 

Koda sadauki Razmir yaga haka sai ya takarkare ya kwarara uban ihu yana mai daga takobin sa sama nan take wadannan birirrikan suka ce kafa mai naci ban baki ba kan kace wani Abu sun gudu ba koh daya a gurin sai gimbiya Numaira dake gefe daya tana maida numfashi

 

 

 

Da rarrafe ta taho inda sadauki Razmir yake a tsugune tana mai dafa kafadar sa suna hada idanu ta sakar masa wani tattausan murmushi kana ta bude baki tace”ngd da ceton rayuwata da kayi

 

 

 

Shima murmushi yayi mata amma baice kala ba ya mike y zaro battar ruwansa ya kafa baki ya kama sha bayan ya sha ya isheshi nehh suka tashi suka koma inda sukabar aljani shabrul

 

 

 

Ba tare da bata wani lokaci ba suka ci gaba da tafiyar su inda suka durfafi birnin sin kai tsaye ba tare da shakkar komai ba

 

 

 

A cikin Rabin sa’a suka iso birnin sin basu sha wahala ba gurin Neman gidan boka mutsulul gayush dan ya shahara a birnin

 

 

Da Isar sadauki Razmir fadar boka mutsulul gayush nehh yaji an fara tafa masa ana mai yi masa kirari gaba daya bangon fadar ya dauka ko ina amma baiga Wanda yake masa wannan tafin ba

Previous page 1 2 3 4 5 6 7Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button