SHU’UMIN NAMIJI COMPLETE HAUSA NOVEL

Da sauri taje ta faɗa jikinsa, kuka take sosai, durƙusawa tayi haɗe da zube guiwowinta a ƙasa, kana ta riƙe rigarsa, kanta tashiga girgizawa, tana kuka tace. “A da na sosa fiye da yanda naso kaina, amma ayanzu baya acikin zuciyata kamar yanda kake tunani, Inasonka da duka zuciyata, bana fatan wata ƙaddara tazo wacce zata rabani dakai, kabani farinciki, kajiyar dani daɗi, kashayar dani zuman soyayyarka, bazan iya watsa maka ƙasa idanunka ba, kai mijinane wanda bayan kai bani da wani tamkarka, nasan kai ɗin me sonane, amma meyasa kayi haka? mai yasa kai da kanka, zaka amince da na karɓi kyautar wanda yazama silar rugujewar rayuwata?”
Durƙusawa yayi agabanta, haɗe da sanya hanunsa ya share mata hawayen dake gudu akan fuskarta, cike da kulawa yace. “Banason kukanki Zahrah, keɗin wata babban jigo kuma mahaɗi ne acikin rayuwata, nasan Zaid ya cutar da rayuwarki, amma kuma hakan bazai hana ki amshi kyautarsa ba, ayanzu kowa yasan cewa ke matatace, saboda haka Zaid bazaiyi miki kyauta da wata manufa ba, kuma kafun ya miki kyautar saida ya tambayi amincewata tukunna, nakuma amince masa, nayarda da Zaid Zahrah, nasan idan duka mutanen duniya zasu taru su cutar dake, to Zaid bazaiyi hakan ba, haka kuma idan ni zan iya cutar dake, to ina tabbatar miki idan Zaid yasan da hakan, to bazai bari na cutar dake ba, Zaid ɗin da kikasani ada bashine wanda yake a yanzu ba, kada kiyi tunanin wai ko zanji haushi akan kyautar da Zaid yayi miki, niba jahili bane Zahrah, haka kuma halina ya banbanta da na wasu mazan, ni mutum ne me saurin fahimta, sannan kuma abune mawuyaci nayiwa wani na mummunan zato, agurin wasu mazan, hakan zai iya zama matsala, amma a wajena hakan ba komai bane, tunda nasan cewa keɗin tawace ni kaɗai, bakuma wai don bana kishinki bane yasa hakan tafaru ba a’a, ni kalan nawa kishin ba irin na wasu bane, inakishinki sosai, sai dai kuma kome acikin nutsuwa nakeyinsa, ke kinsan inasonki ina kuma kishinki ” yaƙare maganar yana me lakace mata dogon hancinta.
Kukane yakuma ƙwace mata sai kawai tafaɗa jikinsa, ta rungumesa ƙam, shima rungumeta yayi yana shafa bayanta ahankali, haɗe da hura mata iskan bakinsa, acikin kunnenta.
Saida tayi kukanta sosai, kafun ta soma sauƙe ajiyar zuciya, cikin murya me sanyi tace.
“Kai na da banne Mijina, irinka basu da yawa acikin duniya, haƙiƙa nafi kowacce mace sa’a dana sameka, dakai kaɗai zan rayu har izuwa mutuwa ta, kaima ka rayu dani ni kaɗai kaji, bazan iya jure ganinka da wata mace ba bayanni, Ina maka son da bansan iyakarsa ba!”
Murmushinsa dake ƙara masa kyau yayi, haɗe da sanya iskan bakinsa ya hura mata fuska.
“Dake kaɗai Zan rayu Zahrah na, ni nakine ke kaɗai, amma idan kina kukan nan fa, dole zan ɗan yi ƙasa da idanuna, na hango wata, saina kawota ko wanke wanke ne tanayi mana ko, idan dare yayi kuma sai ina raba muku kwana ko…”
Bata bari yakai ƙarshen zancen nasa ba, ta muntsine sa aciki, saida yasaki wata ƴar ƙaramar ƙara, cike da shagwaɓa tace “Wallahi nidai babu ruwana dakai, idan dai har kace zakamin kishiya!”
Dariya yayi sosai haɗe da cusa kansa acikin ƙirjinta. “Ni na isa ma nayiwa ƴar sakalalliyar matata kishiya, amma bandai saniba wataƙila idan naga kin tsofe na miki!” yanzuma cikin zolaya yayi maganar.
Hannayenta tasanya acikin gashin kansa, tashiga ya mutsawa, hadda kai masa cizo a wuyansa. Sai da tayi masa buji buji da kayan jikinsa kafun ta ƙyalesa, gashin kansa ma gaba ɗaya ta hargitsa masa shi. Koda ta kawo masa abinci tare sukaci, yana kwance ajikinta itakuma tana bashi abincin abaki, ahaka har ya ƙoshi.
Kallonta yayi da idanunsa, dake tsumata kana yace “Namatsu abani ke Baby na, wallahi ina kewar ɗumin ki sosai, amma Hajiya gaba ɗaya ta kanenaye min ke, waidole saikinyi arba’in, Babyna kice tabarmu mu koma gidanmu kinji!” cikin yanayi na shagawaɓa ya faɗi haka.
Murmushi Zahrah tayi, haɗe da sanya hanu ta shafi kumatun sa, cike da ƙaunarsa tace “Kayi haƙuri Hubby, nima ina kewar sucking ɗinka, kuma ai bawai bazan dawo bane zan dawo fa” tafaɗi hakane don kawai ta kwantar masa da hankali.
Ya buɗe baki zaiyi magana kenan muryar Hajiya ta karaɗe kunnuwansu, inda take cewa.
“To iyayen rashin kunya, saika tashi katafi dare na ƙarayi, ke kuma miji daɗi, ga yaronki nan, abincinsa yakeso ki basa.” kunyar Hajiya ne yakama Zahrah, haka ta amshi yaron kanta a ƙasa.
Doctor kuwa turawa Hajiya baki yayi, haɗe da cewa “Hajiya zantafi, amma kiɗanyi haƙuri ba yanzu ba mana”
Baki Hajiya ta sake tana kallonsa. “Sannu marar ta ido, wallahi saika tafi yanzu kuwa” Hajiya tafaɗi haka tana me kama hanunsa, haka yanaji yana gani ta fitar dashi daga ɗakin, Zahrah kam dariya taketa yi masa. Bayan ta shayar da yaron natane, tashiga toilet tayi wanka, doguwar rigan bacci tasanya, kana ta ɗauko diary’nta, rubutu tayi aciki, ta mayar dashi ma’ajinsa. Kwanciya tayi luf akan gado, cike da tunani kala kala bacci ya ɗauketa….
Yau kwanansu 50 cif cif agidan Hajiya, sunƙara kwanaki 10 akan kwanakin gama wankansu, idan kaga Zahrah bazakace ita bace, sosai taƙara cika da kyau, fatarta ta ƙara haske, komai nata yasake cika, gwanin sha’awa, yau ne zata koma gidanta, tuni Dr.Sadeeq ya sanja mata kayan furnitures ɗinta, komai yasanya mata sabo, Hajiya kuwa tun tuni taketa ɗirka mata magunguna, haka Aunty Raliya ma ta dage sai bata wasu magunguna masu ƙarfi take, ita kuwa sha take abunta, wanda taji yanada bauri ne kawai take ajiyewa bata sha.
Wanka ta tsantsara cikin wata jar atamfa Super Exclusive, wacce taji ɗinkin riga da sket, sosai kayan ya amshi jikinta, zama tayi da kanta, ta tsantsarawa fuskarta kwalliya, sai gashi kuwa kyawunta ya ƙara bayyana, dogon gashinta dayasha gyara ta tubke da ribbon haɗe da kafa ɗaurin ɗan kwalinta me kyau, wani red ɗin takalmi tasanya aƙafanta me tsinin gaske, ɗan ƙaramin mayafi ja ta ɗauka ta rufe jikinta dashi, babu abun dake fita ajikinta, sai daddaɗan ƙamshi.
Yana tsaye ajikin motarsa dake fake a compound ɗin gidan, yaga fitowarta, kusan suman tsaye yayi. “Tabbas Zahrah me kyauce, tahaɗu tako ina, kullum ƙara kyau da cika take, lallai kuwa da yayi saken barin Zahrah, tabbas da yazama soko, marar rabo, samun mace kamar Zahrah, babban sa’ane daya samu a rayuwarsa” yafaɗi haka acikin zuciyarsa, yana hangame da baki wajen kallonta, baisan ma taƙaraso garesa ba, saida yaji ni’imtaccen ƙamshinta na ratsa cikin hancinsa.
Murmushinta me kyau tayi masa haɗe da kashe masa idanunta ɗaya. “Ya dai kwalliyar tayi maka ne” tafaɗi haka tana me juya masa bayanta. Alaman yaganta da kyau.
Yawu ya haɗiye, alokacin da idanunsa suka sauƙa akan hips ɗinta, baigama dawowa hayyacinsa ba, yakuma jefa idanunsa akan ƙirjinta, jikinsa na rawa ya jawota ya rungumeta.
Wani irin ajiyar zuciya suka sauƙe atare.
“I really Miss you Babyy!!” yafaɗi haka akasalance.
“Miss you too dear!” itama ta mayar masa da amsa cikin muryar raɗa.